• English
  • Business News
Saturday, September 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kofin Duniya 2026: Kasashen Da Suka Samu Tikitin Shiga Gasar Zuwa Yanzu

by Abba Ibrahim Wada
6 months ago
in Wasanni
0
Kofin Duniya 2026: Kasashen Da Suka Samu Tikitin Shiga Gasar Zuwa Yanzu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kasashe hudu ne suka samu gurbin shiga gasar cin kofin duniya na shekarar 2026 da za a buga a kasashe uku da su ka hada da Canada da Medico da kuma Amurka, gasar cin kofin duniya ta 2026, wadda za a yi a ranar 11 ga Yuni zuwa 19 ga Yuli, 2026, ita ce gasar karo na 23 kuma za ta kasance gasar cin kofin duniya ta farko da kasashe uku za su karvi bakuncinta.  

Wani gagarumin sauyi ga wannan gasa shi ne fadada yawan adadin kasashen da za su buga daga kasashe 32 zuwa 48, mahukuntan hukumar kwallon kafa ta FIFA ne su ka yanke wannan hukunci a bara, yayin da shekarun baya da su ka gabata kasashe 32 ne ke buga gasar Kofin Duniya amma yanzu FIFA ta kara kasashe 16.

  • Jami’in Sin: Ba Za A Lamunci Ayyukan ‘Yan Aware Na “Ballewar Taiwan” Ta Ko Wace Hanya Ba
  • Juma Bah: Balladolid Za Ta Kai Manchester City Kara Gaban Kotu

Tawagar farko da ta samu gurbin zuwa kasashen da ke karvar bakuncin ita ce Kasar Japan, Kasar Japan ta samu gurbin shiga gasar cin kofin duniya ta FIFA a shekarar 2026, inda ta zama kasa ta farko a wajen kasashen da suka karvi bakuncin gasar.

Nasarar da suka yi a kan Bahrain da ci 2-0 a ranar Alhamis 20 ga watan Maris, ya sa su ka samu wannan nasara ta fara zuwa kofin Duniya na shekarar 2026, a ranar 24 ga Maris, 2025, New Zealand ta samu gurbin shiga gasar cin kofin duniya ta FIFA 2026, bayan da ta doke New Caledonia da ci 3-0, sai kasar Argentina wadda ta lashe kofin karshe na gasar Kofin Duniya da aka buga a kasar Katar a shekarar 2022, ita ma ta samu wannan nasara ta zuwa Kofin Duniya ne bayan ta doke kasar Brazil da ci 4-1 a Buines Aires.

Hakazalika kasar Iran ta samu tikitin shiga gasar cin kofin duniya ta FIFA 2026 a ranar Talata 25 ga Maris, 2025, sun samu hakan ne bayan da suka tashi kunnen doki 2-2 da kasar Uzbekistan a wasan neman tikitin shiga gasar cin kofin nahiyar Asiya, inda Mehdi Taremi ya zura wa Iran kwallayen biyu a wasan da suka tashi canjaras, wanda hakan ya ishe su hujja a wasan karshe.

Labarai Masu Nasaba

Saliba Ya Sabunta Kwantiraginsa Da Arsenal Har Tsawon Shekaru 5

An Kama Tsohon Ɗan Wasan Super Eagles, Victor Ezeji, Kan Zargin Aikata Zambar ₦39.8m

Ya zuwa yanzu dai ga kasashen da suka samu tikitin shiga gasar cin kofin duniya ta 2026.

1. Japan(Asia). 2. New Zealand (Oceania). 3. Iran (Asia). 4. Argentina (Kudancin Amurka). 5. Kanada (Masu Masaukin Baki). 6. Meziko (Masu Masaukin Baki). 7. Amurka (Masu Masaukin Baki).


