• English
  • Business News
Saturday, October 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasashen Turai Sun Fusata Da Matakin Amurka

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasashen Turai Sun Fusata Da Matakin Amurka

An employee works in the X3 X4 assembly hall at the BMW Spartanburg plant in Greer, S.C. Wednesday, Oct. 19, 2022. BMW's sprawling factory near Spartanburg, will get a $1 billion investment, and the German automaker will spend another $700 million to build a battery plant nearby as it begins the transition to electric vehicles in the U.S., the company announced. (AP Photo/Sean Rayford)

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A daren ranar 21 ga wata, a fadar shugaban kasar Faransa ta “Elysee”, shugaba Emmanuel Macron na kasar ya shirya wata liyafa, inda ‘yan kasuwar kasashen Turai da dama suka halarta, ciki hadda manyan jami’an kamfanonin Ericsson, da Volvo, da Unilever. Mr. Macron ya shirya liyafar ba domin murnar wani abu ba, sai don fatan wadannan kamfanoni ba za su bar kasashen Turai su je kasar Amurka ba.

Yanzu farashin makamashi ya karu matuka a kasashen Turai, wanda hakan ya sa kudin sarrafa hajoji ya karu sosai, lamarin da ya sanya kamfanonin kasashen Turai fuskantar matsananciyar matsala.

  • An Yi Ganawa Tsakanin Ministocin Tsaron Kasashen Sin Da Amurka 

Kamar yadda wani babban jami’in kawancen masana’antun sarrafa karfe na kasar Faransa ya fada, kila matsakaicin farashin iskar gas da wutar lantarki zai karu da ninki 4.

Amma a kasar Amurka, farashin makamashi bai sauya da yawa ba, kana kuma, shirin dokar yaki da hauhawar farashin kaya da gwamnatin kasar Amurka ta zartas, ya samar wa kamfanonin da ke Amurka kudin alawas da yawa, shi ya sa kamfanonin kasashen Turai ba abun da za su yi, sai dai janyewa daga nahiyar Turai, su koma kasar Amurka.

A watan Agustan bana, gwamnatin kasar Amurka ta gabatar da shirin dokar yaki da hauhawar farashin kaya, a kokarin samar wa kamfanonin kera motoci masu amfani da wutar lantarki a Amurka kudin alawas, amma shirin dokar bai shafi kamfanonin kasashen kungiyar EU, Japan, da Koriya ta Kudu ba. Irin wannan shirin doka maras adalci, ta sanya kamfanoni masu ruwa da tsaki juya hankalinsu daga masana’antun kera motoci masu amfani da wutar lantarki na Turai, zuwa kasar Amurka.

Labarai Masu Nasaba

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasashen Turai sun yi matukar fusata da hakan. Har ma shugaban Faransa Emmanuel Macron ya zargi Amurka da laifin ba da kariya kan cinikayya.

Kana ministan tattalin arzikin kasar Jamus Robert Habeck ya ce, Amurka tana cin zalin Turai yanzu. Har ila yau jami’an EU sun zargi Amurka da laifin saba wa ka’idojin kungiyar cinikayyar duniya.

Kaza lika a ranar 22 ga wata, kasashen Faransa da Jamus, sun ba da sanarwar hadin gwiwa, inda suka nuna cewa, za a kiyaye masana’antun Turai da kauracewa shirin dokar Amurka ta yaki da hauhawar farashin kaya cikin hadin gwiwa. (Tasallah Yuan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Matsalar Karancin Man Fetur Na Ci Gaba Da Ta’azzara A Legas

Next Post

Zan Magance Rashin Aikin Yin Matasa Da Dala Biliyan 10 – Atiku

Related

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

36 minutes ago
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

2 hours ago
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci
Daga Birnin Sin

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

3 hours ago
Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu
Daga Birnin Sin

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

4 hours ago
Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo
Daga Birnin Sin

Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

23 hours ago
Xi Ya Taya Grand Duke Guillaume Na Luxembourg Murnar Hawa Karagar Mulki
Daga Birnin Sin

Xi Ya Taya Grand Duke Guillaume Na Luxembourg Murnar Hawa Karagar Mulki

24 hours ago
Next Post
Zan Magance Rashin Aikin Yin Matasa Da Dala Biliyan 10 – Atiku

Zan Magance Rashin Aikin Yin Matasa Da Dala Biliyan 10 - Atiku

LABARAI MASU NASABA

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

October 4, 2025
An Nada Adamar Kamaye Sarautar Jakadiya A Kasar Ghana

An Nada Adamar Kamaye Sarautar Jakadiya A Kasar Ghana

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.