ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kenya Ta Dakatar Da Yi Wa Ma’aikatan Gwamnati Karin Albashi

by Sadiq
2 years ago
Kenya

Hukumar Albashi da Jin Dadin Ma’aikata ta Kenya, ta janye shirinta na kara albashin ‘yan siyasa masu rike da madafun iko daga 1 ga watan Yuli.

Kenya ta dakatar da shirinta na kara albashin ‘yan siyasa masu rike da madafun iko daga 1 ga watan Yuli.

  • NDLEA Ta Bayar Da Shawarar Tilasta Wa Ma’aurata Yin Gwajin Shan Ƙwaya A Kano
  • Tinubu Zai Halarci Zikirin Juma’a A Fadar Aminu Ado Ta Nassarawa

A ranar Laraba ne Hukumar Kula da Albashi da Jindadin Ma’aikata ta bayyana cewa ta “dakatar da shirin kara albashin dukkanin ‘yan siyasa masu rike da madafun iko, kuma za ta yi duba ga shawara kan albashin dukkanin ‘yan siyasa don tabbatar dorewar kashe kudade.”

ADVERTISEMENT

Shugabar Hukumar Lyn Mengich ta ce an yanke hukuncin dakatar da shirin karin albashin ne bayan tattaunawa da neman shawarwarin jama’a.

Hukumar ta SRC ta fitar da wata sanarwa a hukumance a jaridar Gwamnatin Kenya a watan Agustan 2023 inda ta bayyana shirinta na ƙara albashin ‘yan siyasa masu rike da madafun iko daga 1 ga Yulin 2024.

LABARAI MASU NASABA

Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya

Amurka Ta Dakatar Da Takunkumin Man Fetur Kan Iran

‘Mu rayu daidai gwargwadon arzikinmu’

Shugaban Kasar Kenya William Ruto ya umarci Ma’aikatar Kudi ta kasa da ta dakatar da shirin karin albashin.

Shugaba Ruto ya ce wannan mataki zai taimaka wa Kenya ‘Ta rayu daidai gwagwardon arzikinta”.

Kungiyar gwamnoni, wadda ta kunshi dukkan gwamnoni 47 na kasar Kenya, ta yi kira ga Hukumar SRC da ta dakatar da shirin karin albashin ‘yan siyasa masu rike da madafun iko.

Sabon tsarin albashin da aka kawo ya tanadi cewa dan majalisar dokoki zai dinga karbar kudin Kenya 739,600 kwatankwancin dalar Amurka 5,730 a kowanne wata, kari kan ksh 725,500 kwatankwacin dala 5,620 da suke karba a halin yanzu.

Almubazzaranci a gwamnati

Sabon albashin gwamnoni zai kama ksh 990,000 ($7,620), daga 957,000 ($7,420) da suke karba a yanzu.

Ministoci kuma da suke da matsayi iri daya da na gwamnonin za su samu kari kwatankwacin na gwamnonin.

Kenya na da ministoci 22.

Karin albashin zai janyo kenya ta kashe kusan Sulallan kasar biliyan 11 (dala miliyan $85.3) a kowacce shekara, kamar yadda jaridar ƙasa ta Kenya ta rawaito a ranar Laraba.

Matakin janye karin albashin ‘yan siyasar ya zo ne a lokacin da ‘yan kasar ke kira ga gwamnatin Ruto da ta kawo karshen almubazzaranci a cikin gwamnati.

Zanga-angar adawa da karin haraji da aka yi a baya-bayan nan a Kenya ta janyo asarar rayukan mutum 39, kamar yadda Hukumar Kare Hakkokin Dan’adam ta Kenya mallakin gwamnati ta sanar.

Zanga-zangar ta sanya Ruto janye Dokar Kudade ta 2024, wadda ta tanadi kara yawan haraji a kasar.

MASU ALAKA

Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya
Kasashen Ketare

Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya

June 23, 2026
Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
Kasashen Ketare

Amurka Ta Dakatar Da Takunkumin Man Fetur Kan Iran

June 22, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran
Kasashen Ketare

Iran Ta Ce Shirinta Na Makamai Masu Linzami Ba Ya Cikin Tattaunawa Da Amurka

June 18, 2026
Next Post
Kotu Ta Dage Shari’ar Matashin Da Ya Kone Masallata A Kano

Kotu Ta Dage Shari'ar Matashin Da Ya Kone Masallata A Kano

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.