ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kofin Afirka: Me Ya Sa Ba A Gayyaci Alkalin Wasa Daga Nijeriya Ba?

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
Kofin Afirka

Hukumar dake kula da kwallon kafa ta nahiyar Afirka ta CAF ta fitar da sunayen alkalan wasan da za su jagoranci yin alkalanci a gasar cin kofin nahiyar Afirka da kasar Cote d’Ivoir za ta karbi bakunci, amma babu alkalin ko guda daya daga Nijeriya.

Ana kallon Nijeriya a matsayin daya daga cikin manyan kasashen da suka fi shahara a harkar kwallon kafa a nahiyar Afirka kuma kasar da take da tasiri a nahiyar a fannoni da dama.

  • Ronaldo Ya Sake Cin Kwallo Uku Rigis A Saudiyya

Sai dai rashin daukar wani daga cikin dubunnan alkalan wasan kasar nan wata alama ce wadda take nuna cewa akwai matsaloli birjik musamman a harkokin da suka shafi wasanni a kasar nan, kuma suke bukatar daukar mataki na gaggawa.

ADVERTISEMENT

Dalilin da ya sa ba a dauki alkalin wasa daga Nijeriya ba

 

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Cin Hanci Da Rashawa?

Cin hanci da rashawa dai yana daya daga cikin matsalolin da suka hana abubuwa da dama ci gaba a kasar nan ciki har da kwallon kafa inda ko a wasannin gasar firimiyar Nijeriya ma ana yawan korafi akan yadda ake samun matsalolin cin hanci da rashawa daga wajen kungiyoyi zuwa alkalan wasa.

 

Rashin Kayan Aiki Na Zamani

A yayin da aka samu ci gaba wajen saukakawa alkalan wasa ta hanyar na’urar taimaka musu wajen yanke hukunce-hukunce masu tsauri ta hanyar amfani da na’urar nan mai suna BAR, har yanzu a kasar nan ana fama da matsalolin BAR din domin hukumomi sun kasa yin abin da ya kamata wajen samar da na’urar a filayen wasannin dake fadin kasar nan.

 

Rashin Haska Gasar Firimiya Ta Nijeriya

Haska gasa yana taimaka wa wajen rage magudi, wanda kuma daman cin hanci da rashawa ne yake kawo magudin, saboda haka rashin haska wasannin gasar gaba daya shi ne yake sawa ake samun rashin tabbas a gasar, sannan suma alkalan wasan suna ganin duniya ba ta ganin su hakan yake sawa suke yin abin da suka ga dama a wajen yin alkalanci.

Hukumar kula da kwallon kafa ta Afirka, CAF ta sanya sunayen alkalan wasa 85 na sassa daban-daban, gabanin gasar cin kofin Afirka na shekara ta 2024 da kasar Cote d’Iboir za ta karbi bakunci.

Kamar yadda jerin sunayen ya fito a ranar Talata, alkalan wasan da suka fi yawa a cikin jerin sunayen sun fito ne daga kasashe biyu na Arewacin Afirka, wato Masar da Aljeriya.

A gasar da aka fafata wadda Kamaru ta karbi bakunci a baya, Samuel Pwadutakam ne dan Nijeriya daya tilo da aka saka cikin alkalan wasa 63 a gasar AFCON da ta gabata kuma shima ya je ne a matsayin mai jiran ko ta kwana.

Kofin Afirka
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Kasan ‘Yanwasan Da Za Su Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe?
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Ta Samu Lambobin Yabo 16 A Wasannin Tseren Keke
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Za Ta Karbi Bakuncin Babban Taron Hukumar CAF Na Bana
  • Abba Ibrahim Wada
    Shin Ko Arsenal Za Ta Mamaye Duniya?

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya
Wasanni

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa
Wasanni

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

June 2, 2026
Next Post
Bauchi

Gwamnan Bauchi Ya Kaddamar Da Aikin Hanyar Liman Katagum Zuwa Luda Zuwa Lekka Kan Biliyan 2.4

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.