• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kofin Afirka: Me Ya Sa Ba A Gayyaci Alkalin Wasa Daga Nijeriya Ba?

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
in Wasanni
0
Kofin Afirka: Me Ya Sa Ba A Gayyaci Alkalin Wasa Daga Nijeriya Ba?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar dake kula da kwallon kafa ta nahiyar Afirka ta CAF ta fitar da sunayen alkalan wasan da za su jagoranci yin alkalanci a gasar cin kofin nahiyar Afirka da kasar Cote d’Ivoir za ta karbi bakunci, amma babu alkalin ko guda daya daga Nijeriya.

Ana kallon Nijeriya a matsayin daya daga cikin manyan kasashen da suka fi shahara a harkar kwallon kafa a nahiyar Afirka kuma kasar da take da tasiri a nahiyar a fannoni da dama.

  • Ronaldo Ya Sake Cin Kwallo Uku Rigis A Saudiyya

Sai dai rashin daukar wani daga cikin dubunnan alkalan wasan kasar nan wata alama ce wadda take nuna cewa akwai matsaloli birjik musamman a harkokin da suka shafi wasanni a kasar nan, kuma suke bukatar daukar mataki na gaggawa.

Dalilin da ya sa ba a dauki alkalin wasa daga Nijeriya ba

 

Labarai Masu Nasaba

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

Cin Hanci Da Rashawa?

Cin hanci da rashawa dai yana daya daga cikin matsalolin da suka hana abubuwa da dama ci gaba a kasar nan ciki har da kwallon kafa inda ko a wasannin gasar firimiyar Nijeriya ma ana yawan korafi akan yadda ake samun matsalolin cin hanci da rashawa daga wajen kungiyoyi zuwa alkalan wasa.

 

Rashin Kayan Aiki Na Zamani

A yayin da aka samu ci gaba wajen saukakawa alkalan wasa ta hanyar na’urar taimaka musu wajen yanke hukunce-hukunce masu tsauri ta hanyar amfani da na’urar nan mai suna BAR, har yanzu a kasar nan ana fama da matsalolin BAR din domin hukumomi sun kasa yin abin da ya kamata wajen samar da na’urar a filayen wasannin dake fadin kasar nan.

 

Rashin Haska Gasar Firimiya Ta Nijeriya

Haska gasa yana taimaka wa wajen rage magudi, wanda kuma daman cin hanci da rashawa ne yake kawo magudin, saboda haka rashin haska wasannin gasar gaba daya shi ne yake sawa ake samun rashin tabbas a gasar, sannan suma alkalan wasan suna ganin duniya ba ta ganin su hakan yake sawa suke yin abin da suka ga dama a wajen yin alkalanci.

Hukumar kula da kwallon kafa ta Afirka, CAF ta sanya sunayen alkalan wasa 85 na sassa daban-daban, gabanin gasar cin kofin Afirka na shekara ta 2024 da kasar Cote d’Iboir za ta karbi bakunci.

Kamar yadda jerin sunayen ya fito a ranar Talata, alkalan wasan da suka fi yawa a cikin jerin sunayen sun fito ne daga kasashe biyu na Arewacin Afirka, wato Masar da Aljeriya.

A gasar da aka fafata wadda Kamaru ta karbi bakunci a baya, Samuel Pwadutakam ne dan Nijeriya daya tilo da aka saka cikin alkalan wasa 63 a gasar AFCON da ta gabata kuma shima ya je ne a matsayin mai jiran ko ta kwana.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AFCONAlkalin WasaKofin nahiyar Afirka
ShareTweetSendShare
Previous Post

Majalisar Kano Za Ta Karrama Dan Adaidaitan Da Ya Maida Wa Dan Chadi Miliyan 15 Da Ya Tsinta

Next Post

Gwamnan Bauchi Ya Kaddamar Da Aikin Hanyar Liman Katagum Zuwa Luda Zuwa Lekka Kan Biliyan 2.4

Related

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack
Wasanni

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

1 day ago
Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 
Wasanni

Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

4 days ago
Neman Gurbi: Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Afirka Ta Kudu A Bloemfontein
Wasanni

Neman Gurbi: Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Afirka Ta Kudu A Bloemfontein

4 days ago
Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana
Wasanni

Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

6 days ago
Ƴan Wasan Nijeriya Da Suka Sauya Sheka A Kasuwar Musayar Ƴan Ƙwallo Ta Bana
Wasanni

Ƴan Wasan Nijeriya Da Suka Sauya Sheka A Kasuwar Musayar Ƴan Ƙwallo Ta Bana

6 days ago
Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda
Wasanni

Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

7 days ago
Next Post
Bauchi

Gwamnan Bauchi Ya Kaddamar Da Aikin Hanyar Liman Katagum Zuwa Luda Zuwa Lekka Kan Biliyan 2.4

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

September 13, 2025
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

September 13, 2025
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

September 13, 2025
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

September 13, 2025
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.