• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar Samar Wa Kotunan Korafe-korafen Zabe Kudaden Gudanarwa

by Leadership Hausa
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Bukatar Samar Wa Kotunan Korafe-korafen Zabe Kudaden Gudanarwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A daidai lokacin dababban zaben kasa na shekarar 2023 ke karatowa, kusan saura wata biyar a halin yanzu. Ana sa ran zuwa yanzu dukkan abubuwan da suka shafi harkar zaben duk an kammala su don tabbatar da gudanar da zaben tare da fuskanta da kuma warware dukkan matsalolin da za su iya tasowa daga zabukan daza a yi.

A kan wannan nemuke matukar damuwa a bisa yadda zuwa yanzu gwamnatin tarayya ba ta samar da kudade ba ga kotuna sauraron kararrakin zaben da ka iya tasowa a zaben 2023, musamman ganin tuni aka kafa kotunana fadin tarayyar kasar nan gaba daya.

  • Firaministan Habasha Ya Kaddamar Da Dakin Adana Kayan Kimiyya Da Fasaha Da Kasar Sin Ta Samar
  • Tinubu Ya Dawo Nijeriya Bayan Shafe Kwanaki 12 A Birtaniya

Bayanin da muka samu ya nuna cewa, shirye-shiryen da suka shafi horas da manyan masu shari’a, shugabannin kotuna na musamman da sauran ma’aikatan kotunan ya tsaya saboda rashin isasashen kudade wanda gwamnati ta kasa samarwa.

Shugaban Kotun Daukaka Kara, ya yi wannan koken inda ya kara da cewa, kotunan musammnan da ake da su a halin yanzu duk sun cinye kudaden da hukumar ta tanada.

Ya kuma sanar da cewa, a halin yanzu babu wani kudi a asusun hukumar da za a iya kafawa tare da gudanar da kotunan sauraron kararrakin zaben. Kotunan sauraron korafe-korafen zabe na da muhimmanci a harkokin gudanar da zabe, su ne ke sauraro korafe-korafen da ke tasowa tun daga lokacin da ake tantance masu kada kuri’a har zuwa lokacin daza a sanar da wanda ya lashe zaben gaba daya.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Nada ÆŠan Babangida A Matsayin Shugaban Bankin Manoma

Sojoji Sun Daƙile Wani Harin Ta’addanci Tare Da Cafke Wasu Mutum Biyu A Taraba

Hakan na da matukar muhimmanci don kare aukuwar rikice-rikicen da ka iya tasowa bayan zabe tare da tabbatar da cikakken zaman lafiya a kasa. Hakki ne na Kotun Daukaka Kara kafa Kotunan sauraron kararrakin zabe, ana kuma kafa su ne tare da la’akari da tanade-tanaden sashi na 285 (2) na kundin tsarin mulkin shekarar1999 (kamar yadda aka yi wa sashi na 9 na dokar kwaskwarima a shekarar 2010).

A ka’ida, Kotun Daukaka Kara ta Tarayyya ce daga ita sai kotun koli a tsarin kotunan Nijeriya. Amma kuma Kotun Daukaka Kara ce ke tsara yadda za a gudanar da shari’un dauka kakara a tsarin shari’ar kasar nan, haka kuma hukumar kula da harkokin shari’a ce ke zabo masu shari’a a wadannan kotunan su mika wa shugaban kasa daga nan kuma majalisar Dattawa ta amince da su.

Dole masu shari’a na kotuna daukaka karar su zama suna da kwarewar gudanar da ayyukansun a Nijeriya sun kuma yi aiki a matsayin masu shari’a a Nijeriya na fiye da shekara 12.

Tsarin mulkin ya kuma tanadi cewa, masu shari’ar za su ajiye aiki in har suka kai shekara 65 a duniya. A saboda haka ya kamata a fahimci cewa, kotunan na da matukar muhimmanci a tsarin gudanar da harkokin dimokradiyya.

Kotunan na bayar da dama ga wanda yake da korafi ya tafi kai tsaye gaban kotun don mika korafinsa don neman a warware masa matsalolin da ya hango a yayin gudanar da zabukka.

Babu wani bangare na gwamnati da ke da irin wannan karfin, wannan alakar yana daga cikin zuciya da ginshikin harkar dimokradiyya. Yana da matukar muhimmanci a fahimci cewa, yin cikakken shiri a dukkan harkokin rayuwa yana tattare ne da isasshen kudi na gudanar da harkokin lamarin.

A saboda haka samar da kudi na da muhimmanci in har ana son kotunan su gudanar da ayyukansu yadda ya kamata. A kan haka muna kira ga hukumomin da ke da ruwa da tsaki da su gaggauta samar da kudaden da suka kamata ga kotunan zabe don a samu nasarar da ya kamata a zaben 2023 da ke tafe.

Tabbatar da tsayayyiyar bangaren shari’a na da matukar muhimmanci ga kokarin tabbatar da aldaci da sahihin zabe a harkar dimokracdiyya, dole a tabbatar da ana yin adalci tare da ganin adalcin a bayyane, kuma hakan ga zai taba yiwu ba har sai an samar wa da bangaren shari’a isasshen kudaden gudanar da aiki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Korafe-KorafeKotunaKudadeZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotu Ta Yanke Wa Wani Mutum Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Kashe Wata Mata A Ebonyi

Next Post

Kogin Kumadugu Ya Yi Ambaliya Karon Farko Cikin Shekara 100 A Yobe

Related

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Ya Nada ÆŠan Babangida A Matsayin Shugaban Bankin Manoma

7 hours ago
Sojoji Sun Daƙile Wani Harin Ta’addanci Tare Da Cafke Wasu Mutum Biyu A Taraba
Manyan Labarai

Sojoji Sun Daƙile Wani Harin Ta’addanci Tare Da Cafke Wasu Mutum Biyu A Taraba

12 hours ago
Buhari 1942 – 2025: Rayuwarsa, Rasuwarsa, Jana’izarsa, Da Ci gaba Da Ta’aziyya
Manyan Labarai

Buhari 1942 – 2025: Rayuwarsa, Rasuwarsa, Jana’izarsa, Da Ci gaba Da Ta’aziyya

17 hours ago
Natasha Ta Rubuta Wa Majalisa, Tana Neman A Yi Biyayya Ga Umarnin Kotu
Manyan Labarai

Natasha Ta Rubuta Wa Majalisa, Tana Neman A Yi Biyayya Ga Umarnin Kotu

1 day ago
Babu Wata Sabuwar Ƙungiyar  Ƴan Ta’adda Mai Suna Fethulla A Nijeriya – DHQ
Tsaro

Babu Wata Sabuwar Ƙungiyar  Ƴan Ta’adda Mai Suna Fethulla A Nijeriya – DHQ

1 day ago
Sojoji Sun Ƙi Karɓar Cin Hancin Miliyan 13 Daga Ƴan Ta’adda A Filato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ƙi Karɓar Cin Hancin Miliyan 13 Daga Ƴan Ta’adda A Filato

1 day ago
Next Post
Kogin Kumadugu Ya Yi Ambaliya Karon Farko Cikin Shekara 100 A Yobe

Kogin Kumadugu Ya Yi Ambaliya Karon Farko Cikin Shekara 100 A Yobe

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.