ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasashen Duniya Na Bukatar Kasar Sin Fiye Da Yadda Take Bukatarsu

by CMG Hausa
3 years ago
Kasashen duniya

Tun daga karshen makon da ya gabata, ministan harkokin kudin kasar Faransa Bruno Le Maire, ya fara ziyara a kasar Sin, a wani yunkuri na karfafa hadin gwiwa da tattaunawa batutuwan cinikayya da tattalin arziki da kasar Sin. Wannan ziyara dai manuniya ce cewa, Faransa ta san abun da ya dace da ci gabanta da ma na duniya, haka kuma ba ta biyewa ra’ayin sauran kasashen yamma dake gani ko daukar kasar Sin a matsayin barazana, tare da kiraye-kirayen raba gari da ita ba.

A baya-bayan nan, an ga yadda jami’an Amurka, wadda ita ce ke yada jita-jitar “barazanar kasar Sin” da batun “raba gari da kasar Sin”, suka yi ta kai-komo a kasar Sin, shin idan da gaske suna son raba gari da kasar Sin, me ke kawo su? Sanin kowa ne suna zuwa ne da zummar kyautata alakar dake tsakaninsu da ita, musamman ganin yadda Amurkar ke fama da matsalar tattalin arziki. Kamar yadda sakatariyar baitulmalin Amurkar Janet Yellen ta bayyana, raba gari tsakanin tattalin arzikin Sin da Amurka, ba zai taba yiwu ba. A ganina, wani abu ne kawai da Amurka ke furtawa domin yaudarar duniya saboda wasu muradu nata, amma zancen ba haka yake ba a hakikanin gaskiya.

  • Za A Kaddamar Da Tashar Wutar Lantarki Da Sin Ta Fadada A Zimbabwe

Tabbas, dogaro da kai da neman ci gaba bisa yanayin kasa, abu ne da Sin ke kira da bada kwarin gwiwar aiwatarwa ga kasashen duniya, domin ta kasance abar misali a wannan bangare. Amma kiraye-kirayen raba gari da Sin ko mayar da ita saniyar ware, abu ne da ba zai amfani kasashen ba har ma da duniya baki daya. Babu wata kasa da za ta bugi kirji ta ce za ta dogara da kanta kadai, ba tare da hada hannu da sauran kasashe ba.

ADVERTISEMENT

Kuma zuwa yanzu, ya kamata wadancan kasashe masu yada jita-jita su fahimci cewa, suna matukar bukatar kasar Sin fiye da yadda take bukatarsu, kasancewar kasuwarta mai girma, da tubalin tattalin arziki mai kwari da fasahohin zamani da ta mallaka da dimbin kyawawan manufofi da a kullum take samarwa domin jan hankalin ’yan kasuwa da ma kyautata musu yanayin kasuwanci a kasar.

Abun da suka kasa fahimta shi ne, janyewa daga kasar Sin wani yunkuri ne na durkusar da kamfanoninsu da ’yan kasuwa. Kowa ya shaida yadda aka samu tsaikon samar da kayayyaki da tabarbarewar tattalin arziki har ma da hauhawar farashin kayayyaki a lokacin da annobar COVID-19 ta afkawa kasar Sin, lamarin da ya nuna cewa, ba shakka kasashen duniya na bukatar kasar Sin, fiye da yadda take bukatarsu.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Har kullum kasar Sin na ci gaba da fadada bude kofarta da maraba da kamfanoni da ’yan kasuwar kasashen waje, domin samun moriyar bai daya da hada gwiwa domin gina al’umma mai makoma ta bai daya. Wadanda kuma suke ganin nisanta kansu da kasar Sin shi ne mafita a gare su, su yi kuka da kansu idan lamura suka kara tabarbare musu. (Fa’iza Mustapha)

Kasashen duniya
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Daga Birnin Sin

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Daga Birnin Sin

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Next Post
Me Takardar Bayani Ta Japan Ke Nufi?

Me Takardar Bayani Ta Japan Ke Nufi?

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.