• English
  • Business News
Saturday, August 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

by Abubakar Sulaiman
4 hours ago
in Labarai
0
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A lokacin da ƴaƴan masu hannu da shuni ke zubar da abinci, suna karin kumallo, suna rayuwa mai kyau, dubban yara ƙanana a Nijeriya, musamman a yankin Arewa, kuwa su na bushewa a idanunmu saboda yunwa, an manta da su.

A halin yanzu, Nijeriya na samar da tsarar yara masu fama da tamowa wadanda ba su da damar aiki nan gaba saboda rashin sinadirai da ake buƙata domin samun ci gaban ƙwaƙwalwa yadda ya kamata.

Abin takaici, tare da wannan yanayin mai cike da damuwa shi ne, rabin mata masu juna biyu a Nijeriya (kashi 50 cikin 100) suna fama da rashin abinci mai gina jiki, galibi suna fama da cutar rashin jini da matsalolin lafiya.

  • Gwamna Nasir Ya Ƙaddamar da Aikin Titin Koko–Zuru Kan Naira Biliyan 64
  • Shekara 2 Ta Gwamnatin Tinubu: Gwamnonin Arewa Sun ƙaryata Zargin ACF Na Watsi ɗa Yankin

A matsayin wani muhimmin al’amari na kiwon lafiyar jama’a, ƙasar na ci gaba da fama da matsanancin rashin abinci mai gina jiki a tsakanin yara da mata masu juna biyu, wanda hakan ke haifar da babbar barazana ga jin daɗinsu da kuma makomar ƙasar.

Wakilinmu, wanda ya yi tafiye-tafiyen yaƙin neman lafiya ya zo mana da wannan labari mai ban mamaki:

Labarai Masu Nasaba

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

A’isha ƴar shekara uku da suke zaune a ƙarƙashin inuwar bishiyar ɗogoyaro a wani ƙauye mai nisa a yankin Arewa maso Gabas (sansanin gudun hijira).

Babu takalmi a ƙafarta, ta yi shiru, saboda radaɗi da take ji. ƙafafuwanta sirara sun yi rauni, cikinta ya dan kumbura saboda yunwa, idanunta sun fito tana cikin halin da bai kamata a ce mai shekaru irinta na ciki ba.

Aisha Abdullahi ba ta iya yin kuka ba, domin babu ƙarfin halin yin hakan Mahaifiyarta, Maryam Abdullahi, tana girgiza ta a hankali a cinyarta, ta hada man gero mai ruwa da dakakken ganye a cikin wani ƙaramar roba. Abincin da suke ci a cikin kwana biyu.

Ta shaida wa LEAɗERSHIP Weekend cewa, “wani lokaci ta ci abinci, wani lokacin kuma sai dai ta yi ta kuka, a gaskiya babu isasshen abinci, babu kuɗi, babu taimako.”

An ba da rahoton cewa fiye da kashi 40 cikin 100 na yara ƴan ƙasa da shekaru biyar a cikin al’ummomin da ke fama da talauci suna takure, girma da ci gaban ƙwaƙwalwarsu na lalacewa a koda yaushe saboda rashin abinci mai gina jiki. Wannan yana nufin miliyoyin yaran da aka hana su damarsu, na fama da ƙanƙancewar a jiki, a hankali, kuma su ne mafiya saurin kamuwa da cuta da kusanci da mutuwa.

A cewar masana, kalmar “rashin abinci” ba lallai ba ne yana nufin cewa yara ba sa cin abinci

Yana nufin ba sa cin abinci daidai gwargwado da ake buƙata don ci gaban da ya dace.

LEAɗERSHIP Weekend ta ruwaito cewa, shekarar 2023 zuwa 2024, Hukumar Kiwon Lafiya Ta ƙasa (NɗHS) ta bayyana cewa huɗu daga cikin yara goma ƴan Nijeriya ƴan ƙasa da shekara biyar (kashi 40) na fama da matsalar tsangwama, wanda ya ƙaru daga kashi 37 cikin 100 a shekarar 2018.

Bugu da ƙari, kashi 8 cikin 100 na yara a yanzu suna fama da rashin kulawa, kusan daya cikin kowane goma, idan aka kwatanta da kashi 7 cikin 100 a shekarar 2018.

A cewar binciken daya daga cikin kashi 22 cikin 100 na yara ƴan ƙasa da shekara biyar ba su da ƙiba tun a shekarar 2018, adadin da ya ƙaru zuwa kashi 25 cikin 100 a bayanan 2023/2024.

