ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kofin Gwamna Uba Sani: Ahmed Musa Ya Yi Alƙawarin Fitar Da ‘Yan Wasa 6

by Sulaiman
2 years ago
Uba Sani

A wani muhimmin mataki na wanzar da zaman lafiya da hada kan matasa, an kammala gasar lashe kofin ‘Unity cup’ na Gwamna Uba Sani wanda Akanta Janar (AG), Bashir Suleiman Zuntu ya shirya wa matasan Kubau kuma ya ɗauki nauyi.

 

Gasar ta kwallon kafa, ta kwashe kimanin Mako 6 ana gwabzawa a tsakanin kungiyoyi 32 da suka fito daga sassa daban-daban na yankin mazabar Kubau, da ke shiyya ta daya a Kaduna.

ADVERTISEMENT
  • Gwamna Uba Sani Zai Kaddamar Da Kwalejin Koyon Aikin Jinya Da Ungozoma A Pambegua 
  • Kaduna: Ruftawar Hanya Sakamakon Ambaliyar Ruwa Ta Katse Garuruwa Biyar A Lere 

An kamala gasar ne a ranar Lahadi, 15 ga watan Satumba, 2024 a filin wasa na Zuntu Township.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

AG Bashir, ya bayyana jin dadinsa da yadda yaga al’ummar yankin sun taru wuri guda suna nishadi ba tare da nuna banbancin yare ko wata wariya ba, inda ya kara da cewa, wannan shiri za a inganta shi, kuma zai ci gaba da gudana.

 

Da yake bayyana muhimmancin gudanar da wasanni a tsakanin Matasa, musamman wasan kwallon kafa, AG ya ce, “kwallo tana da farin jini a tsakanin matasan yankin, inda ta sake hada kawunansu, kowa ke jin dadin zama da juna ba kyara ba tsangwama.”

 

Ya kuma bayyana jin dadinsa da yadda matasan ke bin tsarin doka, babu hatsaniya, kowa na tsayawa inda jami’an tsaro suka umurta da a kiyaye.

Uba Sani
Akanta-janar na jihar Kaduna, Hon. Bashir Suleiman Zuntu

Ya kuma yi kira ga matasa da cewa, akwai hanyoyin samun nasara a rayuwa da yawa, musamman a bangaren wasanni, ba dole ba ne, sai mutum ya yi aikin Gwamnati, ko Kasuwanci, ko Siyasa, ne zai yi nasara ba. Inda ya buga misali da cewa, “Ga Shahararren dan wasan kwallon kafa kuma kaftin din tawagar kwallon kafa ta Nijeriya da yake tare da mu a wannan filin wasa, Ahmed Musa, ya zama mutum mai nasara a rayuwa ta hanyar wasan kwallon kafar, kuma kowa ya son shi da taimakon matasa sanadiyyar wannan Nasarar”.

 

Ahmed Musa, akan abinda ya saba na taimakon matasa don ganin sun cimma burikan su na samun nasara, ya yi alkawarin fitar da ‘yan wasa 6 da suka yi fice a gasar zuwa kasashen ketare.

 

AG Bashir, Ya kuma nanata alkawarin Gwamna Uba Sani cewa, nan ba da jimawa ba, za a fara aikin gyaran filin wasa na Sir Ahmadu bello da ke Kaduna (ASB), kuma kungiyar kwallon kafa ta Kaduna United, da tuni ta fita acikin jerin kungiyoyin da suke buga gasar Firimiya ta Nijeriya, za ta komo cikin jerin kungiyoyin.

 

Ya kuma gode wa Gwamna Uba Sani, kan kudirinsa na maido da Kaduna United cikin jerin kungiyoyin Firimiya.

 

Daga cikin fitattun ‘yan wasan kwallon kafa da suka halarci wasan karshen, akwai Ahmad Musa da Shehu Abdullahi duka, su biyun, suna daga cikin tawagar kwallon kafa ta Nijeriya (Super Eagles).

Uba Sani
Kungiyar D.officer da ta zama zakara

Tun da Farko, Hon. Musa Danjuma Bello, Shugaban Shirya gasar kofin ‘Unity Cup’, ya bayyana cewa, an shirya gasar ne domin wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a tsakanin matasan Karamar hukumar Kubau.

 

“Wannan gasar, ta tattaro kungiyoyin kwallon kafa 32, kuma kowacce kungiya za ta samu kyautar sunkin jesi da sauran kayayyakin kwallo. Bugu da kari, Kungiyar D.Officer FC wacce ta zama zakara, ta samu Karin kyautar kudi har Naira 500,000; Bagadaza FC wacce ta zama ta biyu, ta samu karin kyautar kudi naira 300,000 yayin da kungiyar Bugau FC ta samu karin kyautar kudi naira 200,000.

 

A nasa Jawabin, Kakakin majalisar jihar kaduna, Hon. Yusuf Liman ya nuna jin dadinsa da yadda yaga matasan Kubau, masoya kwallo a filin wasa na Zuntu township sun taru suna murnar wannan gasa, “lallai ya tabbata kwallo tana hada kan matasa”.

Uba Sani
Kungiyar Bagadaza FC da ta Zama ta Biyu a gasar

Liman, ya kuma jinjina wa kwamitin shirya wannan gasar lashe kofin hada kan al’umma ‘Unity Cup’ na Sanata Uba Sani wanda Akanta-janar, Hon. Bashir Suleiman Zuntu ya dauki nauyi.

 

Haka kuma, Dan Majalisa mai wakiltar mazabar Kubau, Shehu Yunus Pambegua ya nuna farin cikinsa da Allah ya kawo wannan rana da aka buga wasa na karshe na ‘Unity Cup’ kuma aka tashi lafiya.

Uba Sani
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Next Post
Kasar Sin Na Girmama Cikakken ‘Yancin Serbia

Kasar Sin Na Girmama Cikakken ‘Yancin Serbia

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.