• English
  • Business News
Friday, August 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Korafin Dogara Kan Yunkurin Kasheshi: Muna Kan Bincike Ne Har Yanzu, Amma Mun Kama Mutum Biyu – Kwamishinan ‘Yansanda

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
Korafin Dogara Kan Yunkurin Kasheshi:  Muna Kan Bincike Ne Har Yanzu, Amma Mun Kama Mutum Biyu – Kwamishinan ‘Yansanda
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram
  • Tunin Muka Kaddamar Da Bincike Kan Bacewar Bindigoginmu, In Ji Shi
  • Wai Me Kwamishinan Ke Boyewa – Dogara Ya Tambaya

Kwamishinan ‘Yansandan Jihar Bauchi Umar Mamman Sanda, ya bayyana cewar tunin suka maida hankali wajen gudanar da bincike kan ikirarin da wani ya yi na cewa zai kashe tsohon Kakakin Majalisar wakilai ta tarayya, Rt. Hon. Yakubu Dogara da wasu mutum uku.

Kan hakan, kwamishinan ya ce suna gudanar da ayyukansu ne yadda ya dace kuma za su fitar da hakikanin abun da ya faru. Sai dai ya nuna cewa ba su tabbatar da cewa rayuwar Dogaran na cikin hatsari ba, illa dai sun kama wanda ya furta cewa zai sayi bindiga ne don kashe Dogaran tare da dan sandan da ya saci bindigar da nufin saidawa mutumin.

  • Rayuwata Na Cikin Hatsari, Ana Kokarin Kashe Ni – Yakubu Dogara

Kwamishinan wanda ke maida bayani kan wasikar korafi da Yakubu Dogara ya aike wa Shugaban ‘yansanda na kasa Usman Baba Alkali inda ke shaida masa cewar rayuwarsa na cikin hatsari domin wani mai suna Barau Joel Amos na son sayan bindigogi a hannun wasu ‘yan sanda Insifekta Dakat Samuel da Insifekta Auwalu Mohammed domin ya kasheshi shi da wasu mutum uku.

Sauran wadanda Amos ke son kashewa a vewar Dogara har da shugaban CAN na karamar hukumar Tafawa Balewa, Rabaran Markus Musa, Barr. Istifanus Bala Gambar da wani Mr. Emmanuel (Shugaban NL, na T/Balewa).

Said dai kwamishinan ‘yansandan ya ce: “Abun da ya faru shine mun samu bayanai na sirri cewa lallai akwai wani dan sandanmu da yake son zai sayar da bindiga. Sai muka je muka nemoshi daman an ba mu labarin cewa har ya sanya bindigun a cikin motarsa, sai muka je muka sameshi muka ce waye mai motar ya ce shi ne, muka binciki motar muka samu bindigogi.

Labarai Masu Nasaba

Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta, Sun Kashe Ƴan Ta’adda A Borno

Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu

“Aka tambayeshi waye ya baka bindigogin ya ce ya dauko ne zai sayar. Bindigogin ‘yansandan za ka sayar? Ya ce eh. Muka kamashi muka fara bincike, a cikin binciken ya kama sunan wani dan uwansa wanda suke wuri daya. Shi wanda muka kaman da farko ya bamu labari ya ce mana wani mutum ne dan can yankin Tafawa Balewa shi ne yake so ya sayi bindiga shi ya sanya ya dauko masa bindigogi, ya fada mana waye sai muka je muka kamo wancan din.

“Da muka kama shi (na biyun) shi ma muka ce ya aka yi ya ce gaskiya ne yana neman bindiga ne saboda gaskiya wani abun al’ajabi ya sameshi akwai dan tarzomar da ya tashi a can wajajen Tafawa Balewa, Bogoro a kan kaddamar da littafin da aka rubuta na Baba Gwanto a watan Disamban da ya gabata an kona masa gidaje da na sauran jama’a.

“An kona maka gidaje shine meye? Ya ce a’a ai su Dogara da wadansu mutane ne, shi ya sa yake neman bindiga don ya kashesu.”

“Ka san ba kasafai ne idan dan adam ya yi laifi zai fito ya fada maka gaskiyar abun da ya yi ba, sai ka masa ‘yan hikima kafin nan sai gaskiyar ta fito. Bayan da aka yi haka din mun kaddamar da bincike a kan wannan batun.”

Kwamishinan ya kuma ce, bayan hakan ma kan batar bindigoginsu nan take ya bada umarnin cewa dukkanin wuraren ajiye makamansu a je a kirga musu makamai a bincika menene babu, “Sai muka samu bayan wadannan bindigogi biyun da muka kama wasu ma babu su sun bata. Nan fa bincike ya fadada. A yanzu maganar da nake maka akwai mai kula da wajen ajiye makamanmu wanda ya yi ritaya shekaru biyu zuwa uku da suka wuce a shekarar jiya (ranar Juma’a) aka kamashi domin mun yi ta nemansa ba mu sameshi ba.

“Na ce shi ma a kulleshi, muna nan muna kan bincike kwatsam kawai sai muka ga shi (Dogara) ya rubutu wasika. Har yana zargin cewa ba mu kirashi mun gaya mishi ba, ba mu tabbatar ba, bayan maganar da shi wannan mutumin ya yi ba mu sake samun wani tabbacin lallai cewa rayuwarsa (Dogara) na cikin barazana ba, ko kuma wannan bindigar da aka sayen an yi ne saboda a