• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Komawar Ronaldo Saudiyya: Riba Ko Faduwa Ga Al-Nassr?

by Abba Ibrahim Wada
11 months ago
in Wasanni
0
Komawar Ronaldo Saudiyya: Riba Ko Faduwa Ga Al-Nassr?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon dan wasan kungiyar kwallon kafa ta Manchester United, Cristiano Ronaldo, ya bayyana cewa yana ganin a kungiyar kwallon kafa ta Al-Nassr ta kasar Saudiyya zai yi ritaya daga buga kwallo a duniya baki daya. A ranar 30 ga watan Disamban 2022 ne kyaftin din tawagar kasar Portugal.

din, Cristiano Ronaldo ya koma buga wasa a kungiyar Al-Nassr ta Saudiyya kuma ya koma kungiyar ne a kan farashin Fam miliyan 200 duk shekara, wanda shi ne albashi mafi tsoka a kwallon kafa.

  • Ronaldo Ya Jefa Kwallo Biyu Yayin Da Portugal Ta Lallasa Bosnia Da Ci 5-0
  • Ronaldo Ya Fashe Da Kuka Bayan Rashin Nasara A Wasan Ƙarshe

Sai dai tun bayan komawarsa Saudiya masu sharhi a kan harkar suke ci gaba da tattauna nasarar da ya samu da akasin haka inda a ranar Asabar ne 17 ga Agusta ce Al-Hilal ta lallasa Al-Nassr da ci hudu da 1 a wasan Saudi Super Cup.

Ronaldo ne ya fara zuwa kwallo a wasan bayan minti 44, inda magoya bayan kungiyar suka fara murna, kafin daga bisa murnar ta koma ciki kuma hakan na zuwa ne bayan a ranar 1 ga Yuni, Al-Hilal din ta doke Al-Nassr a wasan Kofin Kings Cup, inda Al-Hilal ta yi nasara a bugun fanareti bayan an tashi canjaras.

Bayan an tashi wasan ne fitaccen dan wasan ya fashe da kuka, inda abokan wasansa suka taru a kansa suna ba shi hakuri haka kuma na biyu Al-Nassr ta kare a gasar Sausi Pro League a kakar bara kuma har yanzu kofin da ya ci tun zuwansa kungiyar ita ce Kofin Arab Club ta kakar bara.

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

Ganin yadda Al-Hilal ke ci gaba da kaka-gida a wasan kwallon Saudiyyar ce ya sa ake ganin shin akwai amfanin da zuwan Ronaldo ya yi wa Al-Nassr?

A bangaren zura kwallaye ba a cewa komai, domin a kakar bara ya kafa tarihin cin kwallaye a gasar, inda ya zura kwallo 35 a kaka daya, inda ya karya tarihin Abderrazak Hamdallah, wanda ya taba zura kwallo 34 a kakar 2028-2019. Zuwa yanzu, dan wasan na zura kwallo 67, ya taimaka an ci kwallo 16 a wasa 73 da ya buga wa kungiyar ta Al-Nassr. Ke nan za a iya cewa a

matakinsa da dan wasa, ya ci kwallaye, kuma ya nuna bajinta, sai dai duk kungiyar da ya buga wa kwallo ya lashe kofi, ciki har da Sporting CP, inda ya faro a Portugal.

Sai dai yadda Al-Nassr din ba ta lashe kofuna sosai, sai wasu ke diga alamar tambaya a kan nasarar da ya samu a kungiyar domin kafin komawarsa Al-Nassr, Ronaldo ya lashe kofuna da dama a kungiyoyin da ya buga wasa, kamar Manchester United, da Real Madrid, inda ya fi lashe kofuna.

Sannan ya lashe kofuna a kungiyar Jubentus, inda ya je kafin ya koma Saudiyya. Babban dalilin da ya sa kungiyar Al-Nassr ta dauki dan wasa Ronaldo shi ne cin kofi sannan zuwansa zai taimaka wajen ganin wasu ‘yan wasan sun shiga kungiyar, kamar yadda daga baya irinsu Sadio Mane da Aled Telles suka bishi kungiyar.

Sai dai kuma kungiyar Al-Hilal tana da matukar tasiri a kwallon kafa a Saudiyya, sannan ta dauki zakakuran ‘yan wasa daga Nahiyar Turai sama da wadanda Al-Nassr ta dauka wanda hakan ya sa take ci gaba da jan zarenta.

Sai dai har yanzu akwai jan aiki a gaban kungiyar Al-Nassr wajen ganin ta sha gaban kungiyar Al-Hilal musamman lashe kofunan kasar Saudiyya tare kuma da mamaye gasar kasar Saudiyya kamar yadda Al-Hilar ta yi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AlnassarFIFARonaldoSaudiyya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Nijar Za Ta Fara Tattara Bayanan ‘Yan Ta’adda

Next Post

Hamas: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Isra’ila Saboda Ƙin Amincewar Ƙasar Kan Tsagaita Buɗe Wuta

Related

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

53 minutes ago
WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe
Wasanni

WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

12 hours ago
Zan Ci Gaba da Taka Leda A Kano Pillars Duk da Matsayin Da Na Samu — Ahmed Musa
Wasanni

Zan Ci Gaba da Taka Leda A Kano Pillars Duk da Matsayin Da Na Samu — Ahmed Musa

3 days ago
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu
Wasanni

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu

4 days ago
Oshoala Za Ta Yi Ritaya Daga Buga Wa Nijeriya Ƙwallo
Wasanni

Oshoala Za Ta Yi Ritaya Daga Buga Wa Nijeriya Ƙwallo

5 days ago
Rashford Na Dab Da Komawa Barcelona A Matsayin Aro
Wasanni

Rashford Na Dab Da Komawa Barcelona A Matsayin Aro

5 days ago
Next Post
Hamas: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Isra’ila Saboda Ƙin Amincewar Ƙasar Kan Tsagaita Buɗe Wuta

Hamas: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Isra'ila Saboda Ƙin Amincewar Ƙasar Kan Tsagaita Buɗe Wuta

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

July 26, 2025
Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

July 26, 2025
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

July 26, 2025
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

July 26, 2025
Ronaldo

Natijojin Auren Dattijo Ga Budurwa

July 26, 2025
An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

July 26, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)

Dalilan Da Suka Sa Cinikin Bayi Bai Yi Nasara A Arewacin Nijeriya Ba

July 26, 2025
Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko

Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko

July 26, 2025
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.