• English
  • Business News
Wednesday, September 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Za Ta Tsaya Kan Manufar Bude Kofarta Ga Duniya

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasar Sin Za Ta Tsaya Kan Manufar Bude Kofarta Ga Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Firaministan kasar Sin mista Li Keqiang ya ce, tattalin arzikin kasarsa ya hade da na duniya cikin wani matsayi mai zurfi, kana bude kofarta ga duniya wata babbar manufa ce ta kasar.

Saboda haka, Sin za ta tsaya kan wannan muhimmiyar manufa, gami da kokarin inganta harkoki a wannan fanni.

  • Wani Dan Kasuwan Kasar Sin Ya Bullo Da Shirin Magance Matsalar Gurbataccen Ruwa Sha A Nahiyar Afirka

Mista Li ya fadi haka ne a jiya Talata, yayin da yake halartar taron manyan ‘yan kasuwan kasashe daban daban karkashin laimar dandalin tattauna tattalin arzikin duniya, wanda ya gudana ta kafar bidiyo.

A cewar firaministan kasar Sin, manufar bude kofar kasar ta shafi kasashe masu sukuni, da wadanda ke kan hanyar tasowa.

Sa’an nan kasar Sin za ta ci gaba da kokarin kare tsarin ciniki da ya shafi bangarori daban daban, da kungiyar ciniki ta duniya WTO take jagoranta, da sa kaimi ga yin ciniki cikin ‘yanci da adalci.

Labarai Masu Nasaba

Sabuwar Ajandar Mulkin Duniya Ta Nuna Alhakin Da Kasar Sin Ta Dauka

Babban Sakataren MDD: Sin Ta Taka Rawar Gani Sosai Wajen Cimma Nasarar Yakin Duniya Na Biyu

Firaminista Li ya kara da cewa, kasarsa za ta kara kokarin daidaita muhallin gudanar da harkokin kasuwanci, da daukar matakan kandagarkin annobar COVID-19 masu dacewa, da kyautata yanayin ayyukan samar da izinin shiga kasar, da gudanar da gwajin kwayoyin cutar COVID-19. Haka kuma za ta taimakawa mutanen da suke neman yin ciniki ko aiki a kasashen ketare, don inganta mu’ammalar jama’ar Sin da ta kasashen waje.

Ban da wannan kuma, babban jami’in ya nanata cewa, kasar Sin za ta kiyaye manyan manufofinta na yanzu, don tabbatar da cimma burinta na raya tattalin arziki zuwa wani matsayin da take bukata, a wannan shekarar da muke ciki. Ya ce, sabon zagayen yaduwar cutar COVID-19 a duniya gami da sauran abubuwan da ba a iya hasashensu ba, sun sa tattalin arzikin Sin fuskantar matsi.

Duk da haka, a cewar firaministan, matakan daidaita yanayin da gwamnatin kasar Sin ta dauka, musamman ma wadanda suka shafi ba da tallafi ga kamfanoni, da shawo kan hauhawar farashin kayayyaki, sun yi amfani, inda suka sanya tattalin arzikin kasar komawa yanayi na karuwa, sai dai kuma ana bukatar daukar karin matakai don tabbatar da dorewar yanayin. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mai Dokar Barci…

Next Post

Matsalar Tsaro: Gwamnati Da Hukumomin Tsaro Sun Gaza – Masari

Related

Sabuwar Ajandar Mulkin Duniya Ta Nuna Alhakin Da Kasar Sin Ta Dauka
Daga Birnin Sin

Sabuwar Ajandar Mulkin Duniya Ta Nuna Alhakin Da Kasar Sin Ta Dauka

19 minutes ago
Babban Sakataren MDD: Sin Ta Taka Rawar Gani Sosai Wajen Cimma Nasarar Yakin Duniya Na Biyu
Daga Birnin Sin

Babban Sakataren MDD: Sin Ta Taka Rawar Gani Sosai Wajen Cimma Nasarar Yakin Duniya Na Biyu

