ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Rabo Da Gwani Ba: Abdullahi Karkuzu 1931-2025

by Rabilu Sanusi Bena
1 year ago
Abdullahi

Da yammacin ranar Talata 25 ga watan Maris na shekarar 2025, Allah ya yi wa shahararren jarumi kuma dattijo a masana’antar fina-finan Hausa Abdullahi Shuaibu (Karkuzu) rasuwa, ya rasu bayan shafe tsawon lokaci ya na jinya a asibitin koyarwa ta Jami’ar Jos, Karkuzu ya rasu ya na da shekara 94 a duniya inda ya bar ‘ya’ya shida da mata daya.

An yi jana’izar sa da safiyar ranar Laraba 26 ga watan Maris na shekarar 2025 a gidansa da ke Haruna Hadeja Street, cikin garin Jos, Jihar Filato, ‘yan fim da dama sun yi alhinin rashin sa, sun kuma yi addu’ar Allah ya jikan sa, ya ba iyalin sa hakurin jure wannan babban rashin.

  • Kasafin Kudi Na 2025: Kowanne Ɗan Ƙasa Ɗaya Zai Kashe Ƙasa Da $2.15 – Rahoto
  • Me Ya Sa Fina-finai Masu dogon Zango A Masana’antar kannywood ke Zama Cin kwan Makauniya?

Karkuzu dai dan wasan kwaikwayo ne wanda ya yi tashe a wajen masu kallon wasan talabijin na ‘Karkuzu’ a shekarun 1980, a wasan yakan yi wa kan sa kirari da, “Ni ne Karkuzu, dan Kurmuzuzu, jikan Kuzu na Bodara, abar ni sai ta Allah ya yi”, dattijon kafin rasuwarsa ya shafe shekara 43 a masana’antar wasan kwaikwayo, kafin rashin lafiya ya sa ya daina.

ADVERTISEMENT

A cikin watan Agustan shekarar 2023 ya bayyana a shafukan sada zumunta inda aka gan shi ya na neman taimako a wajen al’umma da abokan sana’arsu ta fim, saboda abin da ya kira kuncin rayuwa da yake ciki a wancan lokacin, saboda yanayin rayuwa inda har ya yi kira ga jama’a da su kai masa dauki.

A wancan lokacin Karkuzu ya samu matsalar gani inda har ta kai ga ya rasa idanunsa duka biyun, bugu da kari ya bayyana cewar bayan rashin abincin da zai ci ga kuma rashin muhallin zama saboda a wancan lokacin ya ce baya da gidan kanshi da zai zauna, Karkuzu ya yi bayanin ne a wata hira da yayi da TRT Hausa a shekarar 2023.

LABARAI MASU NASABA

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

A yayin hirar Abdullahi Shuaibu ya ce “Ni dai suna na Abdullahi Shuaibu, amma al’uma na kirana da Karkuzu, ko kuma Abdullahi Kano, yanzu shekaru 43 kenan ina wannan harka ta fina finan Hausa, amma yanzu wasu lokutan sai in kwana ba ni da abin da za a ci a gida na, kuma wani abin tausayi, ni Karkuzu a yanzu zancen da na ke, wannan gida da nake ciki an sa shi a kasuwa, ba gida na ba ne, haya nake yi.

Ya ci gaba da cewa, yanzu a cikin wannan al’amari da na ke yi, in an ce na mallaki gida mai dimbin yawa, wadansu da za su ke kallo na sai su ce gaskiya ne, amma wallahi tallahi, daki daya bani da wani gida da za a kalla ace wannan mallakina ne, na rasa ido yanzu zancen da na ke mai kallo na ba na gani.

A kan batun ‘yan fim da za su iya taimaka masa, Karkuzu ya ce ba wai al’ummar Kano kawai ko al’ummar Jos, Kaduna ko na Legas ba, duk al’ummar duniyar nan ina bukatar a taimaka min, wannan gida yanzu da aka sa shi a kasuwa za a sayar, ba ni da kudi, bayan ba ni da kudi ba na gani, ba na zuwa ko’ina, ina da ‘ya’ya, maganar abinci kam ma babu, wannan shi ne zahirin gaskiya inji Karkuzu a hirar su da TRT Hausa na ranar 10 ga watan Agusta 2023.

