• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Ta Dogara Ne Kan Gaskiya Da Adalci, Za Ta Kuma Ba Da Karin Taimakon Jin Kai Zuwa Gaza

by CGTN Hausa
2 years ago
Sin

A yau Alhamis 26 ga wata, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning ta jaddada cewa, matsayin da kasarta ta dauka ya dogara ne kan gaskiya da adalci, kuma yana mai da martani da kakkausar murya ta kasa da kasa, musamman ma ta kasashen Larabawa.

Jami’ar ta bayyana haka ne a yayin da take amsa tambayar da aka yi kan kin amincewar da kasar Sin ta yi game da daftarin kudurin halin da Falasdinu da Isra’ila ke ciki a kwamitin sulhu na MDD.

  • Xi Jinping Ya Gana Da Gwamnan Jihar California Dake Amurka
  • UNESCO Ta Yi Bikin Ranar Amfani Da Kafofin Watsa Labarai Da Yada Bayanai Ta Duniya A Abuja

Jami’ar ta nuna cewa, zaunannen wakilin kasar Sin a MDD Zhang Jun, ya riga ya yi karin haske kan matsayin kasar Sin a dukkan fannoni a jawabin da ya gabatar bayan kada kuri’a a kwamitin sulhu na MDD. Jami’ar ta kuma jaddada cewa, kasar Sin ba ta da wani muradi na son kai kan batun Falasdinu. Kasar Sin tana goyon bayan duk abin da zai taimaka wajen samar da zaman lafiya, kuma za ta yi iyakacin kokarinta wajen yin sulhu tsakanin Falasdinu da Isra’ila.

A ranar 25 ga watan Oktoba, kasashen Rasha da Sin sun yi watsi da daftarin kudurin kwamitin sulhu na MDD kan halin da ake ciki tsakanin Falasdinu da Isra’ila da Amurka ta tsara, sannan Hadaddiyar Daular Larabawa ita ma ta kada kuri’ar kin amincewa da shi. Baya ga haka, sakamakon adawar da kasashen Amurka da Birtaniya da wasu kasashe suka yi, ba a amince da daftarin kudirin da Rasha ta tsara ba.

Bugu da kari, kakakin hukumar kula da hadin gwiwar ci gaban kasa da kasa ta kasar Sin Xu Wei ya bayyana a yau Alhamis cewa, gwamnatin kasar Sin za ta sake ba da wani rukunin agajin gaggawa na Yuan miliyan 15 kwatankwacin dalar Amurka Miliyan 2.05, da suka hada da abinci da magunguna ga Gaza.

LABARAI MASU NASABA

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

Xu ya kara da ce, kasar Sin tana bakin cikin ganin yadda rikicin Falasdinu da Isra’ila ya haifar da hasarar rayukan fararen hula da dama da kuma tabarbarewar yanayin jin kai a Gaza.

Ya kara da cewa, don taimakawa wajen shawo kan matsalar jin kai a Gaza, kasar Sin ta riga ta ba da tsabar kudi dalar Amurka miliyan 1 ta hannun hukumar ba da agaji ta MDD mai kula da ‘yan gudun hijirar Falasdinu a gabas ta kusa da kuma hukumar Falasdinawa a lokuta daban-daban.

(Mai fassara: Bilkisu Xin)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka
Daga Birnin Sin

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani
Daga Birnin Sin

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025
Next Post
Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Kare Ci Gaban Mata A Duniya

Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Kare Ci Gaban Mata A Duniya

LABARAI MASU NASABA

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

October 28, 2025
Mutum 18 Sun Mutu, 40 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kebbi 

An Kashe Mutum 10 A Harin Ramuwar Gayya A Jihar Kebbi

October 28, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Zargin Almundahana: An Ɗage Shari’ar  Ganduje Da Matarsa Saboda Rashin Miƙa Takardu

October 28, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Sojoji Sun Kashe Masu Yi Wa ISWAP 4 Safarar Makamai A Borno

October 28, 2025
Sin

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.