 

ƙididdiga mai ban tsoro

A duk faɗin ƙasar nan, yara, mata masu juna biyu, har ma da manya na fama da matsalar rashin abinci mai gina jiki, kuma babu wani yanki da ya tsira.

A cewar wani rahoto daga Shirin Buƙatun Jin ƙai da Bayar da Agajin Gaggawa da OCHA ta shirya, kimanin yara ƴan ƙasa da shekaru biyar miliyan 2.55 na iya fuskantar matsalar rashin abinci mai gina jiki a bana.

daga cikin wadannan, ana sa ran miliyan daya za su fuskanci matsanancin rashin abinci mai gina jiki. Bugu da ƙari, kimanin mata da ƴammata masu juna biyu da masu shayarwa (PBWG) kusan 309,000 ne kuma ake hasashen za su fuskanci matsalar rashin abinci mai gina jiki.

Masu ruwa da tsakin sun bayyana damuwarsu kan yadda ƙarancin abinci da tsadar kayan masarufi ke ƙara ta’azzara matsalar rashin abinci mai gina jiki a Nijeriya.

dangane da bayanan 2025 daga Hukumar ƙididdiga ta ƙasa (NBS), hauhawar farashin abinci a watan Mayu ya tsaya da kashi 21.4 bisa dari a duk shekara, ya ragu da kashi 19.52 cikin dari daga kashi 40.66 da aka samu a watan Mayun 2024.

Yayin da raguwar hauhawar farashin kayan abinci ta shekara ta bayyana, al’amura na rashin araha da wadatarsu sun zama manyan cikas ga gidaje da yawa.

A ƙoƙarinta na shawo kan matsalar ƙarancin abinci mai gina jiki, gwamnatin tarayya ta ƙaddamar da shirin Nutrition-774 Initiatiɓe, da nufin farfaɗo da ayyukan cikin gida don inganta samar da abinci, lafiya, da abinci mai gina jiki a faɗin Nijeriya. An tabbatar da tsarin sadarwa na ƙasa akan ingantaccen abinci mai gina jiki don tallafa wa manufofin da suka dace da ƙoƙarin majalisu.

A baya-bayan nan, kwamitin kula abinci na majalisar ya kira taron ƙasa kan abinci da samar da abincin kansa. Taron ya tattaro masu ruwa da tsaki da dama, da suka hada da ƙwararru daga muhimman sassa, ma’aikatu, sassa, da hukumomi da rundunonin soji, da hukumomin tsaro, da sarakunan gargajiya, da ƴan majalisar wakilai, da ƴan majalisar dokokin jiha, da kuma abokan ci gaba.

da yake bayyana buɗe taron, Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima, ya yi kira da a samar da tsarin yaƙi da matsalar ƙarancin abinci mai gina jiki a ɓangarori da dama da kuma ƙarfafa abinci da tsaron ƙasa a faɗin ƙasar.

da yake jawabi a madadin mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima, mataimakin shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa (Ofishin mataimakin shugaban kasa), Sanata Ibrahim Hadejia ya bayyana cewa sabon shirin N-774 da aka ƙaddamar an yi shi ne musamman domin samar da tasiri kai tsaye a sassan ƙasar nan da ba a yi wa hidima ba kuma ba a mantawa da su ba.

“Mun shaida yadda aka kafa ƙungiyar ƴan majalisu ta ƙasa kan samar da abinci, tare da kwafin takardar zaman wannan kwamiti a dukkanin majalisun dokokin jihohi 36. Wannan ya nuna wani gagarumin ci gaba da ba a taɓa ganin irinsa ba a cikin ayyukanmu na majalisar, amma dole ne mu gane cewa dalilin da ya sa muka taru a yau ba wai don murna ba ne,” in ji shi.

A jawabinsa na maraba, shugaban kwamitin kula da abinci na majalisar, Hon. Chike Okafor, ya bayyana cewa majalisar na yin tarukan gina dabaru don ƙara fahimtar asalin lamarin da yanayin ƙalubalen abinci mai gina jiki da abinci da ke fuskantar Nijeriya.

Ya bayyana cewa, “Wannan zai ba mu damar ci gaba da sa ido kan duk abubuwan da suka shafi abinci da abokan aiki, amma ba’a iyakance ga tsarin Majalisar ɗinkin ɗuniya, Bankin ɗuniya, ƙungiyoyi masu zaman kansu na ƙasa da ƙasa da na ƙasa ba, kuma, haka abin yake a gwamnati matakin tarayya, jihohi, da ƙananan hukumomi.