A wancan lokacin sakamakon wannan neman taimako da ya yi, kyaftin din tawagar kwallon kafa ta Nijeriya Ahmed Musa ya gwangwaje Karkuzu da kyautar makudan kudade har Naira 5,000,000, sannan kuma ya ba da umarnin a nemo gida ya saya masa, wanda bai wuce naira miliyan hudu zuwa biyar ba, kuma haka aka yi, domin kuwa Ahmed Musa ya saya masa gida na N5,500,000 kafin rasuwarsa.

Karkuzu ya yi manyan fina-finai madu dimbin yawa da tasiri a masana’antar Kannywood, daga cikinsu akwai Gida Da Waje, Ga Duhu Ga Haske wanda su ka shirya da Jaruma Zainab Muhammad (Indomie), a tsawon shekaru fiye da 40 da ya shafe a masana’antar Kannywood ya yiwa da dama a cikin jarumai hanyar samun daukaka a masana’antar.

Tasirin marigayi Abdullahi Shuaibu Karkuzu ba boyayye ba ne a jahar Kano, Arewacin Nijeriya da ma kasar bakidaya, wata sanarwa da babban daraktan yada labarai na gwamnan jahar Kano Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar a ranar 28 ga watan Maris wadda LEADERSHIP Hausa ta fassara ya nuna yadda gwamnan jahar Abba Kabir Yusuf ya yi ta’aziyar mutuwar Abdullahi Shuaibu Karkuzu.

Sanarwar ta ce: “Gwamna Yusuf Ya Yi Ta’aziya Ga Masana’antar Kannywood Da Iyalan Shahararren Jarumin Kannywood Karkuzu Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya yi alhinin rasuwar shahararren jarumin Kannywood, Abdullahi Shuaibu wanda aka fi sani da Karkuzu wanda ya rasu a kwanakin baya bayan doguwar jinya, Karkuzu ya rasu ya na da shekaru 94 a duniya.

Hakan ya fito ne a wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar a Kano ranar Juma’a, Gwamnan ya ce mutuwar babban rashi ne ga masana’antar Kannywood na wani wanda ya kira kwararren jarumi mai fikira, da ya jajirce wajen yin sana’ar tare da taimako wajen tasowar yan wasa da dama a masana’antar.

Ya ci gaba da cewa marigayin ya bar wani gibi da zai yi wuyar cikewa cikin sauki, a shekarun da ya kwashe a masana’antar, ya nuna kwarewa iri-iri da kuma kokarin kawo sauyi ta hanyar nishadantarwa da kuma fadakarwa.

A madadin gwamnati da jama’ar Jihar Kano, gwamnan ya na mika sakon ta’aziyya ga iyalan mamacin, ‘yan Kannywood da masana’antar fim.

Ya kuma roki Allah Madaukakin Sarki da ya kyautata makwancinsa ya kuma baiwa ruhinsa dawwamammen aminci a cikin kabari, ya kuma roki Allah ya sa Aljanna Firdausi ce makomarshi.”

Wannan ya sa muka rubuta makalar “BA RABO DA GWANI BA” domin tunawa da wannan dattijo da ya shafe kusan rabin shekarun rayuwarshi domin ya nishadantar ya kuma fadakar da al’umma ta hanyar fina-finan Hausa, Karkuzu zai shafe tsawon lokaci ana tunawa da irin gudunmawar da bayar wajen kawo masana’antar Kannywood matsayin da ta ke a yanzu.

Hakazalika masu sha’awar kallon fina finan Hausa zasu dade su na kallon marigayin a matsayin wani mutum da ya nishadantar da kuruciyarsu ya kuma fadakar da tsufansu ta hanyar fina finanshi, sannan kuma matasa a masana’antar Kannywood za su tuna Karkuzu a matsayin wani jigo da su ka kwaikwayi ayyukanshi kuma sukayi amfanin da shawarwarinshi wajen samun daukaka a masana’antar.

Abdullahi
Rabilu Sanusi Bena
+ postsBio
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Turkiyya Ta Zama Ƙasa Ta Biyu Da Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

MASU ALAKA

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina
Nishadi

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

June 14, 2026
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi
Nishadi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

June 14, 2026
Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro
Nishadi

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro

May 31, 2026
Next Post
Yadda Amarya Za Ta Gyara Jikinta Har Zuwa Ranar Aure (II)

Yadda Amarya Za Ta Gyara Jikinta Har Zuwa Ranar Aure (II)

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.