• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kishin Mata Da Kananan Yara Ya Sa Na Kafa Gidauniyata -Maryam Umar

by Abdullahi Muh'd Sheka
2 years ago
in Manyan Labarai, Rahotonni
0
Kishin Mata Da Kananan Yara Ya Sa Na Kafa Gidauniyata -Maryam Umar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hajiya Maryam Umar Kofar Mata, Shugabar Gidauniyar Maryam Kofar Mata, Guda cikin fulogan tafiyar Gidan A A Zaura, sannan ‘yar gaba dai gaba dai a tafiyar Dakta Nasiru Yusif Gawuna.

Mace ta farko data Jagoranci rabawa Mata da Maza tallafi domin Dogaro dakai. A tattaunawartar ta Wakilinmu na Kano Abdullahi Muhammad Sheka.

  • Nnamdi Kanu Ya Maka Gwamnatin Tarayya A Kotun Koli 
  • Gwamnatin Kaduna Ta Jajanta Wa Iyalan Mutane 15 Da ‘Yan Bindiga Suka Kashe

Maryam Kofar Mata ta bayyana dalilin samar da gidauniyar tallafa wa Mata, Marayu da masu karamin karfi, haka kuma ta bayyana matsayar matan Jihar Kano a zaben shekara ta 2023. Ga dai yadda tattaunawar ta Kasance:

Za muso ki gabatar wa da mai karatu kanki da kanki?

Alhamdulillahi kamar yadda aka sani ni sunana Hajiya Maryam Kofar Mata Shugabar Gidauniyar Maryam Kofar Mata ‘Yar Takarar Majalisar Wakilai a Karamar Hukumar Birni da kewaye a baya, guda cikin ‘yan gaba dai Gaba dai na Gidan AA Zaura, sannan guda cikin jagorori Mata Masu yayata kyawawan manufofin Dakta Nasiru Yusif Gawuna dan Takarar Gwamna a Jam’iyyar APC a zaben Shekara ta 2023.

Labarai Masu Nasaba

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

Mene ne dalilin kafa wannan Gidauniya taki?

Kamar yadda aka sani Mata sunfi kowa sanin matsalar Marayu da Mata kasancewarsu masu karamin karfi, wannan dalili yasa na yanke shawarar kafa wannan gidauniya, wadda zuwa yanzu Mata da matasa sama da  300 ne suka amfana da ayyukan da take. Kuma alhamdulillahi akwai rukunin Jama’a daban-daban da suka hada da Mata, Zawarawa, Marayu da marasa galihu da wannan Gidauniya ta duba ta fuskar da za tu kai masu dauki.

Baya ga ayyukan Gidauniyar, an sanki cikin gogaggun ‘yan siyasa Mata da ake damawa dasu, shin ko mene mahangar ki kan zaben shekara ta 2023

Alhamdulillahi yanzu da aka fara kada gangar zaben Shekara ta 2023, daka cikin masu neman kujerar Gwamnan Kano babu wanda ya fi da cewa kamar Dakta Nasiru Yusif Gawuna da sauran ‘yan takarkarun mu daga sama har kasa na Jam’iyyar APC, wannan tasa muka ga ba wanda yafi da cewa da jagorantar Jihar Kano kamar Gawuna da Garo. Haka kuma a Kano ta tsakiya jama’a sun gamsu da nagartar AA Zaura.

Ana ganin kamar ana barin Mata cikin wasu al’amuran siyasa, shin ko me zaki ce a kan haka?

Idan ma ana samun irin wannan wariyar sai dai a wasu jihohin, amma banda Jihar Kano, musamman karkashin Gwamnatin Dakta Abdullahi Umar Ganduje, domin mu a Jihar Kano ba abinda za muce da Khadimul Islam sai godiya, domin a yanzu ba sai gobe ba, babu wata jiha a tarayyar Nijeriya da takai Jihar Kano baiwa Mata mukamai masu Gwabi Gwabi kamar Kano, dubi Kwamishinoni har guda biyu, Shugabar Ma’aikata, ma’ajin Jam’iyyar APC ta Jihar Kano, manyan mashawarta na musamman da mataimaka da sauransu. Saboda haka mu a Jihar Kano lamarin sai godiya.

Kasancewarki mace, shinko wace rawa kike ganin  zaku taka a kakar zaben shekara ta 2023?

Ina tabbatar maka da cewa Mata ne zasu fara yi wa ‘yan takarkarun mu na Jam’iyyar APC luguden kuri’u a lokacin zabe mai zuwa. Domin iyaye mata sun gamsu da kokarin Gwamna Ganduje da kuma mai dakinsa Farfesa Hafsat Ganduje wanda itace tare da jajircewar ta har aka kai ga samun nasarar shigar da mata dukkan mukaman da suke kai a halin yanzu, wannan kuma baya rasa nasaba da kyakkyawar tarbiyarta da kuma kishin cigaban Mata da Kananan yara a Jihar Kano.

Da me kike fatan a dinga tunawa dake?

“Kaunar tallafa wa Mata da Marayu tare da masu karamin karfi, musamman ma ganin haka na taso  a gidanmu na ga mahaifana na hidimtawa Jama’a ba dare ba rana, wannan tasa na yi alkawarin ci gaba da wannan Hidima har zuwa karshen rayuwata.

Duk da cewar ke ba Makamar lissafin habe, da ace abaki damar auna Nasarorin Gwamnatin Dakta Abdullahi Umar Ganduje, Maki nawa zaki bashi?

Ai ko hasidin iza hasada yasan ta Ganduje ba irin tasu bace, shi ne Gwamna daya tilo da ya cika dakacin alkawuran da ya yi wa Jama’a harma da kari. Saboda Haka Khadimul Islam ya canci abashi maki dari bisa dari. Saboda haka muna tabbatarwa da Jam’iyyun Adawa su shafawa kansu Lafiya, domin Kano ta Gawuna da Garo ce da yardar Allah.

Mun gode kwarai da gaske

Nima na gode


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GawunaGidauniyakanoKishiMata
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Kara Baiwa Zimbabwe Allurar Rigakafin COVID-19

Next Post

Abokai Na Zahiri Suna Zurfafa Huldar Zumunci A Sabon Zamani

Related

UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

2 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

7 hours ago
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

13 hours ago
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte
Manyan Labarai

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

17 hours ago
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?
Manyan Labarai

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

18 hours ago
Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar
Manyan Labarai

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

1 day ago
Next Post
Abokai Na Zahiri Suna Zurfafa Huldar Zumunci A Sabon Zamani

Abokai Na Zahiri Suna Zurfafa Huldar Zumunci A Sabon Zamani

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.