ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Dage Shari’ar Matashin Da Ya Kone Masallata A Kano

by Sadiq
2 years ago
Kotu

Kotu ta dage shari’ar Shafiu Abubakar, wanda ake zargin ya yi sanadin mutuwar wasu masallata 19, a garin Gadan da ke karamar hukumar Gezawa a Jihar Kano. 

An dage zaman ne sakamakon rashin kara sunayen mutanen da suka mutu sakamakon lamarin.

  • Kenya Ta Dakatar Da Yi Wa Ma’aikatan Gwamnati Karin Albashi
  • JAMB Ta Bankaɗo Ɗalibai 3000 Da Suka Kammala Karatun Bogi

Leadership ta ruwaito cewar cewa, matashin mai shekaru 38, mazaunin kauyen Gadan da ke karamar hukumar Gezawa, na fuskantar shari’a a babbar kotun Kano da ke Rijiyar Zaki.

ADVERTISEMENT

Tun da farko dai an zargi Abubakar da cinna wa wani masallaci wuta, lamarin da ya yi sanadin mutuwar mutane 14 tare da raunata wasu da dama.

Sai dai mai gabatar da kara, karkashin jagorancin daraktan masu gabatar da kara (DPP) na ma’aikatar shari’a ta Jihar Kano, Barista Salisu Tahir, ya sanar da kotun cewa adadin wadanda suka mutu ya karu daga 14 zuwa 19 saboda haka ya bukaci karin lokaci don sabunta takardar tuhumar.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Tahir ya ce “Muna neman wani kwanan wata don ba mu damar shigar da sabon sauyi don kara adadin wadanda abin ya shafa da kuma gabatar da shaidunmu a gaban kotu,” in ji Tahir.

A cewar masu gabatar da kara, Abubakar ya yi amfani da man fetur wajen cinna wa masallacin da ke kauyen Gadan wuta, a lokacin Sallar Asuba a ranar 15 ga watan Mayu, da misalin karfe 5:15 na asuba.

An garzaya da wadanda lamarin ya rutsa da au Asibitin Kwararru na Murtala Muhammad da ke Kano.

A cewar mai gabatar da karar, laifin ya saba da sashe na 336, 247, da 221 na dokar shari’a ta Jihar Kano.

Lauyar da ke kare wanda ake tuhuma, Barista Asiya Muhammad Imam, ta bukaci masu gabatar da kara da su gabatar da sabbin tuhume-tuhumen.

Daga bisani alkalin kotu, shari’a, Malam Halhalatul Huza’i Zakariyya, ya dage shari’ar zuwa ranar 18 da 19 ga watan Yuli, domin ci gaba da sauraren karar.

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
Xi Jinping Ya Gana Da Vladimir Putin

Xi Jinping Ya Gana Da Vladimir Putin

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.