ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Mai Wadata Za Ta Kara Samar Da Damammaki Ga Duniya

by CMG Hausa
3 years ago
Kasar Sin

A karshen wannan makon ne, aka kammala babban taron wakilan JKS na 20,bayan shafe kwanaki bakwai ana tattauna.

Bayan kammala taron ne kuma babban sakataren kwamitin kolin Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin Xi Jinping, ya jagoranci sauran shugabannin don ganawa da manema labarai na cikin gida da na waje, inda ya bayyana sabuwar alkiblar da kasar ta dosa, da yadda duniya za ta amfana daga jerin matakan da aka tsara aiwatarwa.

  • Sin Tana Maraba Da Kiran Taron Sulhu Tsakanin Al’ummomin Libya

Kamar yadda kasar Sin ta sha bayyanawa, a wannan karon ma, babban sakatare Xi ya kara nanata kudirin kasar Sin na samar da gudummawa ga sauran kasashen duniya wajen samun ci gaba, kuma bunkasuwar kasar Sin za ta yi tasiri ga duniya baki daya. A gabar da kasar ta kama hanyar zamanantar da kanta.

ADVERTISEMENT

Babban taron wata hanya ce ta kara daga tutar JKS, da hada karfi da karfe, da inganta hadin kai da sadaukarwa, don kara yiwa jama’a hidima da ma dogara da jama’a, da ci gaba da yin gyare-gyaren da suka dace da sabon tafarkin da aka sanya a gaba, sabanin yadda wasu jam’iyyun siyasa a kasashen yamma ke kara cusa jama’arsu cikin halin kunci, sakamakon hauhawar farashin kayayyaki da yaduwar annobar COVID-19 da nuna wariya da sauransu.

Batun kara bude kofarta ga kasashen ketare, da sa kaimi ga zurfafa yin gyare-gyare a cikin gida da bude kofa ga waje a dukkan fannoni, bai sauya ba.

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

Kuma ana iya ganin sakamakon haka, daga alkaluman da hukuma ta fitar dake nuna cewa, cinikayyar kayayyaki na ketare na kasar Sin, a cikin watanni 9 na farkon shekarar 2022 da muke ciki, ya karu da kashi 9.9 cikin 100, zuwa kudin Sin RMB Yuan triliyan 31.11, kwatankwacin dalar Amurka triliyan 4.75.

A cikin wannan wa’adi, cinikayyar kasar Sin da kasashen dake aiwatar da shawarar “ziri daya da hanya daya”, ya karu da kashi 20.7 cikin 100 kan makamancin lokaci na bara, zuwa Yuan triliyan 10.04.

Wannan yana kara tabbatar da cewa, tattalin arzikin kasar Sin yana da juriya da kuma dama mai kyau, kuma tushen sa mai karfi ba zai taba sauyawa ba, zai kuma ci gaba da kasancewa bisa yanayi mai kyau da inganci na dogon lokaci.

Don haka, kasar Sin mai wadata, za ta kara samar da damammaki ga duniya baki daya. Kuma kamar yadda kasar Sin ba za ta iya samun ci gaba ita kadai ba, haka ma duniya tana bukatar kasar Sin wajen samun bunkasuwarta.

Masana daga sassan daban-daban na nahiyar Afirka wadanda ke zama kawaye kuma aminan kasar Sin, su ma sun bayyana cewa, taron yana da babbar ma’ana, wanda zai haifar da babban tasiri ga kasar Sin, da kara kuzari ga kasashen duniya wajen yin hadin gwiwa don tinkarar kalubale da samun bunkasuwa tare.

Nasarorin da kasar Sin ta cimma a aikin zamanintar da kanta bisa tsarinta, sun karfafa gwiwar kasashen duniya musamman ma kasashe masu tasowa, wannan zai baiwa sauran kasashe masu tasowa damar zabar dabarun raya kasashensu dake dacewa da yanayinsu. Kowa ne tsuntsu dai kukan gidansu ya ke yi.

Masu fashin baki na fatan kasashen duniya za su koyi fasahohi da shirye-shiryen samun ci gaba na kasar Sin da kuma damar hadin gwiwa daga taron wakilan JKS karo na 20, ta yadda za a tafiyar da harkokin duniya da ma tinkarar kalubalen da duniya ke fuskanta tare. (Ibrahim Yaya)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow
Daga Birnin Sin

An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

December 20, 2025
An Fara Aiki Da Na’urar Fasahar Samar Da Lantarki Daga Iskar CO₂ Da Aka Sarrafa A Lardin Guizhou Na Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Fara Aiki Da Na’urar Fasahar Samar Da Lantarki Daga Iskar CO₂ Da Aka Sarrafa A Lardin Guizhou Na Kasar Sin

December 20, 2025
Next Post
Ya Kamata Amurka Ta Soke Takunkumi Idan Tana Son Taimakawa Afirka

Ya Kamata Amurka Ta Soke Takunkumi Idan Tana Son Taimakawa Afirka

LABARAI MASU NASABA

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.