ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, November 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

by Yusuf Shuaibu
6 months ago
Saraki

Yayin da zaben 2027 ke kara karatowa, babbar jam’iyyar adawa ta Nijeriya wato PDP, ta fada cikin rarrabuwan kai, radani da kuma sauya sheka daga wasu fusatattun ‘ya’yanta.

Bisa ci gaba da fuskantar sauya shekar mambobinta zuwa jam’iyyar APC mai mulki da kuma rikicin cikin gida, PDP ta fahimci cewa akwai bukatar daidaita lafiyarta kafin lokaci ya kure mata.

  • Masanan Najeriya Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwar Afirka Da Sin A Fannin Tinkarar Kalubalen Harajin Kwastam Na Amurka
  • Yawan Wutar Lantarkin Da Sin Ke Iya Samar Ta Amfani Da Karfin Ruwa Ta Kai Matsayin Koli A Duniya

Don aiwatar da wannan muhimmin aiki, gwamnonin da tsofaffin gwamnonin da aka zaba karkashin jam’iyyar sun bukaci tsohon shugaban majalisar dattijai Bukola Saraki ya jagoranci aikin ceto jam’iyyar daga rugujewa.

ADVERTISEMENT

An dora wa tsohon gwamnan Jihar Kwara alhakin jagorantar tattaunawar zaman lafiya a tsakanin bangarorin PDP masu rabuwan kai da warware rikicin game da matsayin sakataren jam’iyyar kafin zaben 2027.

Aikin da aka dora wa Saraki yana da mutukar wahala, don haka masana harkokin siyasa ke ci gaba da saka alamar tambaya kan cewa zai iya kawo zaman lafiya a jam’iyyar PDP?

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Tsara Ka’idojin Da Shugabanninta Za Su Bi Don Tunkarar Zaben 2027

Rikicin PDP: Fiye Da Wakilai 3,000 Ne Za Su Raba Gardama A Babban Taron Jam’iyyar

PDP na fama da rikicin cikin gida mafi muni a tarihin jam’iyyar. Tun lokacin da jam’iyyar ta rasa shugabanci a 2015, ta ci gaba da fuskantar matsaloli wajen magance rikicin da take fama da shi. Ko wani zabe yana zuwa da nashi kalubalan, yana bayyana cin amana na cikin jam’iyya.

Zaben 2023, jam’iyyar ta bai wa Atiku Abubakar takarar shugaban kasa, wanda shi dan Arewa ne, inda lamarin ya haifar da fushi na masu ruwa da tsaki daga kudancin kasar nan, musamman daga wajen ministan Abuja na yanzu, Nyesom Wike.

Haka ma a daidai lokacin da ake kara fuskantar zaben 2027, wannan yanayi na sake kara bayyana adaidai lokacin da Atiku ke kokarin samun tikitin jam’iyyar. A lokaci guda, Wike ya bayyana matsayinsa a fili kan zaben da ke tafe.

A wani taron manema labarai na kwanan nan, tsohon gwamnan Jihar Ribas ya yi gargadin kar jam’iyyar ta bai wa wani dan takarar shugaban kasa daga yankin Arewa, ya yi hasashen cewa PDP za ta sake shan kaye idan har ta kara yin wannan kuskuren.

Ko shugabannin PDP sun ji dadin hakan ko ba su ji dadin ba, matsayin Wike ya dace da mutanen Kudu, wadanda ke ganin yankinsu ya cancanta ya kammala shugabancin shekaru takwas kafin mulki ya dawo Arewacin Nijeriya.

Matsalar tsarin karba-karba ta kunno kai ne bayan da Atiku ya zama dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar a 2023, madadin kira na neman dan takara daga Kudu.

Wannan ya bai wa Wike damar yakar PDP. Lmarin da ya kulla dangantaka da APC, wanda ya sanya shi ya zama babban abokin hamayya a jam’iyyar.

