• English
  • Business News
Wednesday, July 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kofin Gwamna Uba Sani: Ahmed Musa Ya Yi Alƙawarin Fitar Da ‘Yan Wasa 6

by Sulaiman
10 months ago
in Labarai, Wasanni
0
Kofin Gwamna Uba Sani: Ahmed Musa Ya Yi Alƙawarin Fitar Da ‘Yan Wasa 6
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani muhimmin mataki na wanzar da zaman lafiya da hada kan matasa, an kammala gasar lashe kofin ‘Unity cup’ na Gwamna Uba Sani wanda Akanta Janar (AG), Bashir Suleiman Zuntu ya shirya wa matasan Kubau kuma ya ɗauki nauyi.

 

Gasar ta kwallon kafa, ta kwashe kimanin Mako 6 ana gwabzawa a tsakanin kungiyoyi 32 da suka fito daga sassa daban-daban na yankin mazabar Kubau, da ke shiyya ta daya a Kaduna.

  • Gwamna Uba Sani Zai Kaddamar Da Kwalejin Koyon Aikin Jinya Da Ungozoma A Pambegua 
  • Kaduna: Ruftawar Hanya Sakamakon Ambaliyar Ruwa Ta Katse Garuruwa Biyar A Lere 

An kamala gasar ne a ranar Lahadi, 15 ga watan Satumba, 2024 a filin wasa na Zuntu Township.

 

Labarai Masu Nasaba

Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

AG Bashir, ya bayyana jin dadinsa da yadda yaga al’ummar yankin sun taru wuri guda suna nishadi ba tare da nuna banbancin yare ko wata wariya ba, inda ya kara da cewa, wannan shiri za a inganta shi, kuma zai ci gaba da gudana.

 

Da yake bayyana muhimmancin gudanar da wasanni a tsakanin Matasa, musamman wasan kwallon kafa, AG ya ce, “kwallo tana da farin jini a tsakanin matasan yankin, inda ta sake hada kawunansu, kowa ke jin dadin zama da juna ba kyara ba tsangwama.”

 

Ya kuma bayyana jin dadinsa da yadda matasan ke bin tsarin doka, babu hatsaniya, kowa na tsayawa inda jami’an tsaro suka umurta da a kiyaye.

Uba Sani
Akanta-janar na jihar Kaduna, Hon. Bashir Suleiman Zuntu

Ya kuma yi kira ga matasa da cewa, akwai hanyoyin samun nasara a rayuwa da yawa, musamman a bangaren wasanni, ba dole ba ne, sai mutum ya yi aikin Gwamnati, ko Kasuwanci, ko Siyasa, ne zai yi nasara ba. Inda ya buga misali da cewa, “Ga Shahararren dan wasan kwallon kafa kuma kaftin din tawagar kwallon kafa ta Nijeriya da yake tare da mu a wannan filin wasa, Ahmed Musa, ya zama mutum mai nasara a rayuwa ta hanyar wasan kwallon kafar, kuma kowa ya son shi da taimakon matasa sanadiyyar wannan Nasarar”.

 

Ahmed Musa, akan abinda ya saba na taimakon matasa don ganin sun cimma burikan su na samun nasara, ya yi alkawarin fitar da ‘yan wasa 6 da suka yi fice a gasar zuwa kasashen ketare.

 

AG Bashir, Ya kuma nanata alkawarin Gwamna Uba Sani cewa, nan ba da jimawa ba, za a fara aikin gyaran filin wasa na Sir Ahmadu bello da ke Kaduna (ASB), kuma kungiyar kwallon kafa ta Kaduna United, da tuni ta fita acikin jerin kungiyoyin da suke buga gasar Firimiya ta Nijeriya, za ta komo cikin jerin kungiyoyin.

 

Ya kuma gode wa Gwamna Uba Sani, kan kudirinsa na maido da Kaduna United cikin jerin kungiyoyin Firimiya.

 

Daga cikin fitattun ‘yan wasan kwallon kafa da suka halarci wasan karshen, akwai Ahmad Musa da Shehu Abdullahi duka, su biyun, suna daga cikin tawagar kwallon kafa ta Nijeriya (Super Eagles).

Uba Sani
Kungiyar D.officer da ta zama zakara

Tun da Farko, Hon. Musa Danjuma Bello, Shugaban Shirya gasar kofin ‘Unity Cup’, ya bayyana cewa, an shirya gasar ne domin wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a tsakanin matasan Karamar hukumar Kubau.

 

“Wannan gasar, ta tattaro kungiyoyin kwallon kafa 32, kuma kowacce kungiya za ta samu kyautar sunkin jesi da sauran kayayyakin kwallo. Bugu da kari, Kungiyar D.Officer FC wacce ta zama zakara, ta samu Karin kyautar kudi har Naira 500,000; Bagadaza FC wacce ta zama ta biyu, ta samu karin kyautar kudi naira 300,000 yayin da kungiyar Bugau FC ta samu karin kyautar kudi naira 200,000.

 

A nasa Jawabin, Kakakin majalisar jihar kaduna, Hon. Yusuf Liman ya nuna jin dadinsa da yadda yaga matasan Kubau, masoya kwallo a filin wasa na Zuntu township sun taru suna murnar wannan gasa, “lallai ya tabbata kwallo tana hada kan matasa”.

Uba Sani
Kungiyar Bagadaza FC da ta Zama ta Biyu a gasar

Liman, ya kuma jinjina wa kwamitin shirya wannan gasar lashe kofin hada kan al’umma ‘Unity Cup’ na Sanata Uba Sani wanda Akanta-janar, Hon. Bashir Suleiman Zuntu ya dauki nauyi.

 

Haka kuma, Dan Majalisa mai wakiltar mazabar Kubau, Shehu Yunus Pambegua ya nuna farin cikinsa da Allah ya kawo wannan rana da aka buga wasa na karshe na ‘Unity Cup’ kuma aka tashi lafiya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnatin Uba SaniWasannin Olympics
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Lashe Gasar Fasaha Ta Duniya Karo Na 47

Next Post

Kasar Sin Na Girmama Cikakken ‘Yancin Serbia

Related

Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari
Labarai

Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

3 hours ago
VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano
Labarai

VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

4 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

7 hours ago
Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China
Labarai

Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

8 hours ago
Girman Kai Da Son Zuciya Ba Za Su Sa A Amince Ko Ba Da Hadin Kai Ba
Ra'ayi Riga

Girman Kai Da Son Zuciya Ba Za Su Sa A Amince Ko Ba Da Hadin Kai Ba

9 hours ago
Bayan Shekaru 6 A Hannun Boko Haram, Wasu Yara Biyu Sun Kuɓuta
Labarai

Bayan Shekaru 6 A Hannun Boko Haram, Wasu Yara Biyu Sun Kuɓuta

9 hours ago
Next Post
Kasar Sin Na Girmama Cikakken ‘Yancin Serbia

Kasar Sin Na Girmama Cikakken ‘Yancin Serbia

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9

Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9

July 15, 2025
Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

July 15, 2025
VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

July 15, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

July 15, 2025
An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

July 15, 2025
Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

July 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

July 15, 2025
Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

July 15, 2025
Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

July 15, 2025
Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro

Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro

July 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.