• English
  • Business News
Thursday, October 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Zuwan Mbappe Zai Dusashe Tauraruwar Bellingham A Real Madrid?

by Abba Ibrahim Wada
1 year ago
Mbappe

Tun bayan cikar burin shugaban kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid na kawo dan wasa Kylian Mbappe, rahotanni da masu sharhi suka fara bayyana cewa magoya baya da shugabannin kungiyar za su karkatar da soyayyar da suke yi wa Jude Bellingham zuwa Mbappe, matakin da kociyan kungiyar, Carlo Ancelotti ya bayyana a matsayin shaci fadi kuma matsayin Bellingham a Real Madrid ba zai canza ba a bana, bayan daukar Kylian Mbappe.

Bellingham, dan wasan Ingila, mai shekara 21, ya taka rawar gani a Sifaniya a kakarsa ta farko, wanda ya zura kwallo 23 a wasanni 42 kuma yana cikin ‘‘yan wasan da suka taka rawar gani a Real Madrid, wacce ta lashe La Liga da Champions League a kakar da ta wuce.

  • Muna Samun Nasarori A Yaki Da Gurbatattun Masana’antar Kannywood – Tijjani Asase
  • Matasa Sun Yi Warwason Motar Taki A Adamawa

Mbappe, kyaftin din tawagar Faransa, mai shekara 25, ya koma Real Madrid a bana daga Paris St Ger-main, bayan da kwantiraginsa ya kare a watan Yuni kuma tuni ya koma Real Madrid bayan kammala gasar cin kofin Nahiyar Turai.

Ancelotti ya yi watsi da batun cewa Bellingham ba zai dinga buga gurbin da ya saba bugawa a Real Ma-drid ba, domin bai wa Mbappe dama, kociyan dan kasar Italiya ya bayyana cewa babu wani abu da zai canza a gare shi.

“Kakar farko, ya bai wa mutane mamaki, saboda yadda ya nuna kwarewa, yanzu kuma ya kara samun gogewa. Kenan wannan kakar haka zai ci gaba da taka rawar gani kuma zai ci gaba da zama fitatcen dan wasan wannan kungiya, wanda zai ci gaba da taka rawar da kungiyar za ta ci gaba da samun nasarori,” in ji Ancelotti

LABARAI MASU NASABA

Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

El Classico: Abinda Ya Kamata Ku Sani Dangane Da Wasan Barcelona Da Real Madrid

Ancelotti ya goyi da bayan Bellingham, wanda aka rika sukar kwazonsa a Euro 2024, duk da cewar Ingila ta kai wasan karshe a gasar kuma ya ce wannan ra’ayinsa ne, amma Bellingham ya taka rawar gani sosai a gasar cin kofin Zakarun Turai ta Euro 2024.

Sai dai ba iya shugabannin Real Madrid ba ne ake ganin za su mayar da Mbappe dan lele, magoya bayan kungiyar ma ana ganin za su karkata ga Mbappe, kasancewar sun dade suna fatan ganin ya koma kungiyar.

Amma ana ganin ba iya Bellingham da Mbappe bane za a samu wannan cece kucen, dan wasa Binicius ma ana ganin yana bukatar goyon bayan magoya baya da shugabanni saboda nauyin da yake kansa a kungiyar a yanzu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi
Wasanni

Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

October 28, 2025
El Classico: Abinda Ya Kamata Ku Sani Dangane Da Wasan Barcelona Da Real Madrid
Wasanni

El Classico: Abinda Ya Kamata Ku Sani Dangane Da Wasan Barcelona Da Real Madrid

October 26, 2025
Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru
Wasanni

Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

October 26, 2025
Next Post
Gwamnan kano

Gwamna Yusuf Ya Jaddada Ƙudirinsa Na Yaƙi Da Cin Hanci Da Rashawa A Kano

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

October 29, 2025
Asuu

Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU

October 29, 2025
Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

October 29, 2025
Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

October 29, 2025
An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

October 29, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Amince Da Bukatar Amso Bashin Dala Biliyan 2.34 A Kasuwar Jari Ta Duniya

October 29, 2025
An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

October 29, 2025
Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

October 29, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

October 29, 2025
COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

October 29, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.