Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Mao Ning, ta bayyana a yayin taron manema labarai na yau da kullum Jumma’ar nan cewa, kasar Sin za ta ci gaba da inganta hadin gwiwa da sauran kasashe a fannin kimiyya da fasaha da kirkire-kirkire tare da bude kofa ga kasashen ketare.
Alkaluman ci gaban kirkire-kirkire na kasa da kasa na shekarar 2022 da hukumar kare ikon mallakar fasaha ta duniya (WIPO) ta fitar jiya Alhamis, ya nuna cewa, kasar Sin ta zo ta 11 a kididigar kirkire-kirkire ta duniya, karuwar mataki daya kan na shekarar da ta gabata.
Mao ta ce, wannan ya sake tabbatar da manyan nasarorin da kasar ta samu a fannin kare ikon mallakar fasaha. Kasar Sin tana dora muhimmanci matuka kan kirkire-kirkire na kimiyya da fasaha da cudanya a fannin sadarwar zamani ta duniya, da kare ikon mallakar fasaha yadda ya kamata, da karfafa hadin gwiwar kasa da kasa kan kirkire-kirkire da kimiyya da fasaha a dukkan fannoni.
A cikin shekaru 10 da suka gabata, kasar Sin ta rungumi hanyar raya ikon mallakar fasaha mai sigar musamman na kasar Sin.(Ibrahim)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp