ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kofin Afirka: Me Ya Sa Ba A Gayyaci Alkalin Wasa Daga Nijeriya Ba?

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
Kofin Afirka

Hukumar dake kula da kwallon kafa ta nahiyar Afirka ta CAF ta fitar da sunayen alkalan wasan da za su jagoranci yin alkalanci a gasar cin kofin nahiyar Afirka da kasar Cote d’Ivoir za ta karbi bakunci, amma babu alkalin ko guda daya daga Nijeriya.

Ana kallon Nijeriya a matsayin daya daga cikin manyan kasashen da suka fi shahara a harkar kwallon kafa a nahiyar Afirka kuma kasar da take da tasiri a nahiyar a fannoni da dama.

  • Ronaldo Ya Sake Cin Kwallo Uku Rigis A Saudiyya

Sai dai rashin daukar wani daga cikin dubunnan alkalan wasan kasar nan wata alama ce wadda take nuna cewa akwai matsaloli birjik musamman a harkokin da suka shafi wasanni a kasar nan, kuma suke bukatar daukar mataki na gaggawa.

ADVERTISEMENT

Dalilin da ya sa ba a dauki alkalin wasa daga Nijeriya ba

 

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

Cin Hanci Da Rashawa?

Cin hanci da rashawa dai yana daya daga cikin matsalolin da suka hana abubuwa da dama ci gaba a kasar nan ciki har da kwallon kafa inda ko a wasannin gasar firimiyar Nijeriya ma ana yawan korafi akan yadda ake samun matsalolin cin hanci da rashawa daga wajen kungiyoyi zuwa alkalan wasa.

 

Rashin Kayan Aiki Na Zamani

A yayin da aka samu ci gaba wajen saukakawa alkalan wasa ta hanyar na’urar taimaka musu wajen yanke hukunce-hukunce masu tsauri ta hanyar amfani da na’urar nan mai suna BAR, har yanzu a kasar nan ana fama da matsalolin BAR din domin hukumomi sun kasa yin abin da ya kamata wajen samar da na’urar a filayen wasannin dake fadin kasar nan.

 

Rashin Haska Gasar Firimiya Ta Nijeriya

Haska gasa yana taimaka wa wajen rage magudi, wanda kuma daman cin hanci da rashawa ne yake kawo magudin, saboda haka rashin haska wasannin gasar gaba daya shi ne yake sawa ake samun rashin tabbas a gasar, sannan suma alkalan wasan suna ganin duniya ba ta ganin su hakan yake sawa suke yin abin da suka ga dama a wajen yin alkalanci.

Hukumar kula da kwallon kafa ta Afirka, CAF ta sanya sunayen alkalan wasa 85 na sassa daban-daban, gabanin gasar cin kofin Afirka na shekara ta 2024 da kasar Cote d’Iboir za ta karbi bakunci.

Kamar yadda jerin sunayen ya fito a ranar Talata, alkalan wasan da suka fi yawa a cikin jerin sunayen sun fito ne daga kasashe biyu na Arewacin Afirka, wato Masar da Aljeriya.

A gasar da aka fafata wadda Kamaru ta karbi bakunci a baya, Samuel Pwadutakam ne dan Nijeriya daya tilo da aka saka cikin alkalan wasa 63 a gasar AFCON da ta gabata kuma shima ya je ne a matsayin mai jiran ko ta kwana.

Kofin Afirka
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
  • Abba Ibrahim Wada
    FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa
  • Abba Ibrahim Wada
    Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

MASU ALAKA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino
Wasanni

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya
Wasanni

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

June 22, 2026
Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
Wasanni

Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

June 21, 2026
Next Post
Bauchi

Gwamnan Bauchi Ya Kaddamar Da Aikin Hanyar Liman Katagum Zuwa Luda Zuwa Lekka Kan Biliyan 2.4

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.