• English
  • Business News
Monday, November 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Khalifan Sheikh Ibrahim Inyas Daga Ƙasar Sanigal Ya Goyi Bayan Sunusi Lamido Sunusi II

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
Khalifa

Sheikh Muhammad Mahi Inyass khalifan Sheikh Ibrahim Inyass  ya aike da rubutacciyar wasiƙar taya murna cikin harshen Larabci ga Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II.

A cikin wasiƙar an rubuta saƙon taya murna zuwa ga Mai Martaba Sarkin Kano, kuma Khalifan Sheikh Ibrahim Inyass (Allah ya kare ka).

Ga cikakkiyar fassarar wasiƙar:

  • An Shawarci Sarki Aminu Ado Ya Fice Daga Kano
  • Wata Sabuwa: Kotu Ta Hana Aminu Ado Da Sauran Sarakuna 4 Kiran Kansu Sarakuna A Kano

Amincin Allah da Albarkarsa da kuma jinkansa ya tabbata a gare ka.

Bayan haka,

LABARAI MASU NASABA

Wani Sabon Hari Kan Al’ummar Da Ke Iyaka Da Katsina A Kano Ya Rutsa Da Mata 5

Yadda Sojoji Suka Tarwatsa Haramtattun Matatun Mai 14 A Yankin Neja Delta 

A wannan al’amari na sake dawowarka zuwa ga kujerar magabatanka masu martaba, ina mai farin ciki da samun zarafi, a madadina, da dukkan iyalan Sheikh Ibrahim Inyass (R.T.A) domin bayyana farin ciki da murna da fatan alkairi gare ka Mai Martaba.

Kamar yadda muke taya ka murna cikin wannan al’amari na farin ciki, kuma muna sake jaddada goyon bayan mu gare ka, tare da umartar masoyanka da Muridai da su sake maka mubayi’a domin ci gaba da jagorantarsu bisa tafarkin iyaye da kakanninka, wanda zai shiryar zuwa ga tafarkin cin nasara da ya ginu akan karfafa gwiwa da himma domin samun nasarar cimma burin hadin kai a dukkanin sassan Nigeria.

Khalifa

Bisa ga wannan al’amari, ya kai Mai Martaba Sarki, kuma Khalifan Shehu Ibrahim A Nigeria, ina mai tunatar da kai, Allah ya taimakeka, wani zance daga wata wasiƙa ta shugabana, Shehina, kuma Mahaifina ya rubuta zuwa ga masoyinsa kuma abin soyuwarsa Marigayi Kakanka Alhaji Muhammadu Sanusi Bayero, faɗinsa cewa: Dukkanin jama’ar Africa na buƙatar tabbataccen hadin kai kamar Nigeria, ku haɗu da kowa cikin gaskiya da haɗin kai da hakuri.

Haka nan muna tare da dai zuciya da ruhi cikin wannan babbar manufa, kuma muna fata (Manufar) zai cika dukkanin fatan Musulmi tare da kai, ta hanyar ɗaga tutar Musulunci da ka gada daga magabatanka masu daraja.

Allah mai iko ne akan yin komai.

Da aminci.

Daga Sheikh Muhammad Mahi Ibrahim Inyass, Khalifan Sahibul Faydha, kuma hadimin al’umma.

Alhamdulillah.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Da Dumi-duminsa: ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Basarake A Ondo
Labarai

Wani Sabon Hari Kan Al’ummar Da Ke Iyaka Da Katsina A Kano Ya Rutsa Da Mata 5

November 10, 2025
Matatun mai
Labarai

Yadda Sojoji Suka Tarwatsa Haramtattun Matatun Mai 14 A Yankin Neja Delta 

November 10, 2025
Jibrin Kofa
Labarai

Ɗan Majalisar Wakilai, Jibrin Ƙofa Ya Sauya Sheƙa Daga NNPP Zuwa APC

November 10, 2025
Next Post
Unai Emery Ya Sake Rattaba Kwantiragin Shekaru 5 A Aston Villa

Unai Emery Ya Sake Rattaba Kwantiragin Shekaru 5 A Aston Villa

LABARAI MASU NASABA

Da Dumi-duminsa: ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Basarake A Ondo

Wani Sabon Hari Kan Al’ummar Da Ke Iyaka Da Katsina A Kano Ya Rutsa Da Mata 5

November 10, 2025
Matatun mai

Yadda Sojoji Suka Tarwatsa Haramtattun Matatun Mai 14 A Yankin Neja Delta 

November 10, 2025
Jibrin Kofa

Ɗan Majalisar Wakilai, Jibrin Ƙofa Ya Sauya Sheƙa Daga NNPP Zuwa APC

November 10, 2025
Boko haram

Sojoji Sun Fatattaki Boko Haram, Sun Ceto Mutane 86 Da Aka Sace A Borno

November 10, 2025
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

November 9, 2025
An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

November 9, 2025
Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

November 9, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

November 9, 2025
CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

November 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.