• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

by Yusuf Shuaibu
4 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da zaben 2027 ke kara karatowa, babbar jam’iyyar adawa ta Nijeriya wato PDP, ta fada cikin rarrabuwan kai, radani da kuma sauya sheka daga wasu fusatattun ‘ya’yanta.

Bisa ci gaba da fuskantar sauya shekar mambobinta zuwa jam’iyyar APC mai mulki da kuma rikicin cikin gida, PDP ta fahimci cewa akwai bukatar daidaita lafiyarta kafin lokaci ya kure mata.

  • Masanan Najeriya Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwar Afirka Da Sin A Fannin Tinkarar Kalubalen Harajin Kwastam Na Amurka
  • Yawan Wutar Lantarkin Da Sin Ke Iya Samar Ta Amfani Da Karfin Ruwa Ta Kai Matsayin Koli A Duniya

Don aiwatar da wannan muhimmin aiki, gwamnonin da tsofaffin gwamnonin da aka zaba karkashin jam’iyyar sun bukaci tsohon shugaban majalisar dattijai Bukola Saraki ya jagoranci aikin ceto jam’iyyar daga rugujewa.

An dora wa tsohon gwamnan Jihar Kwara alhakin jagorantar tattaunawar zaman lafiya a tsakanin bangarorin PDP masu rabuwan kai da warware rikicin game da matsayin sakataren jam’iyyar kafin zaben 2027.

Aikin da aka dora wa Saraki yana da mutukar wahala, don haka masana harkokin siyasa ke ci gaba da saka alamar tambaya kan cewa zai iya kawo zaman lafiya a jam’iyyar PDP?

Labarai Masu Nasaba

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

PDP na fama da rikicin cikin gida mafi muni a tarihin jam’iyyar. Tun lokacin da jam’iyyar ta rasa shugabanci a 2015, ta ci gaba da fuskantar matsaloli wajen magance rikicin da take fama da shi. Ko wani zabe yana zuwa da nashi kalubalan, yana bayyana cin amana na cikin jam’iyya.

Zaben 2023, jam’iyyar ta bai wa Atiku Abubakar takarar shugaban kasa, wanda shi dan Arewa ne, inda lamarin ya haifar da fushi na masu ruwa da tsaki daga kudancin kasar nan, musamman daga wajen ministan Abuja na yanzu, Nyesom Wike.

Haka ma a daidai lokacin da ake kara fuskantar zaben 2027, wannan yanayi na sake kara bayyana adaidai lokacin da Atiku ke kokarin samun tikitin jam’iyyar. A lokaci guda, Wike ya bayyana matsayinsa a fili kan zaben da ke tafe.

A wani taron manema labarai na kwanan nan, tsohon gwamnan Jihar Ribas ya yi gargadin kar jam’iyyar ta bai wa wani dan takarar shugaban kasa daga yankin Arewa, ya yi hasashen cewa PDP za ta sake shan kaye idan har ta kara yin wannan kuskuren.

Ko shugabannin PDP sun ji dadin hakan ko ba su ji dadin ba, matsayin Wike ya dace da mutanen Kudu, wadanda ke ganin yankinsu ya cancanta ya kammala shugabancin shekaru takwas kafin mulki ya dawo Arewacin Nijeriya.

Matsalar tsarin karba-karba ta kunno kai ne bayan da Atiku ya zama dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar a 2023, madadin kira na neman dan takara daga Kudu.

Wannan ya bai wa Wike damar yakar PDP. Lmarin da ya kulla dangantaka da APC, wanda ya sanya shi ya zama babban abokin hamayya a jam’iyyar.

Yanzu, PDP na fuskantar wannan yanayin na bin tsarin karba-karba kafin 2027. Masu nazarin harkokin siyasa na jiran ganin yadda za ta kaya a wannan lamari tsakanin Kudu da Arewa.

Duk da haka, yayin da masu ruwa da tsaki daga Arewa ke ganin cewa yawansu na iya taimaka wa PDP dawo da iko, abokansu daga Kudu sun yi imani da cewa fitar da dan takarar shugaban kasa daga yankinsu zai taimaka wa jam’iyyar wajen dawo da wurare masu mahimmanci da suka rasa.

Dangane da wannan, Saraki na jagorantar kwamitin sulhu da ke fuskantar kalubale masu yawan gaske. An da dora masa alhakkin dawo da martaban jam’iyyar da sulhunta tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar masu mukami da wadanda ba su da mukami.

An dai nada Saraki wannan matsayin ne saboda dabarunsa na tsare-tsare da iya yin sulhu, ya shawo kan manyan batutuwan siyasa a cikin tarihinsa. Haka ma ko a lokacin da ya zama shugaban majalisar dattawa ya samu nasarar hada kan ‘yan majalisa a cikin yanayi na muni wajen shugabanci.

Duk abin da Saraki ke shirin yi, matakan sulhunsa dole ne su hada da shirye-shiryen da za su gamsar da masu goyon bayan Wike, sake hada masu ruwa da tsaki daga kowane yanki da kuma sake fasalta rabon mukamai na jam’iyyar don kawo daidaiton siyasa a Nijeriya. Wannan aiki ne mai wahala, amma ‘yan Nijeriya da dama na ganin cewa Saraki yana da kwarewar siyasa da zai iya yin wannan jan aikin idan har jam’iyyar ta ba shi dama.

Idan har kokarin sulhu na Saraki ya gaza, to a bayyana yake PDP za ta rasa madafa, sannan za ta kara fadawa cikin Rashin tabbas. Amma idan ya yi nasara, zai iya dawo da martabar siyasar jam’iyyar a Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: PDPSaraki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Gwamnatin Jamus Friedrich Merz

Next Post

Kungiyar Tsofaffin ÆŠaliban BUK Ta Karrama Dr. Sani Dauda Ibrahim Da Walimar Kammala Digiri Na 3

Related

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

7 days ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

1 week ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

1 week ago
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

2 weeks ago
katin zabe
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

2 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga ZaÉ“en Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

2 weeks ago
Next Post
Kungiyar Tsofaffin ÆŠaliban BUK Ta Karrama Dr. Sani Dauda Ibrahim Da Walimar Kammala Digiri Na 3

Kungiyar Tsofaffin ÆŠaliban BUK Ta Karrama Dr. Sani Dauda Ibrahim Da Walimar Kammala Digiri Na 3

LABARAI MASU NASABA

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

September 13, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi GargaÉ—i Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi GargaÉ—i Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

September 13, 2025
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

September 12, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi GargaÉ—i Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi GargaÉ—i Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

September 12, 2025
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.