• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Jam’iyyun Adawa Na Iya Kai Bantensu A 2027?

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
8 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Ko Jam’iyyun Adawa Na Iya Kai Bantensu A 2027?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tun bayan sauyin siyasa a shekarar 2015, lokacin da jam’iyyar APC ta kayar da jam’iyyar PDP shekaru biyu kacal da kafuwarta, jam’iyyun adawa a Nijeriya suke matuka fuskanci rikice-rikicen shugabanci.

Masu fashin baki dai na ganin cewa jam’iyyun adawa sun yi rauni, inda a yanzu babu wata jam’iyya za ta iya kalubalantar jam’iyyar APC mai mulki.

  • Gwamnatin Katsina Ta Fitar Da Naira Miliyan Dubu 50 Domin Samar Da Ruwan Sha 
  • Cece-kuce Ya Barke Kan Shirin “Kur’anic Convention”

Sun yi ikirarin cewa maimakon samar da wata gwamnati ta daban ko samar da ingantaccen bincike, jam’iyyun adawa sun shiga cikin rikicin cikin gida. Har ila yau, sun kasa gina tushe mai inganci don kalubalantar halin da ake ciki yadda ya kamata.

Hasali ma, mafi yawan manazarta na ganin cewa rashin iya zama tare na shugabannin ‘yan adawa gabanin zaben 2023 ne silar share fagen nasarar zaben Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu.

Tun daga wancan lokaci rigingimun cikin gida a tsakanin jam’iyyun adawa sun zama ruwan dare, sakamakon batutuwan da suka hada da zaben fid da gwani, dakatar da manyan mutane, dambarwar ‘yan takara, magudi wajen zaben shugabannin jam’iyya, da hargitsa tarurruka. Jam’iyyun sun kuma fuskanci cin zarafi na kundin tsarin mulki na 1999, da dokar zabe da na jam’iyyunsu.

Labarai Masu Nasaba

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

A kwanakin baya, jam’iyyar PDP da sauran jam’iyyun adawa sun zargi APC da ruruta wutar rikicin da ke tsakaninsu, inda suka yi zargin cewa jam’iyya mai mulki na neman murkushe ‘yan adawa domin tabbatar da ci gaba da mulkin Shugaba Tinubu a 2027. APC ta musanta wadannan ikirari.

Tun da aka hambarar da jam’iyyar PDP, jam’iyyun adawa sun yi yunkuri da dama amma ba su samu nasara ba. Na baya-bayan nan shi ne samar da wata sabon jam’iyyar siyasa mai suna ‘The Alternatibe’, domin tabbatar da madafun iko a babban zabe na 2027. Wani tsohon dan takarar shugabancin jam’iyyar PDP na kasa, Segun Sowunmi, wanda ke tallata wannan sabuwar jam’iyyar, ya ce an kafa jam’iyyar ne saboda ‘yan Nijeriya sun gaji da tsarin siyasar da ake da su, suna kuma neman hanyar da ta dace.

Kafin wannan, a shekarar 2018, jam’iyyar PDP ta kulla kawance da wasu jam’iyyun siyasa 38, inda suka sanya mata suna ‘Coalition of United Political Parties’ (CUPP) a wani taro da aka gudanar a cibiyar Musa Yar’adua da ke Abuja. Wannan gamayyar dai ta yi nufin kayar da tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari da jam’iyyar APC a zaben 2019. Shugabannin jam’iyyun ADC, SDP, NCP, LP, da sauran jam’iyyu da dama da suka yi rajista sun halarci taron.

Sai dai kawancen ta kasa hana Buhari sake lashe zabe, saboda rashin kokarin habaka dimokuradiyya na samun goyon bayan ‘yan Nijeriya.

A ranar 6 ga Disamba, 2023, PDP, NNPP da wasu jam’iyyun siyasa biyar suka kafa sabuwar kawance. Jam’iyyun da abin ya shafa sun hada da ADC, APM, SDP, YPP da ZLP.

Wannan sabon yunkuri mai suna ‘Coalition of Concerned Political Parties’ (CCPP), an kafa shi ne a sakatariyar jam’iyyar SDP ta kasa da ke Abuja. Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben 2023, Atiku Abubakar, ya bukaci jam’iyyun adawa da su hada kai a yunkurin kwace mulki daga hannun APC.

A ranar 12 ga Disamba, 2024, jam’iyyar PRP ta tabbatar da cewa ta fara tattaunawa da jam’iyyar ADC gabanin zaben 2027.

Shugaban jam’iyyar PRP na kasa, Falalu Bello ya tabbatar da tattaunawar a wani taron manema labarai na hadin gwiwa da shugaban ADC, Ralph Nwosu a Abuja. Bello ya jaddada cewa, “Mun fara tattaunawa. Ba ma tsoron hadewa kwata-kwata. Jam’iyyar PRP ita ce jam’iyyar siyasa mafi dadewa a yau, kuma muna da tarihin kawance da suka samu nasara.”

Ana ta rade-radin cewa za a raba madafun iko tsakanin Atiku, Kwankwaso da Obi, inda Atiku zai yi mulki na tsawon shekaru hudu, sai kuma Kwankwaso na wasu shekaru hudu, da Obi na tsawon shekaru takwas. Sai dai a kwanakin baya Kwankwaso ya musanta wanzuwar irin wannan yarjejeniya, inda ya bayyana hakan a matsayin kage.

Shi ma ya musanta wata tattaunawa na hadewa ko yarjejeniyar siyasa da PDP, NNPP ko wata jam’iyya.

Wani mai sharhi kan harkokin siyasa, Jackson Lekan Ojo, ya yi imanin cewa jam’iyyun adawa za su iya kayar da Tinubu a 2027 idan suka yi amfani da dabaru irin na APC kafin zaben 2015. Ojo ya kara da cewa akwai batutuwa da dama a karkashin wannan gwamnati da ‘yan adawa za su iya cin gajiyarsu, da suka hada da kalubalen tsaro, tabarbarewar tattalin arziki, da kuma cin hanci da rashawa.

“Idan har jam’iyyun adawa suka hada kai suka mayar da hankali kan gazawar gwamnati mai ci, musamman matsalar tsaro da tabarbarewar tattalin arzikin kasar, za su iya samun nasara. Abu mai muhimmancin shi ne, a zakulo dan takara mai karfi wanda zai iya hada kan ‘yan adawa tare da gabatar da sahihin zabi,” in ji Ojo.

Daraktan makarantar nazarin zamantakewar siyasa ta Abuja, Dakta Sam Amadi ya yi imanin cewa hadewar jam’iyyun adawa za ta iya yin nasara idan har shugabannin ‘yan adawa suka kuduri aniyar cimma wata manufa ta ci gaban kasa tare da ajiye muradun kashin kai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Nijeriya Na Da Dimbin Dukiyar Da Tinubu Zai Rika Tafiye-tafiye Zuwa Kasashen Waje – Minista

Next Post

Rikicin Shugabanci Na Barazana Ga Babban Taron Jam’iyyar PDP

Related

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

2 weeks ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

2 weeks ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

2 weeks ago
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

3 weeks ago
katin zabe
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

3 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

3 weeks ago
Next Post
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi

Rikicin Shugabanci Na Barazana Ga Babban Taron Jam’iyyar PDP

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

September 18, 2025
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

September 18, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

September 18, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

September 17, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.