ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kofin Afirka: Me Ya Sa Ba A Gayyaci Alkalin Wasa Daga Nijeriya Ba?

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
Kofin Afirka

Hukumar dake kula da kwallon kafa ta nahiyar Afirka ta CAF ta fitar da sunayen alkalan wasan da za su jagoranci yin alkalanci a gasar cin kofin nahiyar Afirka da kasar Cote d’Ivoir za ta karbi bakunci, amma babu alkalin ko guda daya daga Nijeriya.

Ana kallon Nijeriya a matsayin daya daga cikin manyan kasashen da suka fi shahara a harkar kwallon kafa a nahiyar Afirka kuma kasar da take da tasiri a nahiyar a fannoni da dama.

  • Ronaldo Ya Sake Cin Kwallo Uku Rigis A Saudiyya

Sai dai rashin daukar wani daga cikin dubunnan alkalan wasan kasar nan wata alama ce wadda take nuna cewa akwai matsaloli birjik musamman a harkokin da suka shafi wasanni a kasar nan, kuma suke bukatar daukar mataki na gaggawa.

ADVERTISEMENT

Dalilin da ya sa ba a dauki alkalin wasa daga Nijeriya ba

 

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

Cin Hanci Da Rashawa?

Cin hanci da rashawa dai yana daya daga cikin matsalolin da suka hana abubuwa da dama ci gaba a kasar nan ciki har da kwallon kafa inda ko a wasannin gasar firimiyar Nijeriya ma ana yawan korafi akan yadda ake samun matsalolin cin hanci da rashawa daga wajen kungiyoyi zuwa alkalan wasa.

 

Rashin Kayan Aiki Na Zamani

A yayin da aka samu ci gaba wajen saukakawa alkalan wasa ta hanyar na’urar taimaka musu wajen yanke hukunce-hukunce masu tsauri ta hanyar amfani da na’urar nan mai suna BAR, har yanzu a kasar nan ana fama da matsalolin BAR din domin hukumomi sun kasa yin abin da ya kamata wajen samar da na’urar a filayen wasannin dake fadin kasar nan.

 

Rashin Haska Gasar Firimiya Ta Nijeriya

Haska gasa yana taimaka wa wajen rage magudi, wanda kuma daman cin hanci da rashawa ne yake kawo magudin, saboda haka rashin haska wasannin gasar gaba daya shi ne yake sawa ake samun rashin tabbas a gasar, sannan suma alkalan wasan suna ganin duniya ba ta ganin su hakan yake sawa suke yin abin da suka ga dama a wajen yin alkalanci.

Hukumar kula da kwallon kafa ta Afirka, CAF ta sanya sunayen alkalan wasa 85 na sassa daban-daban, gabanin gasar cin kofin Afirka na shekara ta 2024 da kasar Cote d’Iboir za ta karbi bakunci.

Kamar yadda jerin sunayen ya fito a ranar Talata, alkalan wasan da suka fi yawa a cikin jerin sunayen sun fito ne daga kasashe biyu na Arewacin Afirka, wato Masar da Aljeriya.

A gasar da aka fafata wadda Kamaru ta karbi bakunci a baya, Samuel Pwadutakam ne dan Nijeriya daya tilo da aka saka cikin alkalan wasa 63 a gasar AFCON da ta gabata kuma shima ya je ne a matsayin mai jiran ko ta kwana.

Kofin Afirka
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Yaushe Za A Fara Kofin Zakarun Turai
  • Abba Ibrahim Wada
    Messi Ya Yi Ritaya A Argentina: Da Me Za Mu Iya Tuna Gwarzon Duniyar?
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye ‘Yan wasan Nijeriya Da Za Su Buga Gasar Firimiyar Ingila Ta Bana?
  • Abba Ibrahim Wada
    Chelsea A Ƙarƙashin Xavi Alonso

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana
Wasanni

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

September 8, 2026
Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain
Wasanni

Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain

September 7, 2026
Next Post
Bauchi

Gwamnan Bauchi Ya Kaddamar Da Aikin Hanyar Liman Katagum Zuwa Luda Zuwa Lekka Kan Biliyan 2.4

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.