ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Wace Kwarya Tana Da Abokin Burminta

by CMG Hausa
4 years ago
Kwarya

A kwanakin baya, na zanta da wasu masana a yayin wani taro da ya gudana a birnin Beijing, karkashin laimar dandalin masanan Sin da Afirka, inda kalaman da wani masani dan kasar Habasha mai suna Yonas Adaye ya yi, ya burge ni matuka.

Ya ce, “sakamakon bambancin al’adu da tarihi, ba za samu wani tsarin raya kasa da zai biya bukatun dukkan kasashe ba. Wasu kasashen yamma na ganin cewa, ‘Ba za a samu nasarar tafiyar da harkokin mulki ba, idan ba a rungumi tsarinmu ba.’

  • Kasuwanci Bangaren Da Ba Na Masana’Antun Kira Ba A Sin Ya Ci Gaba Da Farfadowa A Watan A Yuli

Amma kasashen Afirka ba za su ci gaba da amincewa da ra’ayinsu ba.” Na yarda da ra’ayin masanin. Saboda idan muka nazarci fasahohin da kasar Sin ta samu, to, dole ne duk wata kasa mai tasowa ta yi kokarin bin turbar raya kasa ta kanta, kafin ta iya samun ci gaba mai dorewa.

ADVERTISEMENT

Tun bayan kafuwar jamhuriyar jama’ar kasar Sin a shekarar 1949, kasar ta nace da zama karkashin mulkin jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, da turbar tsarin gurguzu mai halayyar musamman ta Sin. Hakan a ganin kasashen yamma, wai “mulkin kama karya” ne. Sai dai sakamakon da kasar Sin ta samu karkashin turbar da ta tsara da kanta, shi ne ya haifar da ci gaban tattalin arzikinta.

Wanimasani a kasar Afirka ya taba bayyana cewa, “ Jimillar GDPn kasar Kenya ta fi ta kasar Sin yawa, a shekarar 1961. Amma zuwa shekarar 2020, GDPn Kenya ya karu da ninki 3, yayin da jimillar ta kasar Sin ta karu da ninki 50.” Kalamansa sun shaida cewa, turbar da kasar Sin ta zaba, ita ce daidai.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

Cikin shekaru 5 da suka wuce, duniyarmu ta yi fama da koma bayan tattalin arziki. Inda aka fuskanci tarin kalubaloli, da tsanantar rikici tsakanin wasu kasashe, ko tsakanin al’ummomin wata kasa.

Amma kasar Sin tana bin hanyarta ta neman ci gaba yadda ya kamata. Wasu abubuwan da na gani da ido su ne: Mazauna kauyuka sun samu wadata ta hanyar raya harkar yawon shakatawa, ko kuma tallata amfanin gona ta kafar Internet.

Yayin da a cikin birane, ana samun karin itatuwa da bishiyoyi, da kyautatuwar muhallin zama. Kana ‘yan saman jannatin kasar Sin suna zirga-zirga a sararin samaniya ta cikin kumbunan kasar.

Ban da wannan kuma, kasar ta yi nasarar shawo kan yaduwar cutar COVID-19, da maido da ayyuka masu alaka da tattalin arziki cikin sauri. Haka zalika, a yankin Hong Kong na kasar, kasar Amurka ta ci tura a yunkurin na ta da tarzoma, da juyin juya hali, inda aka maido da kwanciyar hankali a yankin, bisa matakan shari’a da kasar Sin ta dauka.

Ban da wannan kuma, na ga yadda kasar Sin ta iya kare cikakkun yankunanta daga kasar da take nuna fin karfi a duniya. Kana abu mai muhimmanci shi ne, na ga yadda Sinawa suke nuna cikakken imani kan turbarsu, inda ko da yake suna kokarin tinkarar matakan wasu kasashe na neman shafawa kasar Sin bakin fenti, da hana ta samun ci gaba, a hannu guda kuma suna nacewa kan akidar al’ummar dan Adam mai makomar bai daya, da hadin gwiwa don moriyar dukkan bangarori.

Hausawa su kan ce, “Ko wace kwarya tana da abokin burminta”, kana “ Kayan aro ba ya rufe katara.” Idan mun ce kasar Sin na da wani asiri na raya kai, to wannan shi ne zabin turbar da ta dace da yanayin kasa, da kokarin tabbatar da kwanciyar hankali, gami da raya tattalin arziki.

Idan al’ummar wata kasa suna iya kiyaye wani yanayi na hadin kai da juna, a kokarin raya kasarsu, ba tare da ta da zaune-tsaye ba, to, duk wani kalubale, ba zai iya hana kasar samun ci gaba ba. (Bello Wang)

Kwarya
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
Giwa Ta Halaka Tsohuwa, Ta Sake Bin Gawarta Ta Tattake Ana Tsaka Da Jana’izarta

Giwa Ta Halaka Tsohuwa, Ta Sake Bin Gawarta Ta Tattake Ana Tsaka Da Jana'izarta

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.