• English
  • Business News
Tuesday, July 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin, Kyakkyawar Fata Ga Makomar Kasashe Masu Tasowa

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasar Sin, Kyakkyawar Fata Ga Makomar Kasashe Masu Tasowa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kasar Sin za ta jagoranci taro kai tsaye na farko cikin shekaru 31 tsakaninta da kasashen yankin tsakiyar Asiya da suka hada da Kazakhstan da Kyrgystan da Tajikistan da Turkmenistan da Uzbekistan, a ranakun 18 da 19 ga wata, wanda ke zaman muhimmin taro tsakanin bangarorin.

A ganina, wannan taro zai kara tabbatar da karfin kasar Sin na jagorantar kasashe masu tasowa wajen samun ci gaban da suke muradi da kuma ba su damar shiga ana damawa da su cikin harkokin kasa da kasa.

  • Karuwar Cinikin Wajen Sin A Watanni 4 Na Farkon Bana Ta Kai Kaso 5.8 Bisa Dari Kan Na Makamancin Lokaci Na Bara

Hakika ba al’ummar kasar Sin ne kadai ke amfana da ci gaban da kasar ta samu ba, har ma da kasashe masu tasowa, inda take fito da su tare da kara sanyawa ana jin amonsu, domin in ban da kasar Sin, babu wata babbar kasa dake kokarin jan kasashe masu tasowa a jiki da zuciya daya.

Tarihi ya nuna cewa, kasar Sin na daya daga cikin kasashen da suka fara kulla huldar diflomasiyya da wadannan kasashe tun bayan samun ’yancin kansu, kuma tun daga lokacin ake samun kyautatuwar alaka a tsakaninsu.

Hakika hulda da kasar Sin babban tagomashi ne ga kowace kasa domin ta kasance mai tabbatar da adalci da aiwatar da dangantaka bisa girmama juna da moriyar juna, da kuma kaunar ganin an gudu tare an tsira tare. Burin kasar Sin a kullum shi ne ganin ci gaban kasashe masu tasowa, da burin ganin sun tsaya da kafarsu sun kuma nemi ci gaba ta hanyar da ta dace da su. Irin wannan ra’ayi shi ne ya dace da kyautata zaman lafiya da ci gaban duniya da ma kyautata zamantakewar al’umma.

Labarai Masu Nasaba

Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa

Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

Yayin da wasu kasashe suka dukufa wajen yin babakere da tsoma baki da neman ci da gumin kasashe masu tasowa, kasar Sin ta kasance wata sabuwa kuma kyakkayawar fata ga makomar kasashe masu tasowa.

Bugu da kari, dangantakar wadannan kasashe za ta taimaka wajen kyautata zaman lafiyar yankin Asiya. Dangantakar dake tsakanin Sin da kasashen tsakiyar Asiya, dangantaka ce ta moriyar juna bisa la’akari da hadin gwiwarsu a bangarori kamar na makamashi da fasaha da hakar ma’adinai da amfanin gona, inda kayayyakin wadannan bangarori da Sin ta shigo da su daga wadannan kasashe a bara, suka kasance mafi yawa, haka kuma su ne suka fi sayen kayayyakin laturoni da injuna daga kasar Sin.

Lamarin da ke nuna cewa, taron dake karatowa, zai kara bunkasa kyakkyawar dangantakar dake akwai tsakaninsu, tare da samar da karin sabbin damarmaki da ci gaban tattalin arziki. (Fa’iza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Bukaci Jami’ar Ofishin Jakadancin Canada A Shanghai Da Ta Bar Kasar

Next Post

Mutum 15 Sun Mutu A Hatsarin Jirgin Ruwa A Sakkwato

Related

Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa
Daga Birnin Sin

Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa

8 minutes ago
Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

1 hour ago
An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa
Daga Birnin Sin

An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa

2 hours ago
Xi Ya Yi Kira Da A Yi Azamar Kare Rayukan Al’umma Yayin Da Ake Fuskantar Ibtila’in Ambaliya A Wasu Sassan Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Xi Ya Yi Kira Da A Yi Azamar Kare Rayukan Al’umma Yayin Da Ake Fuskantar Ibtila’in Ambaliya A Wasu Sassan Kasar Sin

3 hours ago
An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025

22 hours ago
Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa
Daga Birnin Sin

Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa

23 hours ago
Next Post
Mutum 15 Sun Mutu A Hatsarin Jirgin Ruwa A Sakkwato

Mutum 15 Sun Mutu A Hatsarin Jirgin Ruwa A Sakkwato

LABARAI MASU NASABA

Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa

Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa

July 29, 2025
Babu Wata Karamar Hukumar Dake ƘarÆ™ashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

Babu Wata Karamar Hukumar Dake ƘarÆ™ashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

July 29, 2025
Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

July 29, 2025
Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

July 29, 2025
An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa

An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa

July 29, 2025
Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

July 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Da A Yi Azamar Kare Rayukan Al’umma Yayin Da Ake Fuskantar Ibtila’in Ambaliya A Wasu Sassan Kasar Sin

Xi Ya Yi Kira Da A Yi Azamar Kare Rayukan Al’umma Yayin Da Ake Fuskantar Ibtila’in Ambaliya A Wasu Sassan Kasar Sin

July 29, 2025
Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

July 29, 2025
Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna

Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna

July 29, 2025
Kar Ka Zuga Ƴan Arewa Kan Tinubu — Nabena Ya Gargaɗi Kwankwaso

Kar Ka Zuga Ƴan Arewa Kan Tinubu — Nabena Ya Gargaɗi Kwankwaso

July 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.