• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasuwar Shanu: ‘Yan Arewa Sun Koka Da Barazanar Korar Su A Abiya

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Shanu

Shugabannin kungiyar ‘yan kasuwan arewa da ke kasuwar shanu ta Lobbanta Garke a karamar hukumar Umunneochi cikin Jihar Abiya sun bukaci Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu da mai alfarma sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar ll su saka baki game da wa’adin kwanaki 14 da gwamnatin Abiya ta ba su na su fice daga kasuwar.

Mataimakin shugaban ‘yan kungiyar kasuwan shanu ta Lobbanta, Buba Abdullahi Kedemure shi ne ya jagoranci sauran shugabannin zuwa ofishin kungiyar tuntuba ta kasa (NCM) da ke Kaduna, wanda suka ce sun zo mika kokensu ne kan wa’adin korar da gwamnatin Jihar Abiya ta ba su na ficewa daga kasuwar.

  • Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Nijeriya Ta Samu Ci Gaba Mai Inganci?
  • An Horas Da Makiyaya Dabarun Shuka Ciyawar Shanu A Kaduna

Mataimakin shugaban kungiyar ya kara da cewa sun ‘yan kasa nagari masu bin doka wajen gudanar da harkokin kasuwancinsu a tsawon shekaru masu yawa a cikin jihar, amma a yanzu an ba su wa’adin ficewa daga kasuwan kan zargin aika-ta ta’addanci wanda suka musanta.

“Muna rokon shugabanninmu da su saka baki tare da yin kira ga gwamnan domin janye wa’adin na kwanaki 14 da aka ba mu na ficewa daga kasuwan,” in ji shi.

Shugaban kungiyar tuntuba na arewa, Dakta Auwal Abdullahi ya bayyana kudurinsa na daukan mataki a daidai lokacin da ‘yan kasuwar arewa ke fuskantar wulakanci a Abiya ko wani bangare na jihohin gabashin Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

Ya tunatar da gwamnatin Jihar Abiya da sauran gwamnonin kudu maso gabas ce-wa ‘yan kabilar Igbo na gudanar da harkokin kasuwancinsu na biliyoyin naira a jihohin Kaduna da Kano da Katsina da ma sauran jihohin Arewa amma ba sa fus-kantar wata tsangwama.

Auwal ya ce babban aikinsu shi ne kare muradun Arewa da ‘yan Arewa bisa tsarin doka. Don haka ya yi kira ga gwamnan Jihar Abiya da ya janye wa’adin kwanaki 14 da ya bai wa ‘yan Arewa masu gudanar da sana’o’i na halal a kasuwar shanu ta Garke a jihar.

Da yake mayar da martani game da lamarin, mai bai wa gwamnan shawara na musamman kan harkokin tsaro, MacDonald Ubah, wanda ya yi jawabi ga mane-ma labarai a ranar Litinin a Umuahia, ya yi watsi da jita-jita a matsayin karyar zance mara tushe.

Ya zargi masu yada wannan jita-jita da karkatar da umarnin gaskiya da gwamnati ta bayar domin haifar da rudani da bata wa Gwamna Aled Otti suna.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma
Manyan Labarai

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP
Labarai

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu!
Rahotonni

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
Next Post
CMG Ya Rattaba Hannu Tare Da Kawancen LFP Na Faransa Kan Takardar Bayanin Hadin-Gwiwa

CMG Ya Rattaba Hannu Tare Da Kawancen LFP Na Faransa Kan Takardar Bayanin Hadin-Gwiwa

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.