• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Korafin Dogara Kan Yunkurin Kasheshi: Muna Kan Bincike Ne Har Yanzu, Amma Mun Kama Mutum Biyu – Kwamishinan ‘Yansanda

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Dogara
  • Tunin Muka Kaddamar Da Bincike Kan Bacewar Bindigoginmu, In Ji Shi
  • Wai Me Kwamishinan Ke Boyewa – Dogara Ya Tambaya

Kwamishinan ‘Yansandan Jihar Bauchi Umar Mamman Sanda, ya bayyana cewar tunin suka maida hankali wajen gudanar da bincike kan ikirarin da wani ya yi na cewa zai kashe tsohon Kakakin Majalisar wakilai ta tarayya, Rt. Hon. Yakubu Dogara da wasu mutum uku.

Kan hakan, kwamishinan ya ce suna gudanar da ayyukansu ne yadda ya dace kuma za su fitar da hakikanin abun da ya faru. Sai dai ya nuna cewa ba su tabbatar da cewa rayuwar Dogaran na cikin hatsari ba, illa dai sun kama wanda ya furta cewa zai sayi bindiga ne don kashe Dogaran tare da dan sandan da ya saci bindigar da nufin saidawa mutumin.

  • Rayuwata Na Cikin Hatsari, Ana Kokarin Kashe Ni – Yakubu Dogara

Kwamishinan wanda ke maida bayani kan wasikar korafi da Yakubu Dogara ya aike wa Shugaban ‘yansanda na kasa Usman Baba Alkali inda ke shaida masa cewar rayuwarsa na cikin hatsari domin wani mai suna Barau Joel Amos na son sayan bindigogi a hannun wasu ‘yan sanda Insifekta Dakat Samuel da Insifekta Auwalu Mohammed domin ya kasheshi shi da wasu mutum uku.

Sauran wadanda Amos ke son kashewa a vewar Dogara har da shugaban CAN na karamar hukumar Tafawa Balewa, Rabaran Markus Musa, Barr. Istifanus Bala Gambar da wani Mr. Emmanuel (Shugaban NL, na T/Balewa).

Said dai kwamishinan ‘yansandan ya ce: “Abun da ya faru shine mun samu bayanai na sirri cewa lallai akwai wani dan sandanmu da yake son zai sayar da bindiga. Sai muka je muka nemoshi daman an ba mu labarin cewa har ya sanya bindigun a cikin motarsa, sai muka je muka sameshi muka ce waye mai motar ya ce shi ne, muka binciki motar muka samu bindigogi.

LABARAI MASU NASABA

Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya

Haramcin Haƙar Ma’adanai: Majalisa Za Ta Kawo Ƙarshen Asarar Dala Biliyan 9 Duk Shekara

“Aka tambayeshi waye ya baka bindigogin ya ce ya dauko ne zai sayar. Bindigogin ‘yansandan za ka sayar? Ya ce eh. Muka kamashi muka fara bincike, a cikin binciken ya kama sunan wani dan uwansa wanda suke wuri daya. Shi wanda muka kaman da farko ya bamu labari ya ce mana wani mutum ne dan can yankin Tafawa Balewa shi ne yake so ya sayi bindiga shi ya sanya ya dauko masa bindigogi, ya fada mana waye sai muka je muka kamo wancan din.

“Da muka kama shi (na biyun) shi ma muka ce ya aka yi ya ce gaskiya ne yana neman bindiga ne saboda gaskiya wani abun al’ajabi ya sameshi akwai dan tarzomar da ya tashi a can wajajen Tafawa Balewa, Bogoro a kan kaddamar da littafin da aka rubuta na Baba Gwanto a watan Disamban da ya gabata an kona masa gidaje da na sauran jama’a.

“An kona maka gidaje shine meye? Ya ce a’a ai su Dogara da wadansu mutane ne, shi ya sa yake neman bindiga don ya kashesu.”

“Ka san ba kasafai ne idan dan adam ya yi laifi zai fito ya fada maka gaskiyar abun da ya yi ba, sai ka masa ‘yan hikima kafin nan sai gaskiyar ta fito. Bayan da aka yi haka din mun kaddamar da bincike a kan wannan batun.”

Kwamishinan ya kuma ce, bayan hakan ma kan batar bindigoginsu nan take ya bada umarnin cewa dukkanin wuraren ajiye makamansu a je a kirga musu makamai a bincika menene babu, “Sai muka samu bayan wadannan bindigogi biyun da muka kama wasu ma babu su sun bata. Nan fa bincike ya fadada. A yanzu maganar da nake maka akwai mai kula da wajen ajiye makamanmu wanda ya yi ritaya shekaru biyu zuwa uku da suka wuce a shekarar jiya (ranar Juma’a) aka kamashi domin mun yi ta nemansa ba mu sameshi ba.

