• English
  • Business News
Wednesday, July 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Kyakkyawa Za Ta Kara Samar Da Gudummawarta Ga Duniya

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasar Sin Kyakkyawa Za Ta Kara Samar Da Gudummawarta Ga Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Karancin makamashi matsala ce da galibin kasashen Afirka ke fuskanta, a yayin da kuma nahiyar Afirka ta kasance daya daga cikin sassan duniya da suke karancin karfin tinkarar sauyin yanayi, don haka, ya zama dole kasashen Afirka su bunkasa makamashi mai tsabta a wani kokari na tabbatar da dauwamammen ci gabansu.

A watan Afrilun bana, rukunin na’urori na farko ya fara samar da wutar lantarki a madatsar ruwa ta Zungeru da ke kogin Kaduna na jihar Niger ta kasar Nijeriya, tasha ce da kamfanin kasar Sin ya gina, wadda ake sa ran zata iya samar da wutar lantarki da zai biya bukatun birane biyu da girmansu ya kai kamar na babban birnin Abuja, wadda kuma za ta taimaka ga kyautata matsalar karancin wuta da ake fuskanta a kasar, da ma tabbatar da dauwamammen ci gaban kasar.
A hakika, tuni kasar Sin ta aiwatar da shirye-shirye sama da 100 a fannin samar da makamashi mai tsabta da kiyaye muhalli a kasashen Afirka. Misali a kasar Habasha, tashar Adama da ta Aysha da kamfanonin kasar Sin suka gina, wadanda ke samar da wuta ta amfani da makamashin iska, sun bunkasa makamashi mai tsabta, wadanda suka samar da tabbaci ga bunkasuwar masana’antu da ma rayuwar al’umma a kasar.

  • Shugabar Tanzania Za Ta Zama Shugabar Afirka Ta Farko Da Za Ta Ziyarci Sin Bayan Babban Taron Wakilan JKS Karo Na 20

A kenya, tashar samar da wuta ta amfani da makamashin rana ta Garissa da kamfanin kasar Sin ya gina, ta kasance irinta mafi girma a gabashin Afirka, wadda tsohon shugaban kasar Kenya Uhuru Kenyyata ya taba bayyana ta a matsayin wadda ta taimaka wa Kenya wajen dogara da kanta wurin samar da makamashi mai tsabta.
A cikin shekaru 10 da suka gabata, ra’ayin muhimmancin kare muhalli ya yi ta kara zame wa al’ummar Sinawa jini da tsoka.

A yayin da ake kiyaye saurin bunkasuwar tattalin arziki a kasar, yawan iskar Carbon da aka fitar a kasar ma ya ragu ainun, baya ga muhallin halittu da yake dada kyautata, kasar Sin ta samu gaggarumin ci gaba ta fannin kare muhalli.

A sa’i daya kuma, kasar Sin ta yi kokarin rungumar makomar dan Adam ta bai daya, inda ta yi iyakacin kokarinta wajen samar da fasahohinta ga kasashe masu tasowa ta fuskar kiyaye muhalli. Kawo yanzu dai, kasar Sin ta samar da kudi yuan biliyan 1.2 kwatankwacin dala miliyan 165 wajen aiwatar da hadin gwiwa da kasashe masu tasowa don tinkarar matsalar sauyin yanayi, baya ga kuma daddale yarjejeniyoyin hadin gwiwa 43 tare da kasashe masu tasowa 38, tare da horar da ma’aikatan kula da sauyin yanayi kimanin 2000 daga kasashe masu tasowa sama da 120.

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Na Inganta Samun Nasara Ga Kowane Bangare A Fannin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki A Duniya

Xi Jinping Ya Mika Sakon Ta’aziyya Zuwa Ga Takwaransa Na Najeriya Bisa Rasuwar Muhammadu Buhari

Jam’iyyar kwaminis mai mulki a kasar Sin a babban taron wakilanta na 20 da aka kammala kwanan nan ba da jimawa ba, ta tsara taswirar gina kasa mai tsarin gurguzu ta zamani, inda kuma ta jaddada cewa, “ya kamata kasar Sin ta zamani ta kasance yadda dan Adam ke zaman jituwa da muhalli”, tare da tsara ayyukan da za a sanya gaba a wannan fanni.

