• English
  • Business News
Thursday, June 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kogin Kumadugu Ya Yi Ambaliya Karon Farko Cikin Shekara 100 A Yobe

by Muhammad Maitela
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Kogin Kumadugu Ya Yi Ambaliya Karon Farko Cikin Shekara 100 A Yobe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Al’ummar jihar Yobe, sun bayyana cewa sama da shekara 100 ba a taba ganin makamancin ibtila’in ambaliyar ruwa daga kogin Kumadugu ba da ya mamaye dubban gidaje da amfanin gonakin jama’a.

Wani dattijo mai shekara 78 a garin Gwio Kura da ke karamar hukumar Bade (Gashuwa), yankin Gwio Kura, Baani Ari Kolo, ya bayyana cewa duk dan shekara 100 ba shi da masaniyar malalar ruwan Kogin Kumadugu zuwa garin Gwio Kura da kauyukan da ke makobtaka da ita.

Ya ce a wannan shekara sun fuskanci mummunar ambaliyar ruwan Kogin wanda ya lalata amfanin gonakin dubban jama’a tare da ruguza gidajensu.

Kumadugu

“Bana ina da shekara 78 a duniya, kuma ni haifaffen garin Gwio Kura ne da ke karamar hukumar Bade. Bana Allah ya jarabce mu da ibtila’in ambaliyar ruwan Kogin Kumadugu wanda ya mamaye garuruwanmu da gonakinmu; sannan duk dan shekara 100 ba zai gaya maka cewa ya san ruwan Kogin ya na zuwa wadannan garuruwa namu ba. Saboda haka muna kira ga gwamnatocin Tarayya da ta jihar Yobe su kawo mana daukin gaggawa, hadi da Kungiyoyin jinkai.” In ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Zai Rattaba Hannu Kan Kudirorin Sauya Fasalin Haraji 4 A Yau Alhamis 

Kano Ta Ayyana Ranar Alhamis Hutu Domin Murnar Sabuwar Shekarar Musulunci

Al’ummar jihar Yobe sun bukaci Gwamnatin Tarayya ta kawo musu daukin gaggawa saboda yadda suke ci gaba da fuskantar mummunan ambaliyar ruwan da ta mamaye garuruwansu tare da amfanin gonakin da suka noma a daminar bana.

Haka kuma, sun nuna fargabar barkewar yunwa da fatara sakamakon yadda ambaliyar ruwan ta yi musu kwab-daya ta yadda ba su a tsuntsu kuma ba su ba tarko- yayin da ambaliyar ruwan ta ruguza gidaje tare da lakume amfanin gonakin da suka noma.

  • Firaministan Habasha Ya Kaddamar Da Dakin Adana Kayan Kimiyya Da Fasaha Da Kasar Sin Ta Samar
  • Bukatar Samar Wa Kotunan Korafe-korafen Zabe Kudaden Gudanarwa

Wannan mummunan ambaliyar ruwan ta faru ne sakamakon tumbatsar da Kogin Kumadugu (Riber Yobe) ya yi inda ya malala ruwan tare da mamaye garuruwa da daman gaske hadi da barnata amfanin gonakin dubban jama’ar jihar Yobe.

Wanda ya tilasta jama’a fitowa fili tare da neman gudumawar gaggawa daga Gwamnonin Tarayya da sauran kungiyoyin jinkai a ciki da wajen kasar nan. Kamar yadda aka sani, Kogin Kumadugu (Riber Yobe) ya na daga cikin manyan koguna a Yammacin Afrika wanda ya fada Tafkin Chadi.

Kogi ne wanda ruwan sa ke fitowa daga Kogin Hadeja, Kogin Jama’are hadi da Kumadugu Gana, da wasu Dama-damai da ke antayo ruwansu zuwa kogin, sannan daga cikin manyan garuruwan da suke zaune kan gabar Kogin sun hada da Gashuwa, Gaidam da Damasak a Nijeriya, sai garin Diffa a Nijar.

A wannan shekara, Kogin Kumadugu ya yi cika ya batse tare da tumbatsar da ta haifar da mummunan ambaliyar ruwan da ta shafe wasu garuruwa da dama a jihar Yobe, musamman a kananan hukumomin Bade (Gashu’a) da Jakusko- uwa uba garin Gashuwa da kauyukanta, wanda baya ga mamaye kauyukan kuma ya yi wa garin Gashuwa kawanya da mamaye unguwannin Katuzu, Abujan Amarebda wani yanki na Zango da Unguwan Lawan.

