ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Da Gaske Ne Kasar Sin Barazana Ce?

by CMG Hausa
3 years ago
Kasar Sin

Kafar yada labaran kimiyya ta kasar Amurka da ake kira Protocol, ta wallafa wani rahoton da babbar ’yar jarida Kate Kaye ta bayar, bisa binciken da ta gudanar a kwanan baya, inda ta tona yadda Eric Schmidt, tsohon babban jami’in kamfanin Google, ya ci kazamar riba ta hanyar yayata ra’ayin nan na wai “kasar Sin na haifar da babbar barazana ga Amurka ta fannin fasaha.” 

An ce, a yayin da yake kan kujerar shugabancin kwamitin tsaron kasar Amurka ta fannin fasahar kwaikwayon tunanin dan Adam, ya yi ta bayyana wa gwamnatin kasar damuwar yadda Amurka din ta gaza a takararta da kasar Sin, ta fannin fasahar kwaikwayon tunanin dan Adam, don sa kaimi ga gwamnati ta zuba makudan kudade a fannin nazarin fasahar.

  • CCPIT: Cinikin Waje Na Samun Ci Gaba Yadda Ya Kamata A Kasar Sin

A sa’i daya kuma, kasancewarsa babban mai zuba jari ta fannin nazarin fasahar kwaikwayon tunanin dan Adam, Eric Schmidt ya ci riba mai tsoka bisa ga yadda yake zuba jari a kamfanonin da suka samu kwangila mai tarin kudi daga gwamnatin kasar.

ADVERTISEMENT

A hakika, Amurka ta dade tana fakewa da batun “tsaron kasa” wajen dakile kamfanin kimiyya na kasar Sin, inda ta mayar da harkokin kimiyya da cinikayya a siyasance kuma a matsayin makami. Kuma faduwar ta zo daidai da zama yadda mutane irin Schmidt suka rika baiwa gwamnati shawarwari na wai “kasar Sin barazana ce”, duk da cewa, ko da gaske ne suna damuwa da tsaron kasarsu, amma dai mun san cewa suna cin kudin yin hakan.

A yayin da mutane irinsu Schmidt suke ta hada kai da ’yan siyasar Amurka, Amurka kuma take kara yin babakere a fannin kimiyya.

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Tsokaci Kan Kalaman Da Firaministar Japan Takaichi Sanae Ta Yi A Kanta

Kasar Sin Ta Kara Azamar Kirkiro Da Fasahar Sadarwar 6G

Yadda Amurka ke rika siyasantar da harkokin kimiyya da cinikayya, ya keta dokokin cinikayyar duniya, haka kuma ya lalata tsarin samar da kayayyaki, da ma ci gaban harkokin kimiyya a duniya.

A yayin da sassan kasa da kasa ke kara dunkulewa da juna, ya zama dole su hada gwiwa da juna don tabbatar da ci gabansu. Wadanda ke neman toshe hanyoyin wasu, hanyoyinsu ne za su toshe. (Mai zane: Mustapha Bulama)

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin Ta Yi Tsokaci Kan Kalaman Da Firaministar Japan Takaichi Sanae Ta Yi A Kanta
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Tsokaci Kan Kalaman Da Firaministar Japan Takaichi Sanae Ta Yi A Kanta

November 14, 2025
Kasar Sin Ta Kara Azamar Kirkiro Da Fasahar Sadarwar 6G
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Kara Azamar Kirkiro Da Fasahar Sadarwar 6G

November 14, 2025
Kalubalantar Ka’idar “Kasar Sin Daya Tak A Duniya” Tamkar Wasa Da Wuta Ne
Daga Birnin Sin

Kalubalantar Ka’idar “Kasar Sin Daya Tak A Duniya” Tamkar Wasa Da Wuta Ne

November 14, 2025
Next Post
Mijina Wayayyen Bafulatani Ne, Ba Bafulatanin Daji Ba Ne – Uwargidan Atiku

Mijina Wayayyen Bafulatani Ne, Ba Bafulatanin Daji Ba Ne - Uwargidan Atiku

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Tsokaci Kan Kalaman Da Firaministar Japan Takaichi Sanae Ta Yi A Kanta

Sin Ta Yi Tsokaci Kan Kalaman Da Firaministar Japan Takaichi Sanae Ta Yi A Kanta

November 14, 2025
Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

November 14, 2025
ADC Ta Tsara Ka’idojin Da Shugabanninta Za Su Bi Don Tunkarar Zaben 2027

ADC Ta Tsara Ka’idojin Da Shugabanninta Za Su Bi Don Tunkarar Zaben 2027

November 14, 2025

Rikicin PDP: Fiye Da Wakilai 3,000 Ne Za Su Raba Gardama A Babban Taron Jam’iyyar

November 14, 2025
Kasar Sin Ta Kara Azamar Kirkiro Da Fasahar Sadarwar 6G

Kasar Sin Ta Kara Azamar Kirkiro Da Fasahar Sadarwar 6G

November 14, 2025
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

November 14, 2025
Kalubalantar Ka’idar “Kasar Sin Daya Tak A Duniya” Tamkar Wasa Da Wuta Ne

Kalubalantar Ka’idar “Kasar Sin Daya Tak A Duniya” Tamkar Wasa Da Wuta Ne

November 14, 2025
Musulmin da Aka Kashe  A Zamfara, Katsina Da Sokoto Sun Ninka Na Kiristoci A Tsakiyar Najeriya: MACBAN

Musulmin da Aka Kashe  A Zamfara, Katsina Da Sokoto Sun Ninka Na Kiristoci A Tsakiyar Najeriya: MACBAN

November 14, 2025
Manzon Allah (SAW) A Matsayin Dan Gatan Allah 

Manzon Allah (SAW) A Matsayin Dan Gatan Allah 

November 14, 2025
Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma: Martani

Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma: Martani

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.