ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasashen Afirka Biyar Da Suka Fi Karfin Soji

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
Afirka

Kungiyar nan ta kasa da kasa, ta Global Firepower, mai fitar da jadawalin mizanin karfin sojojin kasashen duniya, ta fitar da rahoton da ke cewa a shekara ta 2025 Nijeriya ta kasance ta 39 a karfin soji daga cikin kasashe 145 na duniya.

Shekaru uku jere karfin sojojin kasar na raguwa kamar yadda rahoton kungiyar ya nuna.

  • Ayyukan Jami’an Ilimi Da Muhimmancinsu (3)
  • Za Mu Farfaɗo Da Masana’antun Dinki 44 Da Aka Yi Watsi Da Su – Gwamnatin Kano

A duniya, Amurka ce ta farko a jadawalin inda ta shafe shekaru 18 jere tana kan matsayin.

ADVERTISEMENT

Sauran kasashen da suke baza karfin sojinsu sun hada da Rasha, da China, da Indiya, da kuma Koriya ta Kudu wadda ta kasance kasa ta biyar a duniya da take da karfin soji.

Mun yi nazarin jadawalin da kungiyar ta fitar ga kuma jerin kasashe biyar da suka fi karfin soji a nahiyar Afirka.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Masar

Masar ce kasa ta farko a nahiyar Afirka kuma ta 19 cikin kasashe 145 na duniya da kungiyar ta yi nazarin karfin sojinsu a 2024.

Kungiyar ta GFP ta bayyana cewa Masar tana bajekolin kokarin da take na zamanantar da tsarin tsaronta inda take da dubban motocin sulke da sauran makaman yaki.

Masar ta rike wannan matsayi ne saboda yadda take iya kera manyan makamai na fasaha, da yawan ma’aikatanta, da karfin sojin ruwanta, da na jiragen sama na musamman, da kuma kasafin tsaro mai yawa.

Shugaba Abdel Fattah El-Sisi ya bayar da gudummawa wajen samar da gagarumin ci gaba a fannin karfin soji da sabunta makaman kasar. Kasar ta kulla alaka mai karfi da kasashen duniya wajen habaka dakarun kasar.

yawan sojojin Masar sun kai dubu dari hudu da arba’in yayin da take da jiragen yaki 238.

Masar na kashe kusan dala biliyan shida duk shekara a harkokinta na tsaro, kamar yadda nazarin GFP ya bayyana.

Aljeriya

Aljeriya ce ta biyu bayan Masar wajen karfin soji a nahiyar Afirka inda kuma a jerin kasashen duniya ta kasance ta 25.

Kamar kowace kasa, Aljeriya tana da sojoji na kasa na ruwa da kuma na sama kari da dakarun tsaron sararin samaniya wadda ta maye gurbin sojin National Liberation Army, wani bangare na kungiyar National Liberation Front da ta yi yaki da mulkin mallakar Faransa lokacin yakin nemar wa Aljeriya ‘yancin gashin kai tsakanin shekarar 1954 zuwa 1962.

Kungiyar ta GFP ta kiyasta cewa kasafin da kasar ke ware wa bangaren tsaronta duk shekara ya kai Dala biliyan 25.

Tana kuma da jiragen yaki 102 da sojoji dubu dari uku da ashirin da biyar.

Nijeriya

Nijeriya ce ta uku a Afirka, kuma ta 31 a duniya cikin kasashe 145 inda ta samu maki 0.5771.

Nijeriya tana bayar da gudummawa sosai wajen samar da tsaro a yammacin Afirka saboda kasafin kudin da take ware wa tsaro da kuma ayyukan sabunta makaman yaki.

A cikin gida kuma, dakarun kasar na bayar da gudummawa wajen murkushe ayyukan ta’addanci musamman a yankin arewa maso gabas sannan kuma ta kasance daya daga cikin na gaba-gaba a Afirka da ke kokarin wanzar da zaman lafiya a duk lokacin da aka samu barkewar hatsaniya a wata kasa ta nahiyar.

A kasafin kudin da gwamnatin kasar ta ware wa bangaren tsaron ya kai naira tiriliyan 4.91, fiye da adadin da aka ware wa bangaren a kasafin da ya gabata.

A jadawalin GFP, Nijeriya tana ware sama da dala biliyan uku a jumulla wajen tafiyar da al’amuran tsaron kasar duk shekara.

Tana kuma da jirage yaki 14 sannan yawan sojojinta sun kai 230,000.

Afirka ta Kudu

Afirka ta Kudu ce kasar da ke biyewa Nijeriya inda ta zo ta hudu a Afirka kuma ta 40 a duniya.

Afirka ta Kudu ta yi fice wajen amfani da makamai na zamani da kwararrun sojoji saboda albarkatun kasar da take da su.

Kasa ce da ta fifita tsaronta sannan kuma tana shiga ayyukan wanzar da zaman lafiya a kasashen da aka samu tarzoma.

GFP ta bayyana cewa kasar tana ware dala biliyan 2,266,800,000 a matsayin kudin ta take kashewa a bangaren tsaronta.

Sannan kuma tana da yawan sojojin da suka kai 71, 235 hadi da jiragen yaki biyu.

Habasha

Habasha ta kasance ta biyar a Afirka kuma ta 52 a duniya a karfin soji

Kungiyar ta GFP ta bayyana cewa Habasha ta ware sama da dala biliyan biyu don tafiyar da harkokin tsaron kasar.

A cewar jadawalin, kasar tana da yawan jiragen yaki da suka kai 25 sannan yawan sojojinta sun kai dubu dari da sittin da biyu.

Afirka
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Sojoji

Rundunar Tsaro Ta Kashe ‘Yan Bindiga 7, Ta Kwato Shanu 109 Da Aka Sace A Katsina

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.