ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Dage Shari’ar Matashin Da Ya Kone Masallata A Kano

by Sadiq
2 years ago
Kotu

Kotu ta dage shari’ar Shafiu Abubakar, wanda ake zargin ya yi sanadin mutuwar wasu masallata 19, a garin Gadan da ke karamar hukumar Gezawa a Jihar Kano. 

An dage zaman ne sakamakon rashin kara sunayen mutanen da suka mutu sakamakon lamarin.

  • Kenya Ta Dakatar Da Yi Wa Ma’aikatan Gwamnati Karin Albashi
  • JAMB Ta Bankaɗo Ɗalibai 3000 Da Suka Kammala Karatun Bogi

Leadership ta ruwaito cewar cewa, matashin mai shekaru 38, mazaunin kauyen Gadan da ke karamar hukumar Gezawa, na fuskantar shari’a a babbar kotun Kano da ke Rijiyar Zaki.

ADVERTISEMENT

Tun da farko dai an zargi Abubakar da cinna wa wani masallaci wuta, lamarin da ya yi sanadin mutuwar mutane 14 tare da raunata wasu da dama.

Sai dai mai gabatar da kara, karkashin jagorancin daraktan masu gabatar da kara (DPP) na ma’aikatar shari’a ta Jihar Kano, Barista Salisu Tahir, ya sanar da kotun cewa adadin wadanda suka mutu ya karu daga 14 zuwa 19 saboda haka ya bukaci karin lokaci don sabunta takardar tuhumar.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Tahir ya ce “Muna neman wani kwanan wata don ba mu damar shigar da sabon sauyi don kara adadin wadanda abin ya shafa da kuma gabatar da shaidunmu a gaban kotu,” in ji Tahir.

A cewar masu gabatar da kara, Abubakar ya yi amfani da man fetur wajen cinna wa masallacin da ke kauyen Gadan wuta, a lokacin Sallar Asuba a ranar 15 ga watan Mayu, da misalin karfe 5:15 na asuba.

An garzaya da wadanda lamarin ya rutsa da au Asibitin Kwararru na Murtala Muhammad da ke Kano.

A cewar mai gabatar da karar, laifin ya saba da sashe na 336, 247, da 221 na dokar shari’a ta Jihar Kano.

Lauyar da ke kare wanda ake tuhuma, Barista Asiya Muhammad Imam, ta bukaci masu gabatar da kara da su gabatar da sabbin tuhume-tuhumen.

Daga bisani alkalin kotu, shari’a, Malam Halhalatul Huza’i Zakariyya, ya dage shari’ar zuwa ranar 18 da 19 ga watan Yuli, domin ci gaba da sauraren karar.

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Xi Jinping Ya Gana Da Vladimir Putin

Xi Jinping Ya Gana Da Vladimir Putin

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.