• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kishin Mata Da Kananan Yara Ya Sa Na Kafa Gidauniyata -Maryam Umar

by Abdullahi Muh'd Sheka
3 years ago
in Manyan Labarai, Rahotonni
0
Kishin Mata Da Kananan Yara Ya Sa Na Kafa Gidauniyata -Maryam Umar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hajiya Maryam Umar Kofar Mata, Shugabar Gidauniyar Maryam Kofar Mata, Guda cikin fulogan tafiyar Gidan A A Zaura, sannan ‘yar gaba dai gaba dai a tafiyar Dakta Nasiru Yusif Gawuna.

Mace ta farko data Jagoranci rabawa Mata da Maza tallafi domin Dogaro dakai. A tattaunawartar ta Wakilinmu na Kano Abdullahi Muhammad Sheka.

  • Nnamdi Kanu Ya Maka Gwamnatin Tarayya A Kotun Koli 
  • Gwamnatin Kaduna Ta Jajanta Wa Iyalan Mutane 15 Da ‘Yan Bindiga Suka Kashe

Maryam Kofar Mata ta bayyana dalilin samar da gidauniyar tallafa wa Mata, Marayu da masu karamin karfi, haka kuma ta bayyana matsayar matan Jihar Kano a zaben shekara ta 2023. Ga dai yadda tattaunawar ta Kasance:

Za muso ki gabatar wa da mai karatu kanki da kanki?

Alhamdulillahi kamar yadda aka sani ni sunana Hajiya Maryam Kofar Mata Shugabar Gidauniyar Maryam Kofar Mata ‘Yar Takarar Majalisar Wakilai a Karamar Hukumar Birni da kewaye a baya, guda cikin ‘yan gaba dai Gaba dai na Gidan AA Zaura, sannan guda cikin jagorori Mata Masu yayata kyawawan manufofin Dakta Nasiru Yusif Gawuna dan Takarar Gwamna a Jam’iyyar APC a zaben Shekara ta 2023.

Labarai Masu Nasaba

Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Mene ne dalilin kafa wannan Gidauniya taki?

Kamar yadda aka sani Mata sunfi kowa sanin matsalar Marayu da Mata kasancewarsu masu karamin karfi, wannan dalili yasa na yanke shawarar kafa wannan gidauniya, wadda zuwa yanzu Mata da matasa sama da  300 ne suka amfana da ayyukan da take. Kuma alhamdulillahi akwai rukunin Jama’a daban-daban da suka hada da Mata, Zawarawa, Marayu da marasa galihu da wannan Gidauniya ta duba ta fuskar da za tu kai masu dauki.

Baya ga ayyukan Gidauniyar, an sanki cikin gogaggun ‘yan siyasa Mata da ake damawa dasu, shin ko mene mahangar ki kan zaben shekara ta 2023

Alhamdulillahi yanzu da aka fara kada gangar zaben Shekara ta 2023, daka cikin masu neman kujerar Gwamnan Kano babu wanda ya fi da cewa kamar Dakta Nasiru Yusif Gawuna da sauran ‘yan takarkarun mu daga sama har kasa na Jam’iyyar APC, wannan tasa muka ga ba wanda yafi da cewa da jagorantar Jihar Kano kamar Gawuna da Garo. Haka kuma a Kano ta tsakiya jama’a sun gamsu da nagartar AA Zaura.

Ana ganin kamar ana barin Mata cikin wasu al’amuran siyasa, shin ko me zaki ce a kan haka?

Idan ma ana samun irin wannan wariyar sai dai a wasu jihohin, amma banda Jihar Kano, musamman karkashin Gwamnatin Dakta Abdullahi Umar Ganduje, domin mu a Jihar Kano ba abinda za muce da Khadimul Islam sai godiya, domin a yanzu ba sai gobe ba, babu wata jiha a tarayyar Nijeriya da takai Jihar Kano baiwa Mata mukamai masu Gwabi Gwabi kamar Kano, dubi Kwamishinoni har guda biyu, Shugabar Ma’aikata, ma’ajin Jam’iyyar APC ta Jihar Kano, manyan mashawarta na musamman da mataimaka da sauransu. Saboda haka mu a Jihar Kano lamarin sai godiya.

Kasancewarki mace, shinko wace rawa kike ganin  zaku taka a kakar zaben shekara ta 2023?

Ina tabbatar maka da cewa Mata ne zasu fara yi wa ‘yan takarkarun mu na Jam’iyyar APC luguden kuri’u a lokacin zabe mai zuwa. Domin iyaye mata sun gamsu da kokarin Gwamna Ganduje da kuma mai dakinsa Farfesa Hafsat Ganduje wanda itace tare da jajircewar ta har aka kai ga samun nasarar shigar da mata dukkan mukaman da suke kai a halin yanzu, wannan kuma baya rasa nasaba da kyakkyawar tarbiyarta da kuma kishin cigaban Mata da Kananan yara a Jihar Kano.

Da me kike fatan a dinga tunawa dake?

“Kaunar tallafa wa Mata da Marayu tare da masu karamin karfi, musamman ma ganin haka na taso  a gidanmu na ga mahaifana na hidimtawa Jama’a ba dare ba rana, wannan tasa na yi alkawarin ci gaba da wannan Hidima har zuwa karshen rayuwata.

Duk da cewar ke ba Makamar lissafin habe, da ace abaki damar auna Nasarorin Gwamnatin Dakta Abdullahi Umar Ganduje, Maki nawa zaki bashi?

Ai ko hasidin iza hasada yasan ta Ganduje ba irin tasu bace, shi ne Gwamna daya tilo da ya cika dakacin alkawuran da ya yi wa Jama’a harma da kari. Saboda Haka Khadimul Islam ya canci abashi maki dari bisa dari. Saboda haka muna tabbatarwa da Jam’iyyun Adawa su shafawa kansu Lafiya, domin Kano ta Gawuna da Garo ce da yardar Allah.

Mun gode kwarai da gaske

Nima na gode


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GawunaGidauniyakanoKishiMata
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Kara Baiwa Zimbabwe Allurar Rigakafin COVID-19

Next Post

Abokai Na Zahiri Suna Zurfafa Huldar Zumunci A Sabon Zamani

Related

Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano
Manyan Labarai

Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano

4 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

15 hours ago
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

1 day ago
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

2 days ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

2 days ago
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

2 days ago
Next Post
Abokai Na Zahiri Suna Zurfafa Huldar Zumunci A Sabon Zamani

Abokai Na Zahiri Suna Zurfafa Huldar Zumunci A Sabon Zamani

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta

Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta

August 25, 2025
Ƙungiyar KSCI Ta Nemi Sabon Tsari Don Magance Ƴan Bindiga A Katsina

Ƙungiyar KSCI Ta Nemi Sabon Tsari Don Magance Ƴan Bindiga A Katsina

August 25, 2025
Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano

Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano

August 25, 2025
Tinubu Ya Isa Brazil, Zai Nemi Masu Zuba Jarin Biliyoyi A Noma, Makamashi Da Fasaha

Tinubu Ya Isa Brazil, Zai Nemi Masu Zuba Jarin Biliyoyi A Noma, Makamashi Da Fasaha

August 25, 2025

ÆŠaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

August 24, 2025
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

August 24, 2025
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

August 24, 2025
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

August 24, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

August 24, 2025
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.