• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kenya Ta Dakatar Da Yi Wa Ma’aikatan Gwamnati Karin Albashi

by Sadiq
1 year ago
in Kasashen Ketare
0
Kenya Ta Dakatar Da Yi Wa Ma’aikatan Gwamnati Karin Albashi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Albashi da Jin Dadin Ma’aikata ta Kenya, ta janye shirinta na kara albashin ‘yan siyasa masu rike da madafun iko daga 1 ga watan Yuli.

Kenya ta dakatar da shirinta na kara albashin ‘yan siyasa masu rike da madafun iko daga 1 ga watan Yuli.

  • NDLEA Ta Bayar Da Shawarar Tilasta Wa Ma’aurata Yin Gwajin Shan Ƙwaya A Kano
  • Tinubu Zai Halarci Zikirin Juma’a A Fadar Aminu Ado Ta Nassarawa

A ranar Laraba ne Hukumar Kula da Albashi da Jindadin Ma’aikata ta bayyana cewa ta “dakatar da shirin kara albashin dukkanin ‘yan siyasa masu rike da madafun iko, kuma za ta yi duba ga shawara kan albashin dukkanin ‘yan siyasa don tabbatar dorewar kashe kudade.”

Shugabar Hukumar Lyn Mengich ta ce an yanke hukuncin dakatar da shirin karin albashin ne bayan tattaunawa da neman shawarwarin jama’a.

Hukumar ta SRC ta fitar da wata sanarwa a hukumance a jaridar Gwamnatin Kenya a watan Agustan 2023 inda ta bayyana shirinta na ƙara albashin ‘yan siyasa masu rike da madafun iko daga 1 ga Yulin 2024.

Labarai Masu Nasaba

An Tsare Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Cin Hanci Da Rashawa

An Kama Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Karkatar Da Dukiyar Gwamnati

‘Mu rayu daidai gwargwadon arzikinmu’

Shugaban Kasar Kenya William Ruto ya umarci Ma’aikatar Kudi ta kasa da ta dakatar da shirin karin albashin.

Shugaba Ruto ya ce wannan mataki zai taimaka wa Kenya ‘Ta rayu daidai gwagwardon arzikinta”.

Kungiyar gwamnoni, wadda ta kunshi dukkan gwamnoni 47 na kasar Kenya, ta yi kira ga Hukumar SRC da ta dakatar da shirin karin albashin ‘yan siyasa masu rike da madafun iko.

Sabon tsarin albashin da aka kawo ya tanadi cewa dan majalisar dokoki zai dinga karbar kudin Kenya 739,600 kwatankwancin dalar Amurka 5,730 a kowanne wata, kari kan ksh 725,500 kwatankwacin dala 5,620 da suke karba a halin yanzu.

Almubazzaranci a gwamnati

Sabon albashin gwamnoni zai kama ksh 990,000 ($7,620), daga 957,000 ($7,420) da suke karba a yanzu.

Ministoci kuma da suke da matsayi iri daya da na gwamnonin za su samu kari kwatankwacin na gwamnonin.

Kenya na da ministoci 22.

Karin albashin zai janyo kenya ta kashe kusan Sulallan kasar biliyan 11 (dala miliyan $85.3) a kowacce shekara, kamar yadda jaridar ƙasa ta Kenya ta rawaito a ranar Laraba.

Matakin janye karin albashin ‘yan siyasar ya zo ne a lokacin da ‘yan kasar ke kira ga gwamnatin Ruto da ta kawo karshen almubazzaranci a cikin gwamnati.

Zanga-angar adawa da karin haraji da aka yi a baya-bayan nan a Kenya ta janyo asarar rayukan mutum 39, kamar yadda Hukumar Kare Hakkokin Dan’adam ta Kenya mallakin gwamnati ta sanar.

Zanga-zangar ta sanya Ruto janye Dokar Kudade ta 2024, wadda ta tanadi kara yawan haraji a kasar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Karin AlbashiKenyaMa'aikatan GwamnatiShugaba William Ruto
ShareTweetSendShare
Previous Post

NDLEA Ta Bayar Da Shawarar Tilasta Wa Ma’aurata Yin Gwajin Shan Ƙwaya A Kano

Next Post

Kotu Ta Dage Shari’ar Matashin Da Ya Kone Masallata A Kano

Related

An Tsare Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Cin Hanci Da Rashawa
Kasashen Ketare

An Tsare Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Cin Hanci Da Rashawa

2 days ago
An Kama Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Karkatar Da Dukiyar Gwamnati
Kasashen Ketare

An Kama Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Karkatar Da Dukiyar Gwamnati

1 week ago
Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka
Kasashen Ketare

Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

2 weeks ago
Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?
Kasashen Ketare

Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

3 weeks ago
Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa
Kasashen Ketare

Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

3 weeks ago
Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza
Kasashen Ketare

Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza

3 weeks ago
Next Post
Kotu Ta Dage Shari’ar Matashin Da Ya Kone Masallata A Kano

Kotu Ta Dage Shari'ar Matashin Da Ya Kone Masallata A Kano

LABARAI MASU NASABA

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

August 22, 2025
Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

August 22, 2025
Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

August 22, 2025
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

August 22, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

August 22, 2025
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

August 21, 2025
Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

August 21, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

August 21, 2025
Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

August 21, 2025
Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

August 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.