• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin, Kyakkyawar Fata Ga Makomar Kasashe Masu Tasowa

by CMG Hausa
2 years ago
Kasar Sin

Kasar Sin za ta jagoranci taro kai tsaye na farko cikin shekaru 31 tsakaninta da kasashen yankin tsakiyar Asiya da suka hada da Kazakhstan da Kyrgystan da Tajikistan da Turkmenistan da Uzbekistan, a ranakun 18 da 19 ga wata, wanda ke zaman muhimmin taro tsakanin bangarorin.

A ganina, wannan taro zai kara tabbatar da karfin kasar Sin na jagorantar kasashe masu tasowa wajen samun ci gaban da suke muradi da kuma ba su damar shiga ana damawa da su cikin harkokin kasa da kasa.

  • Karuwar Cinikin Wajen Sin A Watanni 4 Na Farkon Bana Ta Kai Kaso 5.8 Bisa Dari Kan Na Makamancin Lokaci Na Bara

Hakika ba al’ummar kasar Sin ne kadai ke amfana da ci gaban da kasar ta samu ba, har ma da kasashe masu tasowa, inda take fito da su tare da kara sanyawa ana jin amonsu, domin in ban da kasar Sin, babu wata babbar kasa dake kokarin jan kasashe masu tasowa a jiki da zuciya daya.

Tarihi ya nuna cewa, kasar Sin na daya daga cikin kasashen da suka fara kulla huldar diflomasiyya da wadannan kasashe tun bayan samun ’yancin kansu, kuma tun daga lokacin ake samun kyautatuwar alaka a tsakaninsu.

Hakika hulda da kasar Sin babban tagomashi ne ga kowace kasa domin ta kasance mai tabbatar da adalci da aiwatar da dangantaka bisa girmama juna da moriyar juna, da kuma kaunar ganin an gudu tare an tsira tare. Burin kasar Sin a kullum shi ne ganin ci gaban kasashe masu tasowa, da burin ganin sun tsaya da kafarsu sun kuma nemi ci gaba ta hanyar da ta dace da su. Irin wannan ra’ayi shi ne ya dace da kyautata zaman lafiya da ci gaban duniya da ma kyautata zamantakewar al’umma.

LABARAI MASU NASABA

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

Yayin da wasu kasashe suka dukufa wajen yin babakere da tsoma baki da neman ci da gumin kasashe masu tasowa, kasar Sin ta kasance wata sabuwa kuma kyakkayawar fata ga makomar kasashe masu tasowa.

Bugu da kari, dangantakar wadannan kasashe za ta taimaka wajen kyautata zaman lafiyar yankin Asiya. Dangantakar dake tsakanin Sin da kasashen tsakiyar Asiya, dangantaka ce ta moriyar juna bisa la’akari da hadin gwiwarsu a bangarori kamar na makamashi da fasaha da hakar ma’adinai da amfanin gona, inda kayayyakin wadannan bangarori da Sin ta shigo da su daga wadannan kasashe a bara, suka kasance mafi yawa, haka kuma su ne suka fi sayen kayayyakin laturoni da injuna daga kasar Sin.

Lamarin da ke nuna cewa, taron dake karatowa, zai kara bunkasa kyakkyawar dangantakar dake akwai tsakaninsu, tare da samar da karin sabbin damarmaki da ci gaban tattalin arziki. (Fa’iza Mustapha)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an
Daga Birnin Sin

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

November 6, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST
Daga Birnin Sin

CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

November 6, 2025
Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya
Daga Birnin Sin

Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

November 6, 2025
Next Post
Mutum 15 Sun Mutu A Hatsarin Jirgin Ruwa A Sakkwato

Mutum 15 Sun Mutu A Hatsarin Jirgin Ruwa A Sakkwato

LABARAI MASU NASABA

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

November 6, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

November 6, 2025
Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

November 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

November 6, 2025
Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.