A unguwar Abujan Amare, ambaliyar ruwan ya rusa sama da gidaje 200, haka kuma ruwan ya rusa fiye da wannan adadin a unguwar Katuzu, tare da mamaye Kasuwar Danyen Kaya, Katuzu Primary, Keasawa Primary da shagunan jama’a da ke bakin Tashar Kuka, duk a cikin garin Gashuwa. Yayin da ambaliyar ruwan ta shafi baki dayan gundumomi 10 da ke karamar hukumar Bade, wanda na baya -bayan ne su ne garuruwan Gasima da Dagona da ambaliyar ruwan ta mamaye baki daya.

A hannu guda kuma, ambaliyar ruwan ta yi wa kauyuka da garuruwa da daman gaske dukan a kawo wuka a karamar hukumar Jakusko; ta rushe gidajen jama’a tare da lamushe amfanin gonakinsu- daga ciki akwai garin Girgir, Katamma, Amshi, Guyik, Muguram, Jaba, Jakusko, Dumbari, Gwayo, Dukorel, Lafiya, Bayam, Buduwa, Saminaka, Garin Saje, Dachiya, Zabudum da sauransu. Sauran sun hada da Gasamu, Garin-Mallam, Gamajan, Sabon Sara, Garin Kunu, Kurkushe, Adiya, Damasa, Yim, Kazir, Gafala, Arfani, Kambawo da garin Daklam duk a karamar hukumar Jakusko da ke jihar Yobe.

Bugu da kari kuma, ambaliyar ruwan ta kai Kwanan Koromari (tsakanin Gashu’a zuwa Bayamari) a karamar hukumar Bursari yayin da take barazana ga kauyuka 10 da ke yankin, wadanda suka hada da Girim Bade, Girim Kanuri, Gilbasu Yamma, Gilbasau Tsakiya, Gilbasau Gabar, Dapso, Garin Kabaju, Guba, Kormari da Kurnawa.

A hannu guda kuma, wannan mummunan ambaliyar ruwan ta shamakance wasu kauyukan da ba za a iya shiga ko fita daga cikinsu ba face sai ta hanyar amfani da jiragen kwale-kwale, wanda suka kunshi Kirikasamma, Awakurari, Damakarwa, Lawan kaltume, Dawai, Buwa, Bulakuwa, Bulanguwa, Goyeri, Daudari, Maladari, Malumma kawuwa, Jajeri, Guluri, Mallari, Karabiri, Kesala, Dalari, Darwo Shilandi, Darwo mariri, Darwo Kakanari da kauyen Darwo Lambowu a karamar hukumar Gaidam.

Wadannan jama’a wadanda ibtila’in ya shafa, suna ci gaba da bayyana bacin ransu bisa ga halin ko-in-kula da gwamnatocin Tarayya da na jihar ke nuna musu kan halin da suke ciki.

Alhaji Kanzi, Mai Unguwar Abujan Amare da ke cikin garin Gashuwa, ya ce al’ummar sa suna cikin mawuyacin hali, “Yau sama da kwana 12 muna bakin jingar tare ruwan nan (babu dare babu rana), amma har yanzu ba mu taba samun tallafin gwamnati ba. Hana rantsuwa Shugaban karamar hukumar Bade ya kawo mana gudumawar 20,000, sai Sarkin Bade, ya ba mu buhun garin-kwaki biyu da fatun buhuna 500.Wannan shi ne iyakacin tallafin da muka samu a wannan lokacin.

“Har wala yau, ambaliyar ruwan ta katse manyan hanyoyin jihar, hanyar da ta tashi daga Gashu’a zuwa Bayamari ta shiga Damaturu, da wadda ta tashi daga Gashu’a zuwa Jakusko ta wuce Potiskum zuwa Damaturu, dole sai ta jiragen kwale-kwale al’amarin da ya tilasta jama’a da sauran ma’aikata da ‘yan kasuwa a yankin zagayawa jihar Jigawa sannan su shiga Damaturu.

Shugaban Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar Yobe (SEMA), Dakta Mohammed Goje ya shaida wa wakilinmu a jihar cewa ambaliyar ta shafi kimanin magidanta 31,000 a cikin garuruwa da kauyuka 255 a kananan hukumomin 17 a jihar Yobe, sannan kuma ta tilasta wa sama da mutane 6,592 zama a sansanin yan gudun hijira, sakamakon rugujewar gidajensu.

Dakta Goje ya kara da cewa, kananan hukumomin Gujba, Gulani, Jakusko,Tarmuwa, Geidam da Bade su ne suka fi sauran fuskantar mummunan kalubalen ambaliyar ruwan, wanda sama da shekara 50 ba a ga irinsa ba a yankin.

