• English
  • Business News
Saturday, October 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 months ago
Sin

An bude taron baje kolin cinikayya da zuba jari na duniya karo na 25 a birnin Xiamen na lardin Fujian na kasar Sin, a jiya Litinin. 

 

Hakika baje kolin cinikayya da zuba jari babban jigo ne ga habakar tattalin arzikin duniya bisa la’akari da kyakkyawan tasirinsa da yadda yake samar da wani cikakken dandali da ya hada bangarori da dama daga gwamnatoci da ’yan kasuwa zuwa dukkan masu ruwa da tsaki.

  • Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 
  • Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

Yayin da duniya ke shiga sabon zamani na cudanyar bangarori daban-daban da rarrabuwar iko tsakanin kasashe maimakon kasancewa karkashin ikon wasu ’yan tsiraru, hanyar ganin dorewar hakan ita ce hadin gwiwa da bude kofa da cin moriyar juna.

 

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

Sabanin yadda wasu kasashe ke tayar da takaddamar cinikayya da kawo cikas ga ci gaban tattalin arziki da tsarin samar da kayayyaki a duniya, kasar Sin ta tsaya tsayin daka wajen ganin duniya ta samu ci gaba, musammam kasashe masu tasowa, ta hanyar bude kofa da yin komai cikin adalci.

 

A duk inda aka ambaci “Babba”, to a ko da yaushe, shi ne mai nuna sanin ya kamata da tallafawa da jagorantar na kasa, domin su zamo masu dogaro da kan su da bin daidaitacciyar hanya. Wannan kuma ya yi daidai da dabaru da manufofin kasar Sin, inda take mayar da hankali kan yadda za a gudu tare a tsira tare tsakaninta da kasashe masu tasowa.

 

A sakonsa na murnar bude baje kolin, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya nanata cewa, kasarsa za ta fadada bude kofa domin kara kuzari da tabbaci ga ci gaban duniya. Bude kofar kasar Sin ba dama ce kawai ga kasashe su shigo su ci gajiyar babbar kasuwarta ba, ya kara bayar da dama tare da zama dandalin da kasa da kasa za su hadu, su kulla huldar cinikayya da zuba jari.

 

Baje kolin cinikayya da zuba jari, yana kawo nesa kusa, wato yana saukakawa da dunkule hanyoyi masu sarkakiya kamar na binciken kasuwa, haduwar ’yan kasuwa da tattaunawa a wuri guda, lamarin dake kara fa’ida da daraja ga kasashe da kayayyaki da masana’antu da fadada hanyoyin kasuwanci har ma da rage kudin da ake kashewa. Ke nan, irin wannan bude kofa da Sin ke kara fadada aiwatarwa kasashen duniya suke bukata domin tsayawa da kafarsu da inganta cudanya a tsakaninsu, ta yadda za a kai ga dunkule tattalin arzikin duniya da wanzar da zaman lafiya a tsakaninsu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

October 24, 2025
An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan
Daga Birnin Sin

An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 24, 2025
Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

October 24, 2025
Next Post
majalisar kasa

Majalisa Ta Bai Wa Minista Sa'o'i 48 Ya Bayyana A Gabanta Kan Hatsarin Jirgin Abuja Zuwa Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Gwarzon Kamfanin Fasahar Kuɗaɗe Na Shekarar 2025, Opay Nigeria

Gwarzon Kamfanin Fasahar Kuɗaɗe Na Shekarar 2025, Opay Nigeria

October 25, 2025

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kaya Na Shekarar 2025, Kamfanin Nestlé Pure Life

October 25, 2025
Mata Ne Ginshikin Ci-Gaban Al’umma – Gimbiyar Dange

Mata Ne Ginshikin Ci-Gaban Al’umma – Gimbiyar Dange

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Mawaƙin Shekarar 2025, Skales

October 25, 2025
Jami’ar ABU Ta Ƙaryata Zargin Ƙera Makamin Nukiliya A Asirce

Jami’ar ABU Ta Ƙaryata Zargin Ƙera Makamin Nukiliya A Asirce

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Hukumar Kare Ƴancin Masu Amfani Da Kaya (FCCPC): Tabbatar Da Adalci A Kasuwa

October 25, 2025
Fiye da Janarori 50 Za Su Yi Ritaya Bayan Sabbin Naɗe-Naɗen Tinubu

Fiye da Janarori 50 Za Su Yi Ritaya Bayan Sabbin Naɗe-Naɗen Tinubu

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Ma’aikacin Banki Na Shekarar 2025 Dakta Tony Okpanachi

October 25, 2025
Muna Duba Ƙudirin Ƙirƙiro Jihohi 55 – Barau Jibrin

Muna Duba Ƙudirin Ƙirƙiro Jihohi 55 – Barau Jibrin

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Shugaban Kamfani Na Shekarar 2025 Gbenga Olu Komolafe

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.