ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Uba Sani Zai Kaddamar Da Kwalejin Koyon Aikin Jinya Da Ungozoma A Pambegua 

by Sulaiman
2 years ago
Ruwa

LABARAI MASU NASABA

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

Gwamnatin Jihar Kaduna, karkashin jagorancin Gwamna Uba Sani, ta shirya tsaf don kaddamar da kwalejin koyon aikin jinya da ungozoma da ke karamar hukumar Soba a  yankin Zaria da ke Jihar.

Hakan na kunshe ne acikin wata tattaunawa da manema labarai da shugaban kwalejin, Dakta Yusuf Bello ya yi ranar Litinin, 9 ga watan Satumba, 2024 gabanin kaddamar da Kwalejin a harabar Kwalejin da ke Pambegua.
  • Gine-gine Da Zubar Da Shara A Magudanun Ruwa Ke Haifar Da Ambaliya A Kaduna – Kwamiti
  • Zanga-zanga: Gwamna Uba Sani Ya Musanta Sanya Dokar Hana Fita A Kaduna
Kwalejin Ta Pambegua, daya ce daga cikin sansanonin kwalejojin da ke da babban sansani a Asibitin Dantshoho, a birnin Kaduna, karkashin shugabancin Dakta Yusuf Bello.
Sansanonin Kwalejin sun hada da Kwalejin Koyon aikin jinya ta Asibitin Dantsoho, Tudun wada, da ke cikin birnin Kaduna; Kwalejin Koyon aikin jinya, Kafanchan, da ke kudancin Kaduna, da Kwalejin Koyon aikin jinya, Pambegua da ke yankin Zaria.
Kwalejin ta samu amincewar hukumomin da ke kula da manyan makarantun kiwon lafiya, da hukumar kula da manyan makarantun kimiyya da fasaha (NBTE) don gudanar da karatuttuka a bangaren aikin jinya na shekaru hudu a jere (ND-HND Nursing), ungozoma (Basic Midwifery) da General Nursing.
Dakta Bello ya jinjina wa al’ummar Pambegua bisa namijin kokarinsu da aljihunsu, da karfinsu wajen ganin an samu damar kaddamar da wannan kwalejin a yankinsu, har ta kuma fara aiki.
Shugaban ya kuma sake mika godiyarsa ta musamman ga Gwamna Uba Sani kan kishinsa ga ci gaban al’ummar Kaduna baki daya.
Tun da farko, Hakimin Pambegua, Karfen Dawakin Zazzau, Sufyan Sani Usman, ya jinjina wa Gwamna Uba, bisa kafa irin wannan kwalejin a yankin, inda ya ce, kwalejin ba al’ummar Pambegua kadai ce za ta amfanar ba, har da yankin Zaria da Jihar Kaduna baki daya.
Hakimin ya kuma gode wa Dakta Bello Yusuf wajen ganin wannan Kwalejin ta samu nasarar kafuwa.
Shugaban kwamitin kwalejin koyon aikin jinya da ungozoma da ke Pambegua, Alhaji Haruna Ahmad, ya kuma yaba da irin gudunmawar da al’umma suka bayar, da suka hada da gyare-gyare da kuma sayan kayan aiki domin tabbatar da gudanar da ayyuka a kwalejin.
Ya kuma yabawa gwamnati bisa yadda ta tabbatar da aikin da aka dade ana jira a yankin tare da tabbatar da cewa al’ummar karkara za su ci gajiyar kokarin gwamnati.
Shi ma Akanta Janar na Jihar Kaduna, kuma tsohon shugaban karamar hukuma, Alhaji Bashir Suleiman Zuntu, ya yaba da irin nasarorin da gwamnati ta samu, ya kuma yi fatan samun nasarar gudanar da ayyuka a kwalejin ta Pambegua.
Uba Sani
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
  • Sulaiman
    Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari
  • Sulaiman
    Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
  • Sulaiman
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
Labarai

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Next Post
Nijeriya Ta Samu Lambobin Yabo 7 A Wasannin Nakasassu Ta Bana

Nijeriya Ta Samu Lambobin Yabo 7 A Wasannin Nakasassu Ta Bana

LABARAI MASU NASABA

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.