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DuniyaKasashe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Duk Da Matsin Tattalin Arziki, Bukukuwan Sallar Bana Ta Yi Armashi

Next Post

Ba Rabo Da Gwani Ba: Abdullahi Karkuzu 1931-2025

Related

Saliba Ya Sabunta Kwantiraginsa Da Arsenal Har Tsawon Shekaru 5
Wasanni

Saliba Ya Sabunta Kwantiraginsa Da Arsenal Har Tsawon Shekaru 5

1 day ago
An Kama Tsohon Ɗan Wasan Super Eagles, Victor Ezeji, Kan Zargin Aikata Zambar ₦39.8m
Wasanni

An Kama Tsohon Ɗan Wasan Super Eagles, Victor Ezeji, Kan Zargin Aikata Zambar ₦39.8m

3 days ago
Gavi Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Yi Masa Tiyata
Wasanni

Gavi Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Yi Masa Tiyata

3 days ago
Yadda Aka Bai Wa Ousmane Dembélé Kyautar Ballon d’Or Ta 2025
Manyan Labarai

Yadda Aka Bai Wa Ousmane Dembélé Kyautar Ballon d’Or Ta 2025

4 days ago
Jadawalin ‘Yan Wasa 30 Na Farko A Kyautar Ballon D’or Ta Bana
Manyan Labarai

Jadawalin ‘Yan Wasa 30 Na Farko A Kyautar Ballon D’or Ta Bana

4 days ago
Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan Arsenal Da Manchester City 
Wasanni

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan Arsenal Da Manchester City 

5 days ago
Next Post
Ba Rabo Da Gwani Ba: Abdullahi Karkuzu 1931-2025

Ba Rabo Da Gwani Ba: Abdullahi Karkuzu 1931-2025

LABARAI MASU NASABA

Ana Fatan Majalisar Wakilan Amurka Za Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Raya Hadin Gwiwar Sin Da Amurka

Ana Fatan Majalisar Wakilan Amurka Za Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Raya Hadin Gwiwar Sin Da Amurka

September 26, 2025
2027: Abubuwan Da Jam’iyyun Siyasar Nijeriya Ke Tsammanin Samu Daga Sabon Shugaban INEC

2027: Abubuwan Da Jam’iyyun Siyasar Nijeriya Ke Tsammanin Samu Daga Sabon Shugaban INEC

September 26, 2025
Jerin Tattaunawa Ta Musamman Da CMG Ya Gudanar Sun Maida Hankali Kan GGI

Jerin Tattaunawa Ta Musamman Da CMG Ya Gudanar Sun Maida Hankali Kan GGI

September 26, 2025
’Yansanda Sun Kama ‘Yan Fashi A Kaduna, Sun Ƙwato Bindiga Da Wayoyi

’Yansanda Sun Kama ‘Yan Fashi A Kaduna, Sun Ƙwato Bindiga Da Wayoyi

September 26, 2025
Nazari Kan Littafin Baba Zube Na 5 (Gwamnati)

Nazari Kan Littafin Baba Zube Na 5 (Gwamnati)

September 26, 2025
A Karo Na Hudu ’Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Yi Nasarar Kammala Ayyukansu A Wajen Kumbon

A Karo Na Hudu ’Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Yi Nasarar Kammala Ayyukansu A Wajen Kumbon

September 26, 2025
Katsina Za Ta Ɗauki Nauyin Karatun Mahaddata Alƙur’ani – Gwamna Radda

Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina: Nasara Ko Matsala?

September 26, 2025
Kasar Sin Na Farin Cikin Ganin Kamfanoni Suna Gudanar Da Shawarwarin Kasuwanci Da Kyau Bisa Ka’idojin Kasuwa

Kasar Sin Na Farin Cikin Ganin Kamfanoni Suna Gudanar Da Shawarwarin Kasuwanci Da Kyau Bisa Ka’idojin Kasuwa

September 26, 2025
An Gano Cututtuka Uku Da Suka Ta Da Hankalin Hukumomin Lafiya A Nijeriya

An Gano Cututtuka Uku Da Suka Ta Da Hankalin Hukumomin Lafiya A Nijeriya

September 26, 2025
Kasar Sin Ta Yi Alkawarin Bayar Da Sabuwar Gudummawa Dangane Da Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya

Kasar Sin Ta Yi Alkawarin Bayar Da Sabuwar Gudummawa Dangane Da Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya

September 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.