• English
  • Business News
Thursday, October 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Wace Kwarya Tana Da Abokin Burminta

by CMG Hausa
3 years ago
Kwarya

A kwanakin baya, na zanta da wasu masana a yayin wani taro da ya gudana a birnin Beijing, karkashin laimar dandalin masanan Sin da Afirka, inda kalaman da wani masani dan kasar Habasha mai suna Yonas Adaye ya yi, ya burge ni matuka.

Ya ce, “sakamakon bambancin al’adu da tarihi, ba za samu wani tsarin raya kasa da zai biya bukatun dukkan kasashe ba. Wasu kasashen yamma na ganin cewa, ‘Ba za a samu nasarar tafiyar da harkokin mulki ba, idan ba a rungumi tsarinmu ba.’

  • Kasuwanci Bangaren Da Ba Na Masana’Antun Kira Ba A Sin Ya Ci Gaba Da Farfadowa A Watan A Yuli

Amma kasashen Afirka ba za su ci gaba da amincewa da ra’ayinsu ba.” Na yarda da ra’ayin masanin. Saboda idan muka nazarci fasahohin da kasar Sin ta samu, to, dole ne duk wata kasa mai tasowa ta yi kokarin bin turbar raya kasa ta kanta, kafin ta iya samun ci gaba mai dorewa.

Tun bayan kafuwar jamhuriyar jama’ar kasar Sin a shekarar 1949, kasar ta nace da zama karkashin mulkin jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, da turbar tsarin gurguzu mai halayyar musamman ta Sin. Hakan a ganin kasashen yamma, wai “mulkin kama karya” ne. Sai dai sakamakon da kasar Sin ta samu karkashin turbar da ta tsara da kanta, shi ne ya haifar da ci gaban tattalin arzikinta.

Wanimasani a kasar Afirka ya taba bayyana cewa, “ Jimillar GDPn kasar Kenya ta fi ta kasar Sin yawa, a shekarar 1961. Amma zuwa shekarar 2020, GDPn Kenya ya karu da ninki 3, yayin da jimillar ta kasar Sin ta karu da ninki 50.” Kalamansa sun shaida cewa, turbar da kasar Sin ta zaba, ita ce daidai.

LABARAI MASU NASABA

Diflomasiyyar Shugabanni Na Matukar Taka Rawar Gani Wajen Jagorantar Dangantakar Sin Da Amurka

Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11

Cikin shekaru 5 da suka wuce, duniyarmu ta yi fama da koma bayan tattalin arziki. Inda aka fuskanci tarin kalubaloli, da tsanantar rikici tsakanin wasu kasashe, ko tsakanin al’ummomin wata kasa.

Amma kasar Sin tana bin hanyarta ta neman ci gaba yadda ya kamata. Wasu abubuwan da na gani da ido su ne: Mazauna kauyuka sun samu wadata ta hanyar raya harkar yawon shakatawa, ko kuma tallata amfanin gona ta kafar Internet.

Yayin da a cikin birane, ana samun karin itatuwa da bishiyoyi, da kyautatuwar muhallin zama. Kana ‘yan saman jannatin kasar Sin suna zirga-zirga a sararin samaniya ta cikin kumbunan kasar.

Ban da wannan kuma, kasar ta yi nasarar shawo kan yaduwar cutar COVID-19, da maido da ayyuka masu alaka da tattalin arziki cikin sauri. Haka zalika, a yankin Hong Kong na kasar, kasar Amurka ta ci tura a yunkurin na ta da tarzoma, da juyin juya hali, inda aka maido da kwanciyar hankali a yankin, bisa matakan shari’a da kasar Sin ta dauka.

Ban da wannan kuma, na ga yadda kasar Sin ta iya kare cikakkun yankunanta daga kasar da take nuna fin karfi a duniya. Kana abu mai muhimmanci shi ne, na ga yadda Sinawa suke nuna cikakken imani kan turbarsu, inda ko da yake suna kokarin tinkarar matakan wasu kasashe na neman shafawa kasar Sin bakin fenti, da hana ta samun ci gaba, a hannu guda kuma suna nacewa kan akidar al’ummar dan Adam mai makomar bai daya, da hadin gwiwa don moriyar dukkan bangarori.

Hausawa su kan ce, “Ko wace kwarya tana da abokin burminta”, kana “ Kayan aro ba ya rufe katara.” Idan mun ce kasar Sin na da wani asiri na raya kai, to wannan shi ne zabin turbar da ta dace da yanayin kasa, da kokarin tabbatar da kwanciyar hankali, gami da raya tattalin arziki.

Idan al’ummar wata kasa suna iya kiyaye wani yanayi na hadin kai da juna, a kokarin raya kasarsu, ba tare da ta da zaune-tsaye ba, to, duk wani kalubale, ba zai iya hana kasar samun ci gaba ba. (Bello Wang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 
Daga Birnin Sin

Diflomasiyyar Shugabanni Na Matukar Taka Rawar Gani Wajen Jagorantar Dangantakar Sin Da Amurka

October 22, 2025
Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11
Daga Birnin Sin

Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11

October 22, 2025
Nesa Ta Zo Kusa: Maraba Da Sabon Jirgin Kasa Samfurin CR450 Da Kasar Sin Ta Kera
Daga Birnin Sin

Nesa Ta Zo Kusa: Maraba Da Sabon Jirgin Kasa Samfurin CR450 Da Kasar Sin Ta Kera

October 22, 2025
Next Post
Giwa Ta Halaka Tsohuwa, Ta Sake Bin Gawarta Ta Tattake Ana Tsaka Da Jana’izarta

Giwa Ta Halaka Tsohuwa, Ta Sake Bin Gawarta Ta Tattake Ana Tsaka Da Jana'izarta

LABARAI MASU NASABA

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Sojoji Sun Kama Fitaccen Ɗan Bindiga Babawo Badoo Da Wasu 37 A Filato 

October 23, 2025
Yadda DSS Suka Kama Masu Safarar Makamai Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kaduna

Yadda DSS Suka Kama Masu Safarar Makamai Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kaduna

October 23, 2025
Gwamna Abba Ya Jaddada Mubaya’arsa Ga Kwankwaso 

Gwamna Abba Ya Jaddada Mubaya’arsa Ga Kwankwaso 

October 23, 2025
Shugabannin jam’iyyar PDP Na Arewa Sun Amince Da Turaki A Matsayin Ɗan Takarar Shugabancin Jam’iyyar Na Ƙasa

Shugabannin jam’iyyar PDP Na Arewa Sun Amince Da Turaki A Matsayin Ɗan Takarar Shugabancin Jam’iyyar Na Ƙasa

October 23, 2025
Yajin aiki

Gwamnatin Tarayya Ta Jajantawa Waɗanda Fashewar Tankar Mai Ta Rutsa Da Su A Neja 

October 23, 2025
Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Naira Biliyan 2.5 Na Aikin Haƙo Uranium, Mai Da Iskar Gas

Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Naira Biliyan 2.5 Na Aikin Haƙo Uranium, Mai Da Iskar Gas

October 23, 2025
Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Diflomasiyyar Shugabanni Na Matukar Taka Rawar Gani Wajen Jagorantar Dangantakar Sin Da Amurka

October 22, 2025
NUJ Reshen Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa

NUJ Reshen Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa

October 23, 2025
Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11

Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11

October 22, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Cafke Wani Matashi Ɗan Shekara 15 Da Ake Zargi Da Yin Fashi Da Makami A Gombe

October 22, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.