• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Wace Kwarya Tana Da Abokin Burminta

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ko Wace Kwarya Tana Da Abokin Burminta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kwanakin baya, na zanta da wasu masana a yayin wani taro da ya gudana a birnin Beijing, karkashin laimar dandalin masanan Sin da Afirka, inda kalaman da wani masani dan kasar Habasha mai suna Yonas Adaye ya yi, ya burge ni matuka.

Ya ce, “sakamakon bambancin al’adu da tarihi, ba za samu wani tsarin raya kasa da zai biya bukatun dukkan kasashe ba. Wasu kasashen yamma na ganin cewa, ‘Ba za a samu nasarar tafiyar da harkokin mulki ba, idan ba a rungumi tsarinmu ba.’

  • Kasuwanci Bangaren Da Ba Na Masana’Antun Kira Ba A Sin Ya Ci Gaba Da Farfadowa A Watan A Yuli

Amma kasashen Afirka ba za su ci gaba da amincewa da ra’ayinsu ba.” Na yarda da ra’ayin masanin. Saboda idan muka nazarci fasahohin da kasar Sin ta samu, to, dole ne duk wata kasa mai tasowa ta yi kokarin bin turbar raya kasa ta kanta, kafin ta iya samun ci gaba mai dorewa.

Tun bayan kafuwar jamhuriyar jama’ar kasar Sin a shekarar 1949, kasar ta nace da zama karkashin mulkin jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, da turbar tsarin gurguzu mai halayyar musamman ta Sin. Hakan a ganin kasashen yamma, wai “mulkin kama karya” ne. Sai dai sakamakon da kasar Sin ta samu karkashin turbar da ta tsara da kanta, shi ne ya haifar da ci gaban tattalin arzikinta.

Wanimasani a kasar Afirka ya taba bayyana cewa, “ Jimillar GDPn kasar Kenya ta fi ta kasar Sin yawa, a shekarar 1961. Amma zuwa shekarar 2020, GDPn Kenya ya karu da ninki 3, yayin da jimillar ta kasar Sin ta karu da ninki 50.” Kalamansa sun shaida cewa, turbar da kasar Sin ta zaba, ita ce daidai.

Labarai Masu Nasaba

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

Cikin shekaru 5 da suka wuce, duniyarmu ta yi fama da koma bayan tattalin arziki. Inda aka fuskanci tarin kalubaloli, da tsanantar rikici tsakanin wasu kasashe, ko tsakanin al’ummomin wata kasa.

Amma kasar Sin tana bin hanyarta ta neman ci gaba yadda ya kamata. Wasu abubuwan da na gani da ido su ne: Mazauna kauyuka sun samu wadata ta hanyar raya harkar yawon shakatawa, ko kuma tallata amfanin gona ta kafar Internet.

Yayin da a cikin birane, ana samun karin itatuwa da bishiyoyi, da kyautatuwar muhallin zama. Kana ‘yan saman jannatin kasar Sin suna zirga-zirga a sararin samaniya ta cikin kumbunan kasar.

Ban da wannan kuma, kasar ta yi nasarar shawo kan yaduwar cutar COVID-19, da maido da ayyuka masu alaka da tattalin arziki cikin sauri. Haka zalika, a yankin Hong Kong na kasar, kasar Amurka ta ci tura a yunkurin na ta da tarzoma, da juyin juya hali, inda aka maido da kwanciyar hankali a yankin, bisa matakan shari’a da kasar Sin ta dauka.

Ban da wannan kuma, na ga yadda kasar Sin ta iya kare cikakkun yankunanta daga kasar da take nuna fin karfi a duniya. Kana abu mai muhimmanci shi ne, na ga yadda Sinawa suke nuna cikakken imani kan turbarsu, inda ko da yake suna kokarin tinkarar matakan wasu kasashe na neman shafawa kasar Sin bakin fenti, da hana ta samun ci gaba, a hannu guda kuma suna nacewa kan akidar al’ummar dan Adam mai makomar bai daya, da hadin gwiwa don moriyar dukkan bangarori.

Hausawa su kan ce, “Ko wace kwarya tana da abokin burminta”, kana “ Kayan aro ba ya rufe katara.” Idan mun ce kasar Sin na da wani asiri na raya kai, to wannan shi ne zabin turbar da ta dace da yanayin kasa, da kokarin tabbatar da kwanciyar hankali, gami da raya tattalin arziki.

Idan al’ummar wata kasa suna iya kiyaye wani yanayi na hadin kai da juna, a kokarin raya kasarsu, ba tare da ta da zaune-tsaye ba, to, duk wani kalubale, ba zai iya hana kasar samun ci gaba ba. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kwamishinan Tambuwal Ya Sauya Sheka Daga PDP Zuwa APC

Next Post

Giwa Ta Halaka Tsohuwa, Ta Sake Bin Gawarta Ta Tattake Ana Tsaka Da Jana’izarta

Related

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu
Daga Birnin Sin

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

20 minutes ago
Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya
Daga Birnin Sin

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

1 hour ago
In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba
Daga Birnin Sin

In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba

19 hours ago
Sin Za Ta Gaggauta Aikin Raya Sana’o’in Samar Da Wutar Lantarki Daga Zafin Rana
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Gaggauta Aikin Raya Sana’o’in Samar Da Wutar Lantarki Daga Zafin Rana

19 hours ago
Shugaban Kwamitin AU: Kasar Sin Aminiya Ce Da Za A Iya Dogaro Da Ita
Daga Birnin Sin

Shugaban Kwamitin AU: Kasar Sin Aminiya Ce Da Za A Iya Dogaro Da Ita

20 hours ago
Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin

21 hours ago
Next Post
Giwa Ta Halaka Tsohuwa, Ta Sake Bin Gawarta Ta Tattake Ana Tsaka Da Jana’izarta

Giwa Ta Halaka Tsohuwa, Ta Sake Bin Gawarta Ta Tattake Ana Tsaka Da Jana'izarta

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

July 5, 2025
Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

July 5, 2025
Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

July 5, 2025
Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

July 5, 2025
Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

July 5, 2025
ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

July 5, 2025
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

July 5, 2025
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

July 5, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

July 5, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.