• English
  • Business News
Sunday, October 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kofin Duniya 2026: Kasashen Da Suka Samu Tikitin Shiga Gasar Zuwa Yanzu

by Abba Ibrahim Wada
7 months ago
Duniya

Kasashe hudu ne suka samu gurbin shiga gasar cin kofin duniya na shekarar 2026 da za a buga a kasashe uku da su ka hada da Canada da Medico da kuma Amurka, gasar cin kofin duniya ta 2026, wadda za a yi a ranar 11 ga Yuni zuwa 19 ga Yuli, 2026, ita ce gasar karo na 23 kuma za ta kasance gasar cin kofin duniya ta farko da kasashe uku za su karvi bakuncinta.  

Wani gagarumin sauyi ga wannan gasa shi ne fadada yawan adadin kasashen da za su buga daga kasashe 32 zuwa 48, mahukuntan hukumar kwallon kafa ta FIFA ne su ka yanke wannan hukunci a bara, yayin da shekarun baya da su ka gabata kasashe 32 ne ke buga gasar Kofin Duniya amma yanzu FIFA ta kara kasashe 16.

  • Jami’in Sin: Ba Za A Lamunci Ayyukan ‘Yan Aware Na “Ballewar Taiwan” Ta Ko Wace Hanya Ba
  • Juma Bah: Balladolid Za Ta Kai Manchester City Kara Gaban Kotu

Tawagar farko da ta samu gurbin zuwa kasashen da ke karvar bakuncin ita ce Kasar Japan, Kasar Japan ta samu gurbin shiga gasar cin kofin duniya ta FIFA a shekarar 2026, inda ta zama kasa ta farko a wajen kasashen da suka karvi bakuncin gasar.

Nasarar da suka yi a kan Bahrain da ci 2-0 a ranar Alhamis 20 ga watan Maris, ya sa su ka samu wannan nasara ta fara zuwa kofin Duniya na shekarar 2026, a ranar 24 ga Maris, 2025, New Zealand ta samu gurbin shiga gasar cin kofin duniya ta FIFA 2026, bayan da ta doke New Caledonia da ci 3-0, sai kasar Argentina wadda ta lashe kofin karshe na gasar Kofin Duniya da aka buga a kasar Katar a shekarar 2022, ita ma ta samu wannan nasara ta zuwa Kofin Duniya ne bayan ta doke kasar Brazil da ci 4-1 a Buines Aires.

Hakazalika kasar Iran ta samu tikitin shiga gasar cin kofin duniya ta FIFA 2026 a ranar Talata 25 ga Maris, 2025, sun samu hakan ne bayan da suka tashi kunnen doki 2-2 da kasar Uzbekistan a wasan neman tikitin shiga gasar cin kofin nahiyar Asiya, inda Mehdi Taremi ya zura wa Iran kwallayen biyu a wasan da suka tashi canjaras, wanda hakan ya ishe su hujja a wasan karshe.

LABARAI MASU NASABA

Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

Gwarzon Mai Koyar Da Wasanni Na Shekarar 2025 Justine Madugu

Ya zuwa yanzu dai ga kasashen da suka samu tikitin shiga gasar cin kofin duniya ta 2026.

1. Japan(Asia). 2. New Zealand (Oceania). 3. Iran (Asia). 4. Argentina (Kudancin Amurka). 5. Kanada (Masu Masaukin Baki). 6. Meziko (Masu Masaukin Baki). 7. Amurka (Masu Masaukin Baki).

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru
Wasanni

Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

October 26, 2025
Gwarzon Mai Koyar Da Wasanni Na Shekarar 2025 Justine Madugu
Manyan Labarai

Gwarzon Mai Koyar Da Wasanni Na Shekarar 2025 Justine Madugu

October 25, 2025
Zuwan Tsoffin ’Yan Wasan Barcelona Abuja Ya Nuna Ana Samun Zaman Lafiya A Nijeriya – Matawalle
Wasanni

Zuwan Tsoffin ’Yan Wasan Barcelona Abuja Ya Nuna Ana Samun Zaman Lafiya A Nijeriya – Matawalle

October 25, 2025
Next Post
Ba Rabo Da Gwani Ba: Abdullahi Karkuzu 1931-2025

Ba Rabo Da Gwani Ba: Abdullahi Karkuzu 1931-2025

LABARAI MASU NASABA

Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa

Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa

October 26, 2025
Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

October 26, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Kama Wasu Mutum Biyu Da Ake Zargi Da Haɗa Baki Da ‘Yan Bindiga A Kano

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwamnatin Kaduna Tare Da  AUDA–NEPAD Sun Tallafa Wa Manoma 400 Da Kayan Noma

October 26, 2025
Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

October 26, 2025
Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Ɗan Majalisa Na Shekarar 2025: Benjamin Okezie Kalu

October 26, 2025
An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.