ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 6, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Uba Sani Zai Kaddamar Da Kwalejin Koyon Aikin Jinya Da Ungozoma A Pambegua 

by Sulaiman
2 years ago
Ruwa

LABARAI MASU NASABA

Kwankwaso Ya Yi Ta’aziyyar ’Ya’yan Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi da Suka Rasu a Hatsarin Mota

Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata

Gwamnatin Jihar Kaduna, karkashin jagorancin Gwamna Uba Sani, ta shirya tsaf don kaddamar da kwalejin koyon aikin jinya da ungozoma da ke karamar hukumar Soba a  yankin Zaria da ke Jihar.

Hakan na kunshe ne acikin wata tattaunawa da manema labarai da shugaban kwalejin, Dakta Yusuf Bello ya yi ranar Litinin, 9 ga watan Satumba, 2024 gabanin kaddamar da Kwalejin a harabar Kwalejin da ke Pambegua.
  • Gine-gine Da Zubar Da Shara A Magudanun Ruwa Ke Haifar Da Ambaliya A Kaduna – Kwamiti
  • Zanga-zanga: Gwamna Uba Sani Ya Musanta Sanya Dokar Hana Fita A Kaduna
Kwalejin Ta Pambegua, daya ce daga cikin sansanonin kwalejojin da ke da babban sansani a Asibitin Dantshoho, a birnin Kaduna, karkashin shugabancin Dakta Yusuf Bello.
Sansanonin Kwalejin sun hada da Kwalejin Koyon aikin jinya ta Asibitin Dantsoho, Tudun wada, da ke cikin birnin Kaduna; Kwalejin Koyon aikin jinya, Kafanchan, da ke kudancin Kaduna, da Kwalejin Koyon aikin jinya, Pambegua da ke yankin Zaria.
Kwalejin ta samu amincewar hukumomin da ke kula da manyan makarantun kiwon lafiya, da hukumar kula da manyan makarantun kimiyya da fasaha (NBTE) don gudanar da karatuttuka a bangaren aikin jinya na shekaru hudu a jere (ND-HND Nursing), ungozoma (Basic Midwifery) da General Nursing.
Dakta Bello ya jinjina wa al’ummar Pambegua bisa namijin kokarinsu da aljihunsu, da karfinsu wajen ganin an samu damar kaddamar da wannan kwalejin a yankinsu, har ta kuma fara aiki.
Shugaban ya kuma sake mika godiyarsa ta musamman ga Gwamna Uba Sani kan kishinsa ga ci gaban al’ummar Kaduna baki daya.
Tun da farko, Hakimin Pambegua, Karfen Dawakin Zazzau, Sufyan Sani Usman, ya jinjina wa Gwamna Uba, bisa kafa irin wannan kwalejin a yankin, inda ya ce, kwalejin ba al’ummar Pambegua kadai ce za ta amfanar ba, har da yankin Zaria da Jihar Kaduna baki daya.
Hakimin ya kuma gode wa Dakta Bello Yusuf wajen ganin wannan Kwalejin ta samu nasarar kafuwa.
Shugaban kwamitin kwalejin koyon aikin jinya da ungozoma da ke Pambegua, Alhaji Haruna Ahmad, ya kuma yaba da irin gudunmawar da al’umma suka bayar, da suka hada da gyare-gyare da kuma sayan kayan aiki domin tabbatar da gudanar da ayyuka a kwalejin.
Ya kuma yabawa gwamnati bisa yadda ta tabbatar da aikin da aka dade ana jira a yankin tare da tabbatar da cewa al’ummar karkara za su ci gajiyar kokarin gwamnati.
Shi ma Akanta Janar na Jihar Kaduna, kuma tsohon shugaban karamar hukuma, Alhaji Bashir Suleiman Zuntu, ya yaba da irin nasarorin da gwamnati ta samu, ya kuma yi fatan samun nasarar gudanar da ayyuka a kwalejin ta Pambegua.
Uba Sani
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Kwankwaso Ya Yi Ta’aziyyar ’Ya’yan Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi da Suka Rasu a Hatsarin Mota
  • Sulaiman
    An Kaddamar Da Atisayen Hadin Gwiwa Mai Taken “Hadin Gwiwar Ayyuka Kan Teku-2026” Tsakanin Sin Da Rasha
  • Sulaiman
    Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin
  • Sulaiman
    An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Kwankwaso Ya Yi Ta’aziyyar ’Ya’yan Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi da Suka Rasu a Hatsarin Mota

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata
Manyan Labarai

Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata

July 6, 2026
Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi
Manyan Labarai

Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi

July 6, 2026
Next Post
Nijeriya Ta Samu Lambobin Yabo 7 A Wasannin Nakasassu Ta Bana

Nijeriya Ta Samu Lambobin Yabo 7 A Wasannin Nakasassu Ta Bana

LABARAI MASU NASABA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Kwankwaso Ya Yi Ta’aziyyar ’Ya’yan Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi da Suka Rasu a Hatsarin Mota

July 6, 2026
An Kaddamar Da Atisayen Hadin Gwiwa Mai Taken “Hadin Gwiwar Ayyuka Kan Teku-2026” Tsakanin Sin Da Rasha

An Kaddamar Da Atisayen Hadin Gwiwa Mai Taken “Hadin Gwiwar Ayyuka Kan Teku-2026” Tsakanin Sin Da Rasha

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata

Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata

July 6, 2026
Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi

Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi

July 6, 2026
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami

July 6, 2026
Ƴan Bindiga Sun Kashe Manoma 9, Sun Sace Da Dama A Birnin Gwari

Ƴan Bindiga Sun Kashe Manoma 9, Sun Sace Da Dama A Birnin Gwari

July 6, 2026
Gwamnatin Kano Ta Kashe Biliyan 928 A Ayyukan Ci Gaba 1,508

Gwamnatin Kano Ta Kashe Biliyan 928 A Ayyukan Ci Gaba 1,508

July 6, 2026
Jonathan Ya Musanta Zargin Tayin Naira Biliyan 500 Domin Raba Kuri’un Kudu Maso Kudu

Jonathan Ya Musanta Zargin Tayin Naira Biliyan 500 Domin Raba Kuri’un Kudu Maso Kudu

July 6, 2026
FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

July 5, 2026
Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

July 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.