• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasashen Duniya Na Bukatar Kasar Sin Fiye Da Yadda Take Bukatarsu

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasashen Duniya Na Bukatar Kasar Sin Fiye Da Yadda Take Bukatarsu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tun daga karshen makon da ya gabata, ministan harkokin kudin kasar Faransa Bruno Le Maire, ya fara ziyara a kasar Sin, a wani yunkuri na karfafa hadin gwiwa da tattaunawa batutuwan cinikayya da tattalin arziki da kasar Sin. Wannan ziyara dai manuniya ce cewa, Faransa ta san abun da ya dace da ci gabanta da ma na duniya, haka kuma ba ta biyewa ra’ayin sauran kasashen yamma dake gani ko daukar kasar Sin a matsayin barazana, tare da kiraye-kirayen raba gari da ita ba.

A baya-bayan nan, an ga yadda jami’an Amurka, wadda ita ce ke yada jita-jitar “barazanar kasar Sin” da batun “raba gari da kasar Sin”, suka yi ta kai-komo a kasar Sin, shin idan da gaske suna son raba gari da kasar Sin, me ke kawo su? Sanin kowa ne suna zuwa ne da zummar kyautata alakar dake tsakaninsu da ita, musamman ganin yadda Amurkar ke fama da matsalar tattalin arziki. Kamar yadda sakatariyar baitulmalin Amurkar Janet Yellen ta bayyana, raba gari tsakanin tattalin arzikin Sin da Amurka, ba zai taba yiwu ba. A ganina, wani abu ne kawai da Amurka ke furtawa domin yaudarar duniya saboda wasu muradu nata, amma zancen ba haka yake ba a hakikanin gaskiya.

  • Za A Kaddamar Da Tashar Wutar Lantarki Da Sin Ta Fadada A Zimbabwe

Tabbas, dogaro da kai da neman ci gaba bisa yanayin kasa, abu ne da Sin ke kira da bada kwarin gwiwar aiwatarwa ga kasashen duniya, domin ta kasance abar misali a wannan bangare. Amma kiraye-kirayen raba gari da Sin ko mayar da ita saniyar ware, abu ne da ba zai amfani kasashen ba har ma da duniya baki daya. Babu wata kasa da za ta bugi kirji ta ce za ta dogara da kanta kadai, ba tare da hada hannu da sauran kasashe ba.

Kuma zuwa yanzu, ya kamata wadancan kasashe masu yada jita-jita su fahimci cewa, suna matukar bukatar kasar Sin fiye da yadda take bukatarsu, kasancewar kasuwarta mai girma, da tubalin tattalin arziki mai kwari da fasahohin zamani da ta mallaka da dimbin kyawawan manufofi da a kullum take samarwa domin jan hankalin ’yan kasuwa da ma kyautata musu yanayin kasuwanci a kasar.

Abun da suka kasa fahimta shi ne, janyewa daga kasar Sin wani yunkuri ne na durkusar da kamfanoninsu da ’yan kasuwa. Kowa ya shaida yadda aka samu tsaikon samar da kayayyaki da tabarbarewar tattalin arziki har ma da hauhawar farashin kayayyaki a lokacin da annobar COVID-19 ta afkawa kasar Sin, lamarin da ya nuna cewa, ba shakka kasashen duniya na bukatar kasar Sin, fiye da yadda take bukatarsu.

Labarai Masu Nasaba

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Har kullum kasar Sin na ci gaba da fadada bude kofarta da maraba da kamfanoni da ’yan kasuwar kasashen waje, domin samun moriyar bai daya da hada gwiwa domin gina al’umma mai makoma ta bai daya. Wadanda kuma suke ganin nisanta kansu da kasar Sin shi ne mafita a gare su, su yi kuka da kansu idan lamura suka kara tabarbare musu. (Fa’iza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Nuna Bambanci A Fannin Ba Da Ilmi Na Lahanta Makomar Amurka

Next Post

Me Takardar Bayani Ta Japan Ke Nufi?

Related

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

12 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

13 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

15 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

18 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

19 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

20 hours ago
Next Post
Me Takardar Bayani Ta Japan Ke Nufi?

Me Takardar Bayani Ta Japan Ke Nufi?

LABARAI MASU NASABA

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.