• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasashen Duniya Na Bukatar Kasar Sin Fiye Da Yadda Take Bukatarsu

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasashen Duniya Na Bukatar Kasar Sin Fiye Da Yadda Take Bukatarsu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tun daga karshen makon da ya gabata, ministan harkokin kudin kasar Faransa Bruno Le Maire, ya fara ziyara a kasar Sin, a wani yunkuri na karfafa hadin gwiwa da tattaunawa batutuwan cinikayya da tattalin arziki da kasar Sin. Wannan ziyara dai manuniya ce cewa, Faransa ta san abun da ya dace da ci gabanta da ma na duniya, haka kuma ba ta biyewa ra’ayin sauran kasashen yamma dake gani ko daukar kasar Sin a matsayin barazana, tare da kiraye-kirayen raba gari da ita ba.

A baya-bayan nan, an ga yadda jami’an Amurka, wadda ita ce ke yada jita-jitar “barazanar kasar Sin” da batun “raba gari da kasar Sin”, suka yi ta kai-komo a kasar Sin, shin idan da gaske suna son raba gari da kasar Sin, me ke kawo su? Sanin kowa ne suna zuwa ne da zummar kyautata alakar dake tsakaninsu da ita, musamman ganin yadda Amurkar ke fama da matsalar tattalin arziki. Kamar yadda sakatariyar baitulmalin Amurkar Janet Yellen ta bayyana, raba gari tsakanin tattalin arzikin Sin da Amurka, ba zai taba yiwu ba. A ganina, wani abu ne kawai da Amurka ke furtawa domin yaudarar duniya saboda wasu muradu nata, amma zancen ba haka yake ba a hakikanin gaskiya.

  • Za A Kaddamar Da Tashar Wutar Lantarki Da Sin Ta Fadada A Zimbabwe

Tabbas, dogaro da kai da neman ci gaba bisa yanayin kasa, abu ne da Sin ke kira da bada kwarin gwiwar aiwatarwa ga kasashen duniya, domin ta kasance abar misali a wannan bangare. Amma kiraye-kirayen raba gari da Sin ko mayar da ita saniyar ware, abu ne da ba zai amfani kasashen ba har ma da duniya baki daya. Babu wata kasa da za ta bugi kirji ta ce za ta dogara da kanta kadai, ba tare da hada hannu da sauran kasashe ba.

Kuma zuwa yanzu, ya kamata wadancan kasashe masu yada jita-jita su fahimci cewa, suna matukar bukatar kasar Sin fiye da yadda take bukatarsu, kasancewar kasuwarta mai girma, da tubalin tattalin arziki mai kwari da fasahohin zamani da ta mallaka da dimbin kyawawan manufofi da a kullum take samarwa domin jan hankalin ’yan kasuwa da ma kyautata musu yanayin kasuwanci a kasar.

Abun da suka kasa fahimta shi ne, janyewa daga kasar Sin wani yunkuri ne na durkusar da kamfanoninsu da ’yan kasuwa. Kowa ya shaida yadda aka samu tsaikon samar da kayayyaki da tabarbarewar tattalin arziki har ma da hauhawar farashin kayayyaki a lokacin da annobar COVID-19 ta afkawa kasar Sin, lamarin da ya nuna cewa, ba shakka kasashen duniya na bukatar kasar Sin, fiye da yadda take bukatarsu.

Labarai Masu Nasaba

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Har kullum kasar Sin na ci gaba da fadada bude kofarta da maraba da kamfanoni da ’yan kasuwar kasashen waje, domin samun moriyar bai daya da hada gwiwa domin gina al’umma mai makoma ta bai daya. Wadanda kuma suke ganin nisanta kansu da kasar Sin shi ne mafita a gare su, su yi kuka da kansu idan lamura suka kara tabarbare musu. (Fa’iza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Nuna Bambanci A Fannin Ba Da Ilmi Na Lahanta Makomar Amurka

Next Post

Me Takardar Bayani Ta Japan Ke Nufi?

Related

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

4 hours ago
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka
Daga Birnin Sin

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

5 hours ago
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya
Daga Birnin Sin

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

6 hours ago
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14
Daga Birnin Sin

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

7 hours ago
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

8 hours ago
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar
Daga Birnin Sin

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

9 hours ago
Next Post
Me Takardar Bayani Ta Japan Ke Nufi?

Me Takardar Bayani Ta Japan Ke Nufi?

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.