• English
  • Business News
Friday, October 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 weeks ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An bude taron baje kolin cinikayya da zuba jari na duniya karo na 25 a birnin Xiamen na lardin Fujian na kasar Sin, a jiya Litinin. 

 

Hakika baje kolin cinikayya da zuba jari babban jigo ne ga habakar tattalin arzikin duniya bisa la’akari da kyakkyawan tasirinsa da yadda yake samar da wani cikakken dandali da ya hada bangarori da dama daga gwamnatoci da ’yan kasuwa zuwa dukkan masu ruwa da tsaki.

  • Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 
  • Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

Yayin da duniya ke shiga sabon zamani na cudanyar bangarori daban-daban da rarrabuwar iko tsakanin kasashe maimakon kasancewa karkashin ikon wasu ’yan tsiraru, hanyar ganin dorewar hakan ita ce hadin gwiwa da bude kofa da cin moriyar juna.

 

Labarai Masu Nasaba

Manyan Jami’an Kasashen Afirka Suna Fatan Fadada Hadin Gwiwa Da Kasar Sin

Balaguron Fasinjoji Ta Jirgin Kasa A Kasar Sin Ya Kai Matsayi Mafi Girma A Bikin Ranar Kafuwar PRC

Sabanin yadda wasu kasashe ke tayar da takaddamar cinikayya da kawo cikas ga ci gaban tattalin arziki da tsarin samar da kayayyaki a duniya, kasar Sin ta tsaya tsayin daka wajen ganin duniya ta samu ci gaba, musammam kasashe masu tasowa, ta hanyar bude kofa da yin komai cikin adalci.

 

A duk inda aka ambaci “Babba”, to a ko da yaushe, shi ne mai nuna sanin ya kamata da tallafawa da jagorantar na kasa, domin su zamo masu dogaro da kan su da bin daidaitacciyar hanya. Wannan kuma ya yi daidai da dabaru da manufofin kasar Sin, inda take mayar da hankali kan yadda za a gudu tare a tsira tare tsakaninta da kasashe masu tasowa.

 

A sakonsa na murnar bude baje kolin, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya nanata cewa, kasarsa za ta fadada bude kofa domin kara kuzari da tabbaci ga ci gaban duniya. Bude kofar kasar Sin ba dama ce kawai ga kasashe su shigo su ci gajiyar babbar kasuwarta ba, ya kara bayar da dama tare da zama dandalin da kasa da kasa za su hadu, su kulla huldar cinikayya da zuba jari.

 

Baje kolin cinikayya da zuba jari, yana kawo nesa kusa, wato yana saukakawa da dunkule hanyoyi masu sarkakiya kamar na binciken kasuwa, haduwar ’yan kasuwa da tattaunawa a wuri guda, lamarin dake kara fa’ida da daraja ga kasashe da kayayyaki da masana’antu da fadada hanyoyin kasuwanci har ma da rage kudin da ake kashewa. Ke nan, irin wannan bude kofa da Sin ke kara fadada aiwatarwa kasashen duniya suke bukata domin tsayawa da kafarsu da inganta cudanya a tsakaninsu, ta yadda za a kai ga dunkule tattalin arzikin duniya da wanzar da zaman lafiya a tsakaninsu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

IATF 2025: Zamfara A Shirye Ta Ke Wajen Maraba Da Masu Zuba Jari – Gwamna Lawal 

Next Post

Majalisa Ta Bai Wa Minista Sa’o’i 48 Ya Bayyana A Gabanta Kan Hatsarin Jirgin Abuja Zuwa Kaduna

Related

Manyan Jami’an Kasashen Afirka Suna Fatan Fadada Hadin Gwiwa Da Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Manyan Jami’an Kasashen Afirka Suna Fatan Fadada Hadin Gwiwa Da Kasar Sin

18 hours ago
Balaguron Fasinjoji Ta Jirgin Kasa A Kasar Sin Ya Kai Matsayi Mafi Girma A Bikin Ranar Kafuwar PRC
Daga Birnin Sin

Balaguron Fasinjoji Ta Jirgin Kasa A Kasar Sin Ya Kai Matsayi Mafi Girma A Bikin Ranar Kafuwar PRC

20 hours ago
Xi Ya Taya Jami’ar Tianjin Murnar Cika Shekaru 130 Da Kafuwa
Daga Birnin Sin

Xi Ya Taya Jami’ar Tianjin Murnar Cika Shekaru 130 Da Kafuwa

22 hours ago
Kasar Sin Ta Nuna Takaici Da Matakin Amurka Na Kin Amincewa Da Daftarin Kudurin Gaza
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Nuna Takaici Da Matakin Amurka Na Kin Amincewa Da Daftarin Kudurin Gaza

23 hours ago
Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Gwamnatin Amurka Ta Tsayar Da Ayyukanta
Daga Birnin Sin

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Gwamnatin Amurka Ta Tsayar Da Ayyukanta

2 days ago
Masana’antar AI Ta Kasar Sin Ta Samu Habaka Da Kamfanoni Fiye Da 5300
Daga Birnin Sin

Masana’antar AI Ta Kasar Sin Ta Samu Habaka Da Kamfanoni Fiye Da 5300

2 days ago
Next Post
majalisar kasa

Majalisa Ta Bai Wa Minista Sa'o'i 48 Ya Bayyana A Gabanta Kan Hatsarin Jirgin Abuja Zuwa Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Yadda Na Ji Bayan Faduwa Zaben 2015 – Jonathan 

Ko Jonathan Zai Iya Ja Da Tinubu A 2027?

October 3, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

PENGASSAN Ta Yi Watsi Da Tayin Dangote Na Biyan Ma’aikata Albashin Shekaru 5 Ba Tare Da Yin Aiki Ba

October 3, 2025
NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja

NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja

October 3, 2025
Goron Sallah

GORON JUMA’A

October 3, 2025
NDLEA Ta Kama Kilo 588 Na Miyagun Ƙwayoyi, Ta Ƙona Hekta 6 Na Gonakin Wiwi A Adamawa

NDLEA Ta Kama Kilo 588 Na Miyagun Ƙwayoyi, Ta Ƙona Hekta 6 Na Gonakin Wiwi A Adamawa

October 3, 2025
Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taba Yi

Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taba Yi

October 3, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

‘Yan Nijeriya Na Karbar Sakamakonsu Da Hannun Hagu A Wajen Tinubu – Atiku

October 3, 2025
Raya Al’ada: Bikin Kalankuwa Na 2025 A Kano

Raya Al’ada: Bikin Kalankuwa Na 2025 A Kano

October 3, 2025
Za mu Inganta Fannin Karatun Alkur’ani – Gwamnan Jigawa

Za mu Inganta Fannin Karatun Alkur’ani – Gwamnan Jigawa

October 3, 2025
Yadda Sanata Barau Ke Samar da Masana Don Ci Gaban Kano

Yadda Sanata Barau Ke Samar da Masana Don Ci Gaban Kano

October 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.