 Baya ga rasa rayuka da raunuka ga kimanin mutane sama da 200 hadi da lalata amfanin gonakin dubban jama’a.

A nashi bangaren, Shugaban karamar hukumar Bade, Hon. Sanda Kara-Bade ya bayyana cewa, ambaliyar ruwan ta tagayyara rayuwar jama’a, bsaboda yadda ta rushe gidajensu tare da barnata amfanin gonakin da suka noma. Al’amarin da ya ce dole sai an tashi tsaye wajen tunkarar wannan ibtila’in.

Ya ce, “Saboda haka muna mika sakon godiyarmu ga hukumar SEMA dangane da tallafin da suka bai wa jama’ar da wannan ibtila’in ya shafa. Amma muna kara mika kokon baranmu al’ummarmu ga Gwamnatin Tarayya da ta jihar Yobe su kara kaimi tare da tallafa wa jama’a saboda ana cikin mawuyacin halin gaba kura ba ya sayaki ambaliyar ruwan ta lalata gidaje da gonakin jama’a.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Al'ummaAmbaliyar RuwaAmfanin GonaGeidamGonakiHadejaKogi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Bukatar Samar Wa Kotunan Korafe-korafen Zabe Kudaden Gudanarwa

Next Post

Rundunar ‘Yansanda Ta Kame Mutum 44 Bisa Zargin Aikata Ba Daidai Ba A Adamawa

Related

Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Zai Rattaba Hannu Kan Kudirorin Sauya Fasalin Haraji 4 A Yau Alhamis 

5 hours ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake ÆŠage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Kano Ta Ayyana Ranar Alhamis Hutu Domin Murnar Sabuwar Shekarar Musulunci

15 hours ago
Sojoji
Manyan Labarai

DHQ Za Ta Tura Dakaru Na Musamman 800 Yankunan Da Ke Fama Da Rashin Tsaro – CDS

19 hours ago
Gwamnatin APC Ta Kara Ingiza ‘Yan NIjeriya Cikin Bakin Talauci – PDP
Manyan Labarai

PDP Ta Soke Babban Taronta, Ta Dawo Da Anyanwu A Matsayin Sakatarenta

22 hours ago
KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan ÆŠaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano
Manyan Labarai

KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan ÆŠaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

1 day ago
Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano
Manyan Labarai

Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano

1 day ago
Next Post
Rundunar ‘Yansanda Ta Kame Mutum 44 Bisa Zargin Aikata Ba Daidai Ba A Adamawa

Rundunar 'Yansanda Ta Kame Mutum 44 Bisa Zargin Aikata Ba Daidai Ba A Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Kawayen amarya

Da ÆŠumi-É—umi: ‘Yan Bindiga Sun Ƙwace Iko Da Jagorancin Ƙaramar Hukuma A Katsina

June 26, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Musayar Wuta Tsakanin Sojoji Da ‘Yan Bindiga Ta Ci Rayuka Da Dama A Jihar Neja

June 26, 2025
Tinubu

Tinubu Zai Rattaba Hannu Kan Kudirorin Sauya Fasalin Haraji 4 A Yau Alhamis 

June 26, 2025
Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

June 25, 2025
Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

June 25, 2025
Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya

Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya

June 25, 2025
MSS: Neman Sinawa ‘Yan Leken Asiri Da CIA Ta Yi Tamkar Wasan Ban Dariya Ne

MSS: Neman Sinawa ‘Yan Leken Asiri Da CIA Ta Yi Tamkar Wasan Ban Dariya Ne

June 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake ÆŠage Ranar Komawa Makarantu

Kano Ta Ayyana Ranar Alhamis Hutu Domin Murnar Sabuwar Shekarar Musulunci

June 25, 2025
Gwamnan Jigawa Ya Kaddamar Da Rumbun Sauki Don Sayar Wa Ma’aikata Kayayyakin Abinci A Farashi Mai Rahusa A Sakkwato

Gwamnan Jigawa Ya Kaddamar Da Rumbun Sauki Don Sayar Wa Ma’aikata Kayayyakin Abinci A Farashi Mai Rahusa A Sakkwato

June 25, 2025
Sin Ta Sha Alwashin Rarraba Fasahohinta Na Ainihi Da Dabarunta Na Kirkire-Kirkire Tare Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa

Sin Ta Sha Alwashin Rarraba Fasahohinta Na Ainihi Da Dabarunta Na Kirkire-Kirkire Tare Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa

June 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.