“Na ce shi ma a kulleshi, muna nan muna kan bincike kwatsam kawai sai muka ga shi (Dogara) ya rubutu wasika. Har yana zargin cewa ba mu kirashi mun gaya mishi ba, ba mu tabbatar ba, bayan maganar da shi wannan mutumin ya yi ba mu sake samun wani tabbacin lallai cewa rayuwarsa (Dogara) na cikin barazana ba, ko kuma wannan bindigar da aka sayen an yi ne saboda a kasheshi ba, wannan babu tabbaci a cikinsa. Kuma mu ba za mu fito mu yi magana wa duniya ce ga abun da ke akwai ba kuma ya zo daga baya bincike ya nuna mana ba haka yake ba.

“Saboda haka wannan magaanar ba daidai ba ne kuma mu ‘yansanda muna nan muna cigaba da bincikenmu za mu yi bayani wa jama’a idan muka kammala bincikenmu. Babu wani abun boyewa a ciki,” a cewar kwamishinan.

Umar Mamman Sanda ya ce hatta zuwa ga wannan matakin ma bisa kokarinsu da jajircewarsu ne aka kawo ga wannan, in ba haka ba ma ai ba za mu sani ba.

Kwamishinan ya nemi jama’a da su ba su lokaci domin su kammala bincike tare da fito da bayanin hakikan abubuwan da suka faru.

Kwamishinan ya ce karar da Yakubu Dogara ya kai wajen shugaban ‘yansandan na kasa ba matsala ba ne, amma bai kamata ya nuna cewa su ‘yansandan a jihar Bauchi ba su yi abun da kamata ba ba daidai bane domin har yanzu suna bincike kan bayanin da suka samu da yadda za su tabbatar da shi, “Bayani ne muka samu daga wajen mutum daya, kuma babu wani mutum ko wasu da muka samu suka tababtar mana da wannan maganar cewa lallai a hakan take.

“Sai mun bai wa wasu kwararrunmu wadanda suke bincike a kan maganar bindigogi da maganar kashe mutane su ne za su gaya mana cewa eh lallai wannan maganar haka ne kuma an samu wane da wane a ciki sai mu fito mu fada wa duniya mu yi bayani ga abun da ke akwai, ko shi kansa (Dogara) ba mu kai ga inda za mu tambaya ko akwai wani barazana da ya gani a rayuwarsa kafin wannan abun don mu mu sani sannan mu fito da bayananmu na bincike,” kwamishinan ya karkare.

A gefe guda kuma Yakubu Dogara ya nuna mamakinsa kan yadda kwamishinan da kansa ya tabbatar da cewa sun kama dan sanda guda da bindigogi da yake kokarin sayarwa da kuma wanda suka kama da ya shaida da bakinsa cewa na son sayen bindiga ne don ya kashe shine amma kuma hakan bai zama hujja da zai tabbatar rayuwar tasa na cikin hatsari ba.

Dogaran ta bakin kakakinsa Turaki Hassan ya yi tambaya da cewa, “Akwai wata hujjar da ta wuce wanda ake zargi da kansa ya bayyana batu da bakinsa? Wai meye kwamishinan yake kokarin rufewa ne?.

Ya kuma sake yin tambayar cewa don meye kwamishinan bai bayyana wanda suka cafke da bisa zargin kamasa da bindigogin ba.?

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya
Labarai

Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya

October 10, 2025
Nijeriya
Labarai

Haramcin Haƙar Ma’adanai: Majalisa Za Ta Kawo Ƙarshen Asarar Dala Biliyan 9 Duk Shekara

October 10, 2025
Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

October 10, 2025
Next Post
Masu Garkuwa Da Mutane Sun Shiga Komar ‘Yansanda, An Ceto Wadanda Suka Sace A Delta 

Masu Garkuwa Da Mutane Sun Shiga Komar 'Yansanda, An Ceto Wadanda Suka Sace A Delta 

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  

Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  

October 10, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

2027: INEC Ta Nemi A Gaggauta Amincewa Da Ƙudirin Sake Fasalin Tsarin Zaɓe

October 10, 2025
Sin Ta Gabatar Da Shawarwari Shida Game Da Karfafa Tsarin Shari’a Da Inganta Shugabanci A Duniya

Sin Ta Gabatar Da Shawarwari Shida Game Da Karfafa Tsarin Shari’a Da Inganta Shugabanci A Duniya

October 10, 2025
Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya

Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya

October 10, 2025
Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa

Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa

October 10, 2025
An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi 

An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi 

October 10, 2025
Nijeriya

Haramcin Haƙar Ma’adanai: Majalisa Za Ta Kawo Ƙarshen Asarar Dala Biliyan 9 Duk Shekara

October 10, 2025
Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

October 10, 2025
Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)

Yadda Za A Magance Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya – TRCN

October 10, 2025
Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

October 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.