Okafor ya ƙara jaddada cewa aikin farko na gwamnati shi ne tabbatar da tsaro, musamman a yankunan da ke da matuƙar muhimmanci wajen samar da abinci. Ya ƙara da cewa, “ɗole ne mu tabbatar da wuraren da suka hada da Arewa maso Gabas, Arewa maso Yamma, Arewa ta Tsakiya, da ma Kudu maso Gabas, wadanda duk suna da matuƙar muhimmanci ga samar da abinci a Nijeriya.”

da yake wakiltar gidauniyar Gates, Ekenem Isichie, ya yi kira ga Majalisar ɗokoki ta ƙasa da ta himmatu wajen yin amfani da aikin sa ido na doka don tabbatar da cewa cibiyoyin kula da lafiya a matakin farko a faɗin ƙasar nan suna isar da sahihan bayanai da ingantattun ayyukan kiwon lafiya ga iyaye mata da yara.

Ya kuma jaddada cewa dole ne Nijeriya ta jagoranci nahiyar Afirka wajen rage mace-macen jarirai da mata masu juna biyu, da kawo ƙarshen rashin abinci mai gina jiki, da inganta samar da abinci.

A nasa jawabin, daraktan ƙungiyar Global Alliance for Improɓed Nutrition (GAIN), ɗr. Michael Ojo, ya bayyana sauyin yanayi, rashin tsaro da yunwa, da ƙaruwar al’ummar Nijeriya ya zarce samar da abinci a matsayin manyan matsalolin rashin abinci mai gina jiki.

Ya bayyana cewa, “Muna samar da abinci da yawa, amma adadin mutanenmu na ƙaruwa da sauri fiye da yadda ake noman abinci, wannan yana haifar da matsin lamba ga wadatar abincin da ake samu, abin takaici, a cikin ƴan shekarun nan, ƙarfin samar da kayayyaki ya ragu saboda rashin tsaro da kuma dalilai kamar sauyin yanayi.”

ɗokta Ojo ya jaddada cewa samar da abinci ƙalubale ne, amma samar da abinci mai gina jiki wani abu ne. “Lokacin da muka tattauna matsalar rashin abinci mai gina jiki, dole ne mu yi la’akari da rashin abinci da abinci mai gina jiki.

da gaske muna fuskantar ƙalubale biyu. ɗon haka ne wannan shiri na kwamitin kula da abinci mai gina jiki da samar da abinci na majalisar wakilai ke da matuƙar muhimmanci. Wannan batu ba alhakin gwamnatin tarayya kadai ba ne; yana buƙatar yunƙurin haɗin gwiwa a dukkan matakai uku na gwamnati.”

A cewar dakta Ojo, yayin da gwamnatin tarayya za ta iya tsara manufofi, ainihin tasirin yana faruwa a matakin jihohi da ƙananan hukumomi.

“Akwai matsaloli da yawa da ke buƙatar mafita da yawa, amma haɗin gwiwa yana da mahimmanci don samar da wadannan hanyoyin ingantattu, wasu sun ce manoma ba sa amfani da hanyoyin noma yadda ya kamata, amma yawancin noman mu har yanzu ya dogara da ruwan sama, tare da yawancin gonaki ba sa ban ruwa.

Wannan wani ɓangare ne na ƙalubale, amma kuma dama. Misali, ƙarfafa wa mata, wadanda ke samar da wani kaso mai tsoka na al’ummar noma, ta hanyar samar musu da filayen noma don ƙananan sana’o’i na iya kawo canji,” in ji shi.

A halin da ake ciki kuma, daraktan Cibiyar Samar da Abinci Mai Gina Jiki ta ƙasa da ƙasa, ɗrakta Osita Okonkwo, ya jaddada cewa samar da abinci mai gina jiki ya kasance mai matuƙar muhimmanci ga lafiyar al’umma a Nijeriya.

Ya ƙara da cewa, Nijeriya kamar ƙasashe da dama, na fuskantar ƙalubalen rashin abinci mai gina jiki da ba wai kawai ya shafi lafiya da walwalar al’ummarta ba, har ma da hana ci gaban tattalin arziki, ci gaban al’umma, ci gaban kyawawan halaye, da kuma ci gaban ƙasa baki daya.

