ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Wace Kwarya Tana Da Abokin Burminta

by CMG Hausa
4 years ago
Kwarya

A kwanakin baya, na zanta da wasu masana a yayin wani taro da ya gudana a birnin Beijing, karkashin laimar dandalin masanan Sin da Afirka, inda kalaman da wani masani dan kasar Habasha mai suna Yonas Adaye ya yi, ya burge ni matuka.

Ya ce, “sakamakon bambancin al’adu da tarihi, ba za samu wani tsarin raya kasa da zai biya bukatun dukkan kasashe ba. Wasu kasashen yamma na ganin cewa, ‘Ba za a samu nasarar tafiyar da harkokin mulki ba, idan ba a rungumi tsarinmu ba.’

  • Kasuwanci Bangaren Da Ba Na Masana’Antun Kira Ba A Sin Ya Ci Gaba Da Farfadowa A Watan A Yuli

Amma kasashen Afirka ba za su ci gaba da amincewa da ra’ayinsu ba.” Na yarda da ra’ayin masanin. Saboda idan muka nazarci fasahohin da kasar Sin ta samu, to, dole ne duk wata kasa mai tasowa ta yi kokarin bin turbar raya kasa ta kanta, kafin ta iya samun ci gaba mai dorewa.

ADVERTISEMENT

Tun bayan kafuwar jamhuriyar jama’ar kasar Sin a shekarar 1949, kasar ta nace da zama karkashin mulkin jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, da turbar tsarin gurguzu mai halayyar musamman ta Sin. Hakan a ganin kasashen yamma, wai “mulkin kama karya” ne. Sai dai sakamakon da kasar Sin ta samu karkashin turbar da ta tsara da kanta, shi ne ya haifar da ci gaban tattalin arzikinta.

Wanimasani a kasar Afirka ya taba bayyana cewa, “ Jimillar GDPn kasar Kenya ta fi ta kasar Sin yawa, a shekarar 1961. Amma zuwa shekarar 2020, GDPn Kenya ya karu da ninki 3, yayin da jimillar ta kasar Sin ta karu da ninki 50.” Kalamansa sun shaida cewa, turbar da kasar Sin ta zaba, ita ce daidai.

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cikin shekaru 5 da suka wuce, duniyarmu ta yi fama da koma bayan tattalin arziki. Inda aka fuskanci tarin kalubaloli, da tsanantar rikici tsakanin wasu kasashe, ko tsakanin al’ummomin wata kasa.

Amma kasar Sin tana bin hanyarta ta neman ci gaba yadda ya kamata. Wasu abubuwan da na gani da ido su ne: Mazauna kauyuka sun samu wadata ta hanyar raya harkar yawon shakatawa, ko kuma tallata amfanin gona ta kafar Internet.

Yayin da a cikin birane, ana samun karin itatuwa da bishiyoyi, da kyautatuwar muhallin zama. Kana ‘yan saman jannatin kasar Sin suna zirga-zirga a sararin samaniya ta cikin kumbunan kasar.

Ban da wannan kuma, kasar ta yi nasarar shawo kan yaduwar cutar COVID-19, da maido da ayyuka masu alaka da tattalin arziki cikin sauri. Haka zalika, a yankin Hong Kong na kasar, kasar Amurka ta ci tura a yunkurin na ta da tarzoma, da juyin juya hali, inda aka maido da kwanciyar hankali a yankin, bisa matakan shari’a da kasar Sin ta dauka.

Ban da wannan kuma, na ga yadda kasar Sin ta iya kare cikakkun yankunanta daga kasar da take nuna fin karfi a duniya. Kana abu mai muhimmanci shi ne, na ga yadda Sinawa suke nuna cikakken imani kan turbarsu, inda ko da yake suna kokarin tinkarar matakan wasu kasashe na neman shafawa kasar Sin bakin fenti, da hana ta samun ci gaba, a hannu guda kuma suna nacewa kan akidar al’ummar dan Adam mai makomar bai daya, da hadin gwiwa don moriyar dukkan bangarori.

Hausawa su kan ce, “Ko wace kwarya tana da abokin burminta”, kana “ Kayan aro ba ya rufe katara.” Idan mun ce kasar Sin na da wani asiri na raya kai, to wannan shi ne zabin turbar da ta dace da yanayin kasa, da kokarin tabbatar da kwanciyar hankali, gami da raya tattalin arziki.

Idan al’ummar wata kasa suna iya kiyaye wani yanayi na hadin kai da juna, a kokarin raya kasarsu, ba tare da ta da zaune-tsaye ba, to, duk wani kalubale, ba zai iya hana kasar samun ci gaba ba. (Bello Wang)

Kwarya
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
Daga Birnin Sin

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
Daga Birnin Sin

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
Daga Birnin Sin

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Next Post
Giwa Ta Halaka Tsohuwa, Ta Sake Bin Gawarta Ta Tattake Ana Tsaka Da Jana’izarta

Giwa Ta Halaka Tsohuwa, Ta Sake Bin Gawarta Ta Tattake Ana Tsaka Da Jana'izarta

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.