• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Kyakkyawa Za Ta Kara Samar Da Gudummawarta Ga Duniya

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasar Sin Kyakkyawa Za Ta Kara Samar Da Gudummawarta Ga Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Karancin makamashi matsala ce da galibin kasashen Afirka ke fuskanta, a yayin da kuma nahiyar Afirka ta kasance daya daga cikin sassan duniya da suke karancin karfin tinkarar sauyin yanayi, don haka, ya zama dole kasashen Afirka su bunkasa makamashi mai tsabta a wani kokari na tabbatar da dauwamammen ci gabansu.

A watan Afrilun bana, rukunin na’urori na farko ya fara samar da wutar lantarki a madatsar ruwa ta Zungeru da ke kogin Kaduna na jihar Niger ta kasar Nijeriya, tasha ce da kamfanin kasar Sin ya gina, wadda ake sa ran zata iya samar da wutar lantarki da zai biya bukatun birane biyu da girmansu ya kai kamar na babban birnin Abuja, wadda kuma za ta taimaka ga kyautata matsalar karancin wuta da ake fuskanta a kasar, da ma tabbatar da dauwamammen ci gaban kasar.
A hakika, tuni kasar Sin ta aiwatar da shirye-shirye sama da 100 a fannin samar da makamashi mai tsabta da kiyaye muhalli a kasashen Afirka. Misali a kasar Habasha, tashar Adama da ta Aysha da kamfanonin kasar Sin suka gina, wadanda ke samar da wuta ta amfani da makamashin iska, sun bunkasa makamashi mai tsabta, wadanda suka samar da tabbaci ga bunkasuwar masana’antu da ma rayuwar al’umma a kasar.

  • Shugabar Tanzania Za Ta Zama Shugabar Afirka Ta Farko Da Za Ta Ziyarci Sin Bayan Babban Taron Wakilan JKS Karo Na 20

A kenya, tashar samar da wuta ta amfani da makamashin rana ta Garissa da kamfanin kasar Sin ya gina, ta kasance irinta mafi girma a gabashin Afirka, wadda tsohon shugaban kasar Kenya Uhuru Kenyyata ya taba bayyana ta a matsayin wadda ta taimaka wa Kenya wajen dogara da kanta wurin samar da makamashi mai tsabta.
A cikin shekaru 10 da suka gabata, ra’ayin muhimmancin kare muhalli ya yi ta kara zame wa al’ummar Sinawa jini da tsoka.

A yayin da ake kiyaye saurin bunkasuwar tattalin arziki a kasar, yawan iskar Carbon da aka fitar a kasar ma ya ragu ainun, baya ga muhallin halittu da yake dada kyautata, kasar Sin ta samu gaggarumin ci gaba ta fannin kare muhalli.

A sa’i daya kuma, kasar Sin ta yi kokarin rungumar makomar dan Adam ta bai daya, inda ta yi iyakacin kokarinta wajen samar da fasahohinta ga kasashe masu tasowa ta fuskar kiyaye muhalli. Kawo yanzu dai, kasar Sin ta samar da kudi yuan biliyan 1.2 kwatankwacin dala miliyan 165 wajen aiwatar da hadin gwiwa da kasashe masu tasowa don tinkarar matsalar sauyin yanayi, baya ga kuma daddale yarjejeniyoyin hadin gwiwa 43 tare da kasashe masu tasowa 38, tare da horar da ma’aikatan kula da sauyin yanayi kimanin 2000 daga kasashe masu tasowa sama da 120.

Labarai Masu Nasaba

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Jam’iyyar kwaminis mai mulki a kasar Sin a babban taron wakilanta na 20 da aka kammala kwanan nan ba da jimawa ba, ta tsara taswirar gina kasa mai tsarin gurguzu ta zamani, inda kuma ta jaddada cewa, “ya kamata kasar Sin ta zamani ta kasance yadda dan Adam ke zaman jituwa da muhalli”, tare da tsara ayyukan da za a sanya gaba a wannan fanni.

Ban da wannan, ta kuma yi nuni da cewa, ya kamata a rungumi makomar dan Adam ta bai daya, “a tsaya ga kiyaye muhalli, tare da sa kaimin gina kyakkyawar duniyar dan Adam mai tsabta.” Ta hakan muke iya hasashen cewa, nan da ba da jimawa ba, kasar Sin ba kawai za ta kasance mai karfi ta fannin tattalin arziki da al’adu ba, tabbas kuma za ta kasance mai kyakkyawan muhalli.

Tabbas kuma kasar za ta kara samar da gudummawarta wajen tabbatar da kyakkawar duniyar dan Adam da ma dauwamammen ci gabansu.(Mai zane:Mustapha Bulama)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Illar Amfani Da Manhajar VPN Ta Kyauta

Next Post

Hana ‘Yan Nijeriya Bizar Dubai Manakisa Ce, In Ji Gamayyar Matasa

Related

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
Daga Birnin Sin

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

16 hours ago
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani
Daga Birnin Sin

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

17 hours ago
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

18 hours ago
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari
Daga Birnin Sin

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

19 hours ago
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi
Daga Birnin Sin

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

20 hours ago
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

21 hours ago
Next Post
Hana ‘Yan Nijeriya Bizar Dubai Manakisa Ce, In Ji Gamayyar Matasa

Hana ‘Yan Nijeriya Bizar Dubai Manakisa Ce, In Ji Gamayyar Matasa

LABARAI MASU NASABA

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

September 17, 2025
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

September 17, 2025
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

September 17, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja

September 17, 2025
Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

September 17, 2025
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

September 17, 2025
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.