1 hour ago
Shugaban Uganda: Jarin Sin Na Taimakawa Wajen Bunkasa Ci Gaban Kasashen Afirka
Daga Birnin Sin

Shugaban Uganda: Jarin Sin Na Taimakawa Wajen Bunkasa Ci Gaban Kasashen Afirka

1 hour ago
Xi: Alakar Sin Da Rasha Ta Zama Misali Na Kyakkyawar Dangantakar Manyan Kasashe
Daga Birnin Sin

Xi: Alakar Sin Da Rasha Ta Zama Misali Na Kyakkyawar Dangantakar Manyan Kasashe

3 hours ago
Xi Jinping Ya Jagoranci Taro Karo Na Bakwai Tsakanin Shugabannin Kasashen Sin Da Rasha Da Mongoliya
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Jagoranci Taro Karo Na Bakwai Tsakanin Shugabannin Kasashen Sin Da Rasha Da Mongoliya

3 hours ago
Sabuwar Ajandar Kasar Sin Ta Inganta Magance Gibin Kudi A Duniya
Daga Birnin Sin

Sabuwar Ajandar Kasar Sin Ta Inganta Magance Gibin Kudi A Duniya

4 hours ago
Next Post
Matsalar Tsaro: Gwamnati Da Hukumomin Tsaro Sun Gaza – Masari

Matsalar Tsaro: Gwamnati Da Hukumomin Tsaro Sun Gaza – Masari

LABARAI MASU NASABA

Sabuwar Ajandar Mulkin Duniya Ta Nuna Alhakin Da Kasar Sin Ta Dauka

Sabuwar Ajandar Mulkin Duniya Ta Nuna Alhakin Da Kasar Sin Ta Dauka

September 2, 2025
Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

September 2, 2025
Gwamna Dauda Lawal A Shekara 60: Inda Akwai Fata, Akwai Mafita

Gwamna Dauda Lawal A Shekara 60: Inda Akwai Fata, Akwai Mafita

September 2, 2025
Babban Sakataren MDD: Sin Ta Taka Rawar Gani Sosai Wajen Cimma Nasarar Yakin Duniya Na Biyu

Babban Sakataren MDD: Sin Ta Taka Rawar Gani Sosai Wajen Cimma Nasarar Yakin Duniya Na Biyu

September 2, 2025
Shugaban Uganda: Jarin Sin Na Taimakawa Wajen Bunkasa Ci Gaban Kasashen Afirka

Shugaban Uganda: Jarin Sin Na Taimakawa Wajen Bunkasa Ci Gaban Kasashen Afirka

September 2, 2025
Gwamna Yusuf

Gwamna Yusuf Zai Kaddamar Da Majalisar Shurah Ta Jihar Kano

September 2, 2025
Xi: Alakar Sin Da Rasha Ta Zama Misali Na Kyakkyawar Dangantakar Manyan Kasashe

Xi: Alakar Sin Da Rasha Ta Zama Misali Na Kyakkyawar Dangantakar Manyan Kasashe

September 2, 2025
Xi Jinping Ya Jagoranci Taro Karo Na Bakwai Tsakanin Shugabannin Kasashen Sin Da Rasha Da Mongoliya

Xi Jinping Ya Jagoranci Taro Karo Na Bakwai Tsakanin Shugabannin Kasashen Sin Da Rasha Da Mongoliya

September 2, 2025
Da Ɗum-ɗumi: Tinubu Ya Mayar Da Shugabannin NTA Kan Muƙamansu Bayan Dakatar Da Su A Baya

Da Ɗum-ɗumi: Tinubu Ya Mayar Da Shugabannin NTA Kan Muƙamansu Bayan Dakatar Da Su A Baya

September 2, 2025
Sabuwar Ajandar Kasar Sin Ta Inganta Magance Gibin Kudi A Duniya

Sabuwar Ajandar Kasar Sin Ta Inganta Magance Gibin Kudi A Duniya

September 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.