Yanzu, PDP na fuskantar wannan yanayin na bin tsarin karba-karba kafin 2027. Masu nazarin harkokin siyasa na jiran ganin yadda za ta kaya a wannan lamari tsakanin Kudu da Arewa.

Duk da haka, yayin da masu ruwa da tsaki daga Arewa ke ganin cewa yawansu na iya taimaka wa PDP dawo da iko, abokansu daga Kudu sun yi imani da cewa fitar da dan takarar shugaban kasa daga yankinsu zai taimaka wa jam’iyyar wajen dawo da wurare masu mahimmanci da suka rasa.

Dangane da wannan, Saraki na jagorantar kwamitin sulhu da ke fuskantar kalubale masu yawan gaske. An da dora masa alhakkin dawo da martaban jam’iyyar da sulhunta tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar masu mukami da wadanda ba su da mukami.

An dai nada Saraki wannan matsayin ne saboda dabarunsa na tsare-tsare da iya yin sulhu, ya shawo kan manyan batutuwan siyasa a cikin tarihinsa. Haka ma ko a lokacin da ya zama shugaban majalisar dattawa ya samu nasarar hada kan ‘yan majalisa a cikin yanayi na muni wajen shugabanci.

Duk abin da Saraki ke shirin yi, matakan sulhunsa dole ne su hada da shirye-shiryen da za su gamsar da masu goyon bayan Wike, sake hada masu ruwa da tsaki daga kowane yanki da kuma sake fasalta rabon mukamai na jam’iyyar don kawo daidaiton siyasa a Nijeriya. Wannan aiki ne mai wahala, amma ‘yan Nijeriya da dama na ganin cewa Saraki yana da kwarewar siyasa da zai iya yin wannan jan aikin idan har jam’iyyar ta ba shi dama.

Idan har kokarin sulhu na Saraki ya gaza, to a bayyana yake PDP za ta rasa madafa, sannan za ta kara fadawa cikin Rashin tabbas. Amma idan ya yi nasara, zai iya dawo da martabar siyasar jam’iyyar a Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ADC Ta Tsara Ka’idojin Da Shugabanninta Za Su Bi Don Tunkarar Zaben 2027
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Tsara Ka’idojin Da Shugabanninta Za Su Bi Don Tunkarar Zaben 2027

November 14, 2025
Tambarin Dimokuradiyya

Rikicin PDP: Fiye Da Wakilai 3,000 Ne Za Su Raba Gardama A Babban Taron Jam’iyyar

November 14, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya
Tambarin Dimokuradiyya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
Next Post
Kungiyar Tsofaffin Ɗaliban BUK Ta Karrama Dr. Sani Dauda Ibrahim Da Walimar Kammala Digiri Na 3

Kungiyar Tsofaffin Ɗaliban BUK Ta Karrama Dr. Sani Dauda Ibrahim Da Walimar Kammala Digiri Na 3

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Sin Ba Ta Taba Bukatar Kamfanoni Su Tattara Ko Adana Bayanai Ba Bisa Ka’ida Ba Kuma Ba Za Ta Yi Hakan Ba 

Gwamnatin Sin Ba Ta Taba Bukatar Kamfanoni Su Tattara Ko Adana Bayanai Ba Bisa Ka’ida Ba Kuma Ba Za Ta Yi Hakan Ba 

November 17, 2025
Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

November 17, 2025
Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

November 17, 2025
An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing

An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing

November 17, 2025
NBS

Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ta Ragu Zuwa Kashi 16.065%

November 17, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Rasha Domin Halartar Taron SCO

Firaministan Sin Ya Isa Rasha Domin Halartar Taron SCO

November 17, 2025
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

November 17, 2025
Kudaden Kasafin Kudin Sin Sun Karu Da Kashi 0.8 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

Kudaden Kasafin Kudin Sin Sun Karu Da Kashi 0.8 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

November 17, 2025
Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

November 17, 2025
An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

November 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.