• English
  • Business News
Tuesday, August 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Ta Dogara Ne Kan Gaskiya Da Adalci, Za Ta Kuma Ba Da Karin Taimakon Jin Kai Zuwa Gaza

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasar Sin Ta Dogara Ne Kan Gaskiya Da Adalci, Za Ta Kuma Ba Da Karin Taimakon Jin Kai Zuwa Gaza
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yau Alhamis 26 ga wata, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning ta jaddada cewa, matsayin da kasarta ta dauka ya dogara ne kan gaskiya da adalci, kuma yana mai da martani da kakkausar murya ta kasa da kasa, musamman ma ta kasashen Larabawa.

Jami’ar ta bayyana haka ne a yayin da take amsa tambayar da aka yi kan kin amincewar da kasar Sin ta yi game da daftarin kudurin halin da Falasdinu da Isra’ila ke ciki a kwamitin sulhu na MDD.

  • Xi Jinping Ya Gana Da Gwamnan Jihar California Dake Amurka
  • UNESCO Ta Yi Bikin Ranar Amfani Da Kafofin Watsa Labarai Da Yada Bayanai Ta Duniya A Abuja

Jami’ar ta nuna cewa, zaunannen wakilin kasar Sin a MDD Zhang Jun, ya riga ya yi karin haske kan matsayin kasar Sin a dukkan fannoni a jawabin da ya gabatar bayan kada kuri’a a kwamitin sulhu na MDD. Jami’ar ta kuma jaddada cewa, kasar Sin ba ta da wani muradi na son kai kan batun Falasdinu. Kasar Sin tana goyon bayan duk abin da zai taimaka wajen samar da zaman lafiya, kuma za ta yi iyakacin kokarinta wajen yin sulhu tsakanin Falasdinu da Isra’ila.

A ranar 25 ga watan Oktoba, kasashen Rasha da Sin sun yi watsi da daftarin kudurin kwamitin sulhu na MDD kan halin da ake ciki tsakanin Falasdinu da Isra’ila da Amurka ta tsara, sannan Hadaddiyar Daular Larabawa ita ma ta kada kuri’ar kin amincewa da shi. Baya ga haka, sakamakon adawar da kasashen Amurka da Birtaniya da wasu kasashe suka yi, ba a amince da daftarin kudirin da Rasha ta tsara ba.

Bugu da kari, kakakin hukumar kula da hadin gwiwar ci gaban kasa da kasa ta kasar Sin Xu Wei ya bayyana a yau Alhamis cewa, gwamnatin kasar Sin za ta sake ba da wani rukunin agajin gaggawa na Yuan miliyan 15 kwatankwacin dalar Amurka Miliyan 2.05, da suka hada da abinci da magunguna ga Gaza.

Labarai Masu Nasaba

An Samu Karuwar Adadin Kamfanoni Masu Yin Rajista A Yankin HK

Sashen Masana’antun Kirar Motoci Na kasar Sin Ya Samu Gi Gaba A Watan Yuli

Xu ya kara da ce, kasar Sin tana bakin cikin ganin yadda rikicin Falasdinu da Isra’ila ya haifar da hasarar rayukan fararen hula da dama da kuma tabarbarewar yanayin jin kai a Gaza.

Ya kara da cewa, don taimakawa wajen shawo kan matsalar jin kai a Gaza, kasar Sin ta riga ta ba da tsabar kudi dalar Amurka miliyan 1 ta hannun hukumar ba da agaji ta MDD mai kula da ‘yan gudun hijirar Falasdinu a gabas ta kusa da kuma hukumar Falasdinawa a lokuta daban-daban.

(Mai fassara: Bilkisu Xin)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kimiyya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kimiyya Ba Dabarar Takara Ba Ce

Next Post

Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Kare Ci Gaban Mata A Duniya

Related

An Samu Karuwar Adadin Kamfanoni Masu Yin Rajista A Yankin HK
Daga Birnin Sin

An Samu Karuwar Adadin Kamfanoni Masu Yin Rajista A Yankin HK

15 hours ago
Sashen Masana’antun Kirar Motoci Na kasar Sin Ya Samu Gi Gaba A Watan Yuli
Daga Birnin Sin

Sashen Masana’antun Kirar Motoci Na kasar Sin Ya Samu Gi Gaba A Watan Yuli

16 hours ago
Tattalin Arzikin Kasar Sin Na Da Makoma Mai Haske In Ji Wani Kwararre 
Daga Birnin Sin

Tattalin Arzikin Kasar Sin Na Da Makoma Mai Haske In Ji Wani Kwararre 

18 hours ago
Sin Ta Kammala Yi Wa Yankuna 5 Na Kare Muhalli Da Halittu Na Kasar Rajista
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kammala Yi Wa Yankuna 5 Na Kare Muhalli Da Halittu Na Kasar Rajista

18 hours ago
Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro
Daga Birnin Sin

Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro

20 hours ago
Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK
Daga Birnin Sin

Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK

2 days ago
Next Post
Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Kare Ci Gaban Mata A Duniya

Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Kare Ci Gaban Mata A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

Jagora A ADC Ya Ƙaryata Zargin Atiku Ya Kankane Komai A Jam’iyyar

August 12, 2025
’Yan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 6 A Taraba

’Yan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 6 A Taraba

August 12, 2025
Sadiq Umar Da Bello El-Rufai Sun Sayi Ƙungiyar Rancher Bees FC Ta Kaduna

Sadiq Umar Da Bello El-Rufai Sun Sayi Ƙungiyar Rancher Bees FC Ta Kaduna

August 12, 2025
Ba Iya Yunwa Ce Kaɗai Ke Kashe Ƙananan Yara A Katsina Ba – Gwamnati

Ba Iya Yunwa Ce Kaɗai Ke Kashe Ƙananan Yara A Katsina Ba – Gwamnati

August 12, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Batun Rashin Lafiyar Tinubu

August 12, 2025
Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi

Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi

August 11, 2025
Tireloli Sun Yi Taho Mu Gama, Mutane 4 Sun Jikkata A Titin Zariya–Kaduna

Tireloli Sun Yi Taho Mu Gama, Mutane 4 Sun Jikkata A Titin Zariya–Kaduna

August 11, 2025
An Samu Karuwar Adadin Kamfanoni Masu Yin Rajista A Yankin HK

An Samu Karuwar Adadin Kamfanoni Masu Yin Rajista A Yankin HK

August 11, 2025
Sashen Masana’antun Kirar Motoci Na kasar Sin Ya Samu Gi Gaba A Watan Yuli

Sashen Masana’antun Kirar Motoci Na kasar Sin Ya Samu Gi Gaba A Watan Yuli

August 11, 2025
Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Don Yi Wa Iyalan Ogbeh Ta’aziyya

Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Don Yi Wa Iyalan Ogbeh Ta’aziyya

August 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.