A cewar dakta Okonkwo, sanya hannun jari a fannin abinci mai gina jiki, saka hannun jari ne ga walwala da ci gaban al’umma, saboda rashin abinci mai gina jiki ya kasance babban ƙalubalen kiwon lafiyar al’umma a Nijeriya. Ya kuma buƙaci masu ruwa da tsaki da su hada kai wajen gina Nijeriya mai cike da ƙoshin lafiya, da wadata, ƙasar da kowane dan kasa zai samu ci gaba, ya kai ga ga cimma burinsa, da rayuwa cikin walwala da abinci mai gina jiki.

Ya ƙara da cewa “ɗole ne mu ƙarfafa haɗin gwiwa da kuma ware isassun kasafin kuɗi a sassa daban-daban kamar aikin gona, kiwon lafiya, ilimi, da kuma kare zamantakewar al’umma don samar da cikakkiyar hanya ta abinci mai gina jiki,” in ji shi.

Babban mataimaki na musamman ga shugaban ƙasa kan harkokin kiwon lafiyar jama’a da mai kula da harkokin abinci na ofishin mataimakiyar shugaban ƙasa, Uju Rochas Awuka, ta jaddada buƙatar gaggauta inganta harkokin kiwon lafiya, da kiyaye abinci mai gina jiki a kan manufofin siyasa, da ba da damar shiga tsakani a kan lokaci. Ta bayyana ƙwarin gwiwar cewa kowane ƙalubale na samar da mafita.

Uwargida Awuka ta bayyana shirin Nutrition 774 Initiatiɓe da hukumar kula da abinci ta ƙasa (NCN) ta ƙaddamar kwanan nan a matsayin shirin da aka tsara domin hada kan manyan masu ruwa da tsaki, da ƙarfafa haɗin kai a ɓangarori da dama, da inganta kudaɗe da tabbatar da gaskiya, da kuma magance matsalar rashin abinci mai gina jiki a ƙasar nan yadda ya kamata.

da aka tambaye shi yadda za a sauya yanayin rashin abinci mai gina jiki, Hon. Chike Okafor, shugaban kwamitin majalisar kan harkokin abinci ya bayyana cewa:

“Abu ne mai sauƙi ƙwarai. A yi duk abin da zai yiwu don tabbatar da samun abinci da araha. Wadannan biyun, samuwa da araha, suna da mahimmanci.”

“Yaya za mu yi magana game da abinci mai gina jiki yayin da abinci ba zai iya isa ba? Abinci mai gina jiki da samar da abinci su ne ɓangarori biyu na tsabar kuɗin. Ba za mu iya magance daya ba tare da dayan ba,” in ji shi.

LEAɗERSHIP Weekend ta nanata tambayar cewa: Me ya sa rashin abinci mai gina jiki ke ci gaba da kasancewa cikin kashi 40 cikin 100? Wane ne ke da alhakin kasafin kuɗin da ba a kashe ba, da wuraren da ba su da kayan aiki, da kuma iyaye mata da ba a sani ba?

Wani lamarin gaggawa, yara nawa irin Aisha Nijeriya za ta yi asara kafin ta dauki mataki na hakika, ba wai kawai daukar alƙawura ne abin nufi ba, a samar da canji mai ma’ana.

A cikin al’ummar da ke cike da hazaƙa, babu wani yaro da za a yanke masa hukuncin girma da yunwa kuma a ce zai ci gaba. Yanzu ne lokacin yin aikin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: YaraYunwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

Next Post

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

Related

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto
Labarai

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

46 minutes ago
Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto
Labarai

Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

4 hours ago
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 
Da ɗumi-ɗuminsa

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

6 hours ago
Gwamna Fintiri Ya Karrama Kocin Super Falcons, Madugu Da Naira Miliyan 50
Labarai

Gwamna Fintiri Ya Karrama Kocin Super Falcons, Madugu Da Naira Miliyan 50

6 hours ago
Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO
Manyan Labarai

Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO

7 hours ago
An Sake Kashe Wata Ɗalibar Jami’ar Ondo
Labarai

An Sake Kashe Wata Ɗalibar Jami’ar Ondo

9 hours ago
Next Post
Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

LABARAI MASU NASABA

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

August 2, 2025
Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

August 2, 2025
Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

August 2, 2025
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

August 2, 2025
Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

August 2, 2025
Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

August 2, 2025
An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

August 2, 2025
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

August 2, 2025
Gwamna Fintiri Ya Karrama Kocin Super Falcons, Madugu Da Naira Miliyan 50

Gwamna Fintiri Ya Karrama Kocin Super Falcons, Madugu Da Naira Miliyan 50

August 2, 2025
Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO

Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO

August 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.