Ban da wannan, ta kuma yi nuni da cewa, ya kamata a rungumi makomar dan Adam ta bai daya, “a tsaya ga kiyaye muhalli, tare da sa kaimin gina kyakkyawar duniyar dan Adam mai tsabta.” Ta hakan muke iya hasashen cewa, nan da ba da jimawa ba, kasar Sin ba kawai za ta kasance mai karfi ta fannin tattalin arziki da al’adu ba, tabbas kuma za ta kasance mai kyakkyawan muhalli.

Tabbas kuma kasar za ta kara samar da gudummawarta wajen tabbatar da kyakkawar duniyar dan Adam da ma dauwamammen ci gabansu.(Mai zane:Mustapha Bulama)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Illar Amfani Da Manhajar VPN Ta Kyauta

Next Post

Hana ‘Yan Nijeriya Bizar Dubai Manakisa Ce, In Ji Gamayyar Matasa

Related

Kasar Sin Na Inganta Samun Nasara Ga Kowane Bangare A Fannin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki A Duniya
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Inganta Samun Nasara Ga Kowane Bangare A Fannin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki A Duniya

41 minutes ago
Xi Jinping Ya Mika Sakon Ta’aziyya Zuwa Ga Takwaransa Na Najeriya Bisa Rasuwar Muhammadu Buhari
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Ta’aziyya Zuwa Ga Takwaransa Na Najeriya Bisa Rasuwar Muhammadu Buhari

2 hours ago
Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9

21 hours ago
Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO
Daga Birnin Sin

Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

23 hours ago
An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

23 hours ago
Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%
Daga Birnin Sin

Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

24 hours ago
Next Post
Hana ‘Yan Nijeriya Bizar Dubai Manakisa Ce, In Ji Gamayyar Matasa

Hana ‘Yan Nijeriya Bizar Dubai Manakisa Ce, In Ji Gamayyar Matasa

LABARAI MASU NASABA

Farashin Kayayyaki Sun Sauka A Watan Yuni 2025

Farashin Kayayyaki Sun Sauka A Watan Yuni 2025

July 16, 2025
Kasar Sin Na Inganta Samun Nasara Ga Kowane Bangare A Fannin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki A Duniya

Kasar Sin Na Inganta Samun Nasara Ga Kowane Bangare A Fannin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki A Duniya

July 16, 2025
Afrika Ta Zama Kasuwar Sayar Da Man Fetur Mara Inganci – Dangote

Afrika Ta Zama Kasuwar Sayar Da Man Fetur Mara Inganci – Dangote

July 16, 2025
Xi Jinping Ya Mika Sakon Ta’aziyya Zuwa Ga Takwaransa Na Najeriya Bisa Rasuwar Muhammadu Buhari

Xi Jinping Ya Mika Sakon Ta’aziyya Zuwa Ga Takwaransa Na Najeriya Bisa Rasuwar Muhammadu Buhari

July 16, 2025
An Fara Binciken Mutuwar Wasu Ɗalibai 2 A Makarantar Kwana A Kano

An Fara Binciken Mutuwar Wasu Ɗalibai 2 A Makarantar Kwana A Kano

July 16, 2025
Atiku Abubakar Ya Fice Daga PDP, Duba Dalili

Atiku Abubakar Ya Fice Daga PDP, Duba Dalili

July 16, 2025
Peter Obi Ya Kai Wa Iyalan Buhari Ziyarar Ta’aziyya

Peter Obi Ya Kai Wa Iyalan Buhari Ziyarar Ta’aziyya

July 16, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

Omokri Da Sarki Sun Soki Obi Saboda Rashin Halartar Jana’izar Buhari

July 16, 2025
Kotu Ta Wanke Fayose Daga Zargin Zambar Naira Biliyan 3.3

Kotu Ta Wanke Fayose Daga Zargin Zambar Naira Biliyan 3.3

July 16, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

July 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.