• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasashen Afirka Biyar Da Suka Fi Karfin Soji

by Rabi'u Ali Indabawa
5 months ago
in Labarai
0
Kasashen Afirka Biyar Da Suka Fi Karfin Soji
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar nan ta kasa da kasa, ta Global Firepower, mai fitar da jadawalin mizanin karfin sojojin kasashen duniya, ta fitar da rahoton da ke cewa a shekara ta 2025 Nijeriya ta kasance ta 39 a karfin soji daga cikin kasashe 145 na duniya.

Shekaru uku jere karfin sojojin kasar na raguwa kamar yadda rahoton kungiyar ya nuna.

  • Ayyukan Jami’an Ilimi Da Muhimmancinsu (3)
  • Za Mu FarfaÉ—o Da Masana’antun Dinki 44 Da Aka Yi Watsi Da Su – Gwamnatin Kano

A duniya, Amurka ce ta farko a jadawalin inda ta shafe shekaru 18 jere tana kan matsayin.

Sauran kasashen da suke baza karfin sojinsu sun hada da Rasha, da China, da Indiya, da kuma Koriya ta Kudu wadda ta kasance kasa ta biyar a duniya da take da karfin soji.

Mun yi nazarin jadawalin da kungiyar ta fitar ga kuma jerin kasashe biyar da suka fi karfin soji a nahiyar Afirka.

Labarai Masu Nasaba

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don ÆŠaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

Masar

Masar ce kasa ta farko a nahiyar Afirka kuma ta 19 cikin kasashe 145 na duniya da kungiyar ta yi nazarin karfin sojinsu a 2024.

Kungiyar ta GFP ta bayyana cewa Masar tana bajekolin kokarin da take na zamanantar da tsarin tsaronta inda take da dubban motocin sulke da sauran makaman yaki.

Masar ta rike wannan matsayi ne saboda yadda take iya kera manyan makamai na fasaha, da yawan ma’aikatanta, da karfin sojin ruwanta, da na jiragen sama na musamman, da kuma kasafin tsaro mai yawa.

Shugaba Abdel Fattah El-Sisi ya bayar da gudummawa wajen samar da gagarumin ci gaba a fannin karfin soji da sabunta makaman kasar. Kasar ta kulla alaka mai karfi da kasashen duniya wajen habaka dakarun kasar.

yawan sojojin Masar sun kai dubu dari hudu da arba’in yayin da take da jiragen yaki 238.

Masar na kashe kusan dala biliyan shida duk shekara a harkokinta na tsaro, kamar yadda nazarin GFP ya bayyana.

Aljeriya

Aljeriya ce ta biyu bayan Masar wajen karfin soji a nahiyar Afirka inda kuma a jerin kasashen duniya ta kasance ta 25.

Kamar kowace kasa, Aljeriya tana da sojoji na kasa na ruwa da kuma na sama kari da dakarun tsaron sararin samaniya wadda ta maye gurbin sojin National Liberation Army, wani bangare na kungiyar National Liberation Front da ta yi yaki da mulkin mallakar Faransa lokacin yakin nemar wa Aljeriya ‘yancin gashin kai tsakanin shekarar 1954 zuwa 1962.

Kungiyar ta GFP ta kiyasta cewa kasafin da kasar ke ware wa bangaren tsaronta duk shekara ya kai Dala biliyan 25.

Tana kuma da jiragen yaki 102 da sojoji dubu dari uku da ashirin da biyar.

Nijeriya

Nijeriya ce ta uku a Afirka, kuma ta 31 a duniya cikin kasashe 145 inda ta samu maki 0.5771.

Nijeriya tana bayar da gudummawa sosai wajen samar da tsaro a yammacin Afirka saboda kasafin kudin da take ware wa tsaro da kuma ayyukan sabunta makaman yaki.

A cikin gida kuma, dakarun kasar na bayar da gudummawa wajen murkushe ayyukan ta’addanci musamman a yankin arewa maso gabas sannan kuma ta kasance daya daga cikin na gaba-gaba a Afirka da ke kokarin wanzar da zaman lafiya a duk lokacin da aka samu barkewar hatsaniya a wata kasa ta nahiyar.

A kasafin kudin da gwamnatin kasar ta ware wa bangaren tsaron ya kai naira tiriliyan 4.91, fiye da adadin da aka ware wa bangaren a kasafin da ya gabata.

A jadawalin GFP, Nijeriya tana ware sama da dala biliyan uku a jumulla wajen tafiyar da al’amuran tsaron kasar duk shekara.

Tana kuma da jirage yaki 14 sannan yawan sojojinta sun kai 230,000.

Afirka ta Kudu

Afirka ta Kudu ce kasar da ke biyewa Nijeriya inda ta zo ta hudu a Afirka kuma ta 40 a duniya.

Afirka ta Kudu ta yi fice wajen amfani da makamai na zamani da kwararrun sojoji saboda albarkatun kasar da take da su.

Kasa ce da ta fifita tsaronta sannan kuma tana shiga ayyukan wanzar da zaman lafiya a kasashen da aka samu tarzoma.

GFP ta bayyana cewa kasar tana ware dala biliyan 2,266,800,000 a matsayin kudin ta take kashewa a bangaren tsaronta.

Sannan kuma tana da yawan sojojin da suka kai 71, 235 hadi da jiragen yaki biyu.

Habasha

Habasha ta kasance ta biyar a Afirka kuma ta 52 a duniya a karfin soji

Kungiyar ta GFP ta bayyana cewa Habasha ta ware sama da dala biliyan biyu don tafiyar da harkokin tsaron kasar.

A cewar jadawalin, kasar tana da yawan jiragen yaki da suka kai 25 sannan yawan sojojinta sun kai dubu dari da sittin da biyu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: MasarNijeriyaSoji
ShareTweetSendShare
Previous Post

Turji Na Neman Hanyar Tsira Yayin Da Sojoji Suka Farmaki Mayaƙansa Tare Da Harbe Ɗansa 

Next Post

Rundunar Tsaro Ta Kashe ‘Yan Bindiga 7, Ta Kwato Shanu 109 Da Aka Sace A Katsina

Related

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki
Manyan Labarai

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

10 hours ago
JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don ÆŠaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa
Ilimi

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don ÆŠaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

11 hours ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

12 hours ago
Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS
Labarai

Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

14 hours ago
Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su
Manyan Labarai

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

16 hours ago
Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas

17 hours ago
Next Post
Sojoji

Rundunar Tsaro Ta Kashe ‘Yan Bindiga 7, Ta Kwato Shanu 109 Da Aka Sace A Katsina

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

June 27, 2025
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

June 27, 2025
Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

June 27, 2025
Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

June 27, 2025
Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

June 27, 2025
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

June 27, 2025
Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

June 27, 2025
JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don ÆŠaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don ÆŠaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.