ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasashen Afirka Biyar Da Suka Fi Karfin Soji

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
Afirka

Kungiyar nan ta kasa da kasa, ta Global Firepower, mai fitar da jadawalin mizanin karfin sojojin kasashen duniya, ta fitar da rahoton da ke cewa a shekara ta 2025 Nijeriya ta kasance ta 39 a karfin soji daga cikin kasashe 145 na duniya.

Shekaru uku jere karfin sojojin kasar na raguwa kamar yadda rahoton kungiyar ya nuna.

  • Ayyukan Jami’an Ilimi Da Muhimmancinsu (3)
  • Za Mu Farfaɗo Da Masana’antun Dinki 44 Da Aka Yi Watsi Da Su – Gwamnatin Kano

A duniya, Amurka ce ta farko a jadawalin inda ta shafe shekaru 18 jere tana kan matsayin.

ADVERTISEMENT

Sauran kasashen da suke baza karfin sojinsu sun hada da Rasha, da China, da Indiya, da kuma Koriya ta Kudu wadda ta kasance kasa ta biyar a duniya da take da karfin soji.

Mun yi nazarin jadawalin da kungiyar ta fitar ga kuma jerin kasashe biyar da suka fi karfin soji a nahiyar Afirka.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Masar

Masar ce kasa ta farko a nahiyar Afirka kuma ta 19 cikin kasashe 145 na duniya da kungiyar ta yi nazarin karfin sojinsu a 2024.

Kungiyar ta GFP ta bayyana cewa Masar tana bajekolin kokarin da take na zamanantar da tsarin tsaronta inda take da dubban motocin sulke da sauran makaman yaki.

Masar ta rike wannan matsayi ne saboda yadda take iya kera manyan makamai na fasaha, da yawan ma’aikatanta, da karfin sojin ruwanta, da na jiragen sama na musamman, da kuma kasafin tsaro mai yawa.

Shugaba Abdel Fattah El-Sisi ya bayar da gudummawa wajen samar da gagarumin ci gaba a fannin karfin soji da sabunta makaman kasar. Kasar ta kulla alaka mai karfi da kasashen duniya wajen habaka dakarun kasar.

yawan sojojin Masar sun kai dubu dari hudu da arba’in yayin da take da jiragen yaki 238.

Masar na kashe kusan dala biliyan shida duk shekara a harkokinta na tsaro, kamar yadda nazarin GFP ya bayyana.

Aljeriya

Aljeriya ce ta biyu bayan Masar wajen karfin soji a nahiyar Afirka inda kuma a jerin kasashen duniya ta kasance ta 25.

Kamar kowace kasa, Aljeriya tana da sojoji na kasa na ruwa da kuma na sama kari da dakarun tsaron sararin samaniya wadda ta maye gurbin sojin National Liberation Army, wani bangare na kungiyar National Liberation Front da ta yi yaki da mulkin mallakar Faransa lokacin yakin nemar wa Aljeriya ‘yancin gashin kai tsakanin shekarar 1954 zuwa 1962.

Kungiyar ta GFP ta kiyasta cewa kasafin da kasar ke ware wa bangaren tsaronta duk shekara ya kai Dala biliyan 25.

Tana kuma da jiragen yaki 102 da sojoji dubu dari uku da ashirin da biyar.

Nijeriya

Nijeriya ce ta uku a Afirka, kuma ta 31 a duniya cikin kasashe 145 inda ta samu maki 0.5771.

Nijeriya tana bayar da gudummawa sosai wajen samar da tsaro a yammacin Afirka saboda kasafin kudin da take ware wa tsaro da kuma ayyukan sabunta makaman yaki.

A cikin gida kuma, dakarun kasar na bayar da gudummawa wajen murkushe ayyukan ta’addanci musamman a yankin arewa maso gabas sannan kuma ta kasance daya daga cikin na gaba-gaba a Afirka da ke kokarin wanzar da zaman lafiya a duk lokacin da aka samu barkewar hatsaniya a wata kasa ta nahiyar.

A kasafin kudin da gwamnatin kasar ta ware wa bangaren tsaron ya kai naira tiriliyan 4.91, fiye da adadin da aka ware wa bangaren a kasafin da ya gabata.

A jadawalin GFP, Nijeriya tana ware sama da dala biliyan uku a jumulla wajen tafiyar da al’amuran tsaron kasar duk shekara.

Tana kuma da jirage yaki 14 sannan yawan sojojinta sun kai 230,000.

Afirka ta Kudu

Afirka ta Kudu ce kasar da ke biyewa Nijeriya inda ta zo ta hudu a Afirka kuma ta 40 a duniya.

Afirka ta Kudu ta yi fice wajen amfani da makamai na zamani da kwararrun sojoji saboda albarkatun kasar da take da su.

Kasa ce da ta fifita tsaronta sannan kuma tana shiga ayyukan wanzar da zaman lafiya a kasashen da aka samu tarzoma.

GFP ta bayyana cewa kasar tana ware dala biliyan 2,266,800,000 a matsayin kudin ta take kashewa a bangaren tsaronta.

Sannan kuma tana da yawan sojojin da suka kai 71, 235 hadi da jiragen yaki biyu.

Habasha

Habasha ta kasance ta biyar a Afirka kuma ta 52 a duniya a karfin soji

Kungiyar ta GFP ta bayyana cewa Habasha ta ware sama da dala biliyan biyu don tafiyar da harkokin tsaron kasar.

A cewar jadawalin, kasar tana da yawan jiragen yaki da suka kai 25 sannan yawan sojojinta sun kai dubu dari da sittin da biyu.

Afirka
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
Sojoji

Rundunar Tsaro Ta Kashe ‘Yan Bindiga 7, Ta Kwato Shanu 109 Da Aka Sace A Katsina

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.