ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kofin Gwamna Uba Sani: Ahmed Musa Ya Yi Alƙawarin Fitar Da ‘Yan Wasa 6

by Sulaiman
2 years ago
Uba Sani

A wani muhimmin mataki na wanzar da zaman lafiya da hada kan matasa, an kammala gasar lashe kofin ‘Unity cup’ na Gwamna Uba Sani wanda Akanta Janar (AG), Bashir Suleiman Zuntu ya shirya wa matasan Kubau kuma ya ɗauki nauyi.

 

Gasar ta kwallon kafa, ta kwashe kimanin Mako 6 ana gwabzawa a tsakanin kungiyoyi 32 da suka fito daga sassa daban-daban na yankin mazabar Kubau, da ke shiyya ta daya a Kaduna.

ADVERTISEMENT
  • Gwamna Uba Sani Zai Kaddamar Da Kwalejin Koyon Aikin Jinya Da Ungozoma A Pambegua 
  • Kaduna: Ruftawar Hanya Sakamakon Ambaliyar Ruwa Ta Katse Garuruwa Biyar A Lere 

An kamala gasar ne a ranar Lahadi, 15 ga watan Satumba, 2024 a filin wasa na Zuntu Township.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Bai Wa Ɗalibai 100MB Na Data Kyauta Kullum

AG Bashir, ya bayyana jin dadinsa da yadda yaga al’ummar yankin sun taru wuri guda suna nishadi ba tare da nuna banbancin yare ko wata wariya ba, inda ya kara da cewa, wannan shiri za a inganta shi, kuma zai ci gaba da gudana.

 

Da yake bayyana muhimmancin gudanar da wasanni a tsakanin Matasa, musamman wasan kwallon kafa, AG ya ce, “kwallo tana da farin jini a tsakanin matasan yankin, inda ta sake hada kawunansu, kowa ke jin dadin zama da juna ba kyara ba tsangwama.”

 

Ya kuma bayyana jin dadinsa da yadda matasan ke bin tsarin doka, babu hatsaniya, kowa na tsayawa inda jami’an tsaro suka umurta da a kiyaye.

Uba Sani
Akanta-janar na jihar Kaduna, Hon. Bashir Suleiman Zuntu

Ya kuma yi kira ga matasa da cewa, akwai hanyoyin samun nasara a rayuwa da yawa, musamman a bangaren wasanni, ba dole ba ne, sai mutum ya yi aikin Gwamnati, ko Kasuwanci, ko Siyasa, ne zai yi nasara ba. Inda ya buga misali da cewa, “Ga Shahararren dan wasan kwallon kafa kuma kaftin din tawagar kwallon kafa ta Nijeriya da yake tare da mu a wannan filin wasa, Ahmed Musa, ya zama mutum mai nasara a rayuwa ta hanyar wasan kwallon kafar, kuma kowa ya son shi da taimakon matasa sanadiyyar wannan Nasarar”.

 

Ahmed Musa, akan abinda ya saba na taimakon matasa don ganin sun cimma burikan su na samun nasara, ya yi alkawarin fitar da ‘yan wasa 6 da suka yi fice a gasar zuwa kasashen ketare.

 

AG Bashir, Ya kuma nanata alkawarin Gwamna Uba Sani cewa, nan ba da jimawa ba, za a fara aikin gyaran filin wasa na Sir Ahmadu bello da ke Kaduna (ASB), kuma kungiyar kwallon kafa ta Kaduna United, da tuni ta fita acikin jerin kungiyoyin da suke buga gasar Firimiya ta Nijeriya, za ta komo cikin jerin kungiyoyin.

 

Ya kuma gode wa Gwamna Uba Sani, kan kudirinsa na maido da Kaduna United cikin jerin kungiyoyin Firimiya.

 

Daga cikin fitattun ‘yan wasan kwallon kafa da suka halarci wasan karshen, akwai Ahmad Musa da Shehu Abdullahi duka, su biyun, suna daga cikin tawagar kwallon kafa ta Nijeriya (Super Eagles).

Uba Sani
Kungiyar D.officer da ta zama zakara

Tun da Farko, Hon. Musa Danjuma Bello, Shugaban Shirya gasar kofin ‘Unity Cup’, ya bayyana cewa, an shirya gasar ne domin wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a tsakanin matasan Karamar hukumar Kubau.

 

“Wannan gasar, ta tattaro kungiyoyin kwallon kafa 32, kuma kowacce kungiya za ta samu kyautar sunkin jesi da sauran kayayyakin kwallo. Bugu da kari, Kungiyar D.Officer FC wacce ta zama zakara, ta samu Karin kyautar kudi har Naira 500,000; Bagadaza FC wacce ta zama ta biyu, ta samu karin kyautar kudi naira 300,000 yayin da kungiyar Bugau FC ta samu karin kyautar kudi naira 200,000.

 

A nasa Jawabin, Kakakin majalisar jihar kaduna, Hon. Yusuf Liman ya nuna jin dadinsa da yadda yaga matasan Kubau, masoya kwallo a filin wasa na Zuntu township sun taru suna murnar wannan gasa, “lallai ya tabbata kwallo tana hada kan matasa”.

Uba Sani
Kungiyar Bagadaza FC da ta Zama ta Biyu a gasar

Liman, ya kuma jinjina wa kwamitin shirya wannan gasar lashe kofin hada kan al’umma ‘Unity Cup’ na Sanata Uba Sani wanda Akanta-janar, Hon. Bashir Suleiman Zuntu ya dauki nauyi.

 

Haka kuma, Dan Majalisa mai wakiltar mazabar Kubau, Shehu Yunus Pambegua ya nuna farin cikinsa da Allah ya kawo wannan rana da aka buga wasa na karshe na ‘Unity Cup’ kuma aka tashi lafiya.

Uba Sani
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace
  • Sulaiman
    Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Bai Wa Ɗalibai 100MB Na Data Kyauta Kullum
  • Sulaiman
    Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace
Wasanni

Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar da Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC da NECO
Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Bai Wa Ɗalibai 100MB Na Data Kyauta Kullum

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana
Labarai

Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

September 10, 2026
Next Post
Kasar Sin Na Girmama Cikakken ‘Yancin Serbia

Kasar Sin Na Girmama Cikakken ‘Yancin Serbia

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar da Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC da NECO

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Bai Wa Ɗalibai 100MB Na Data Kyauta Kullum

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

September 10, 2026
Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

September 10, 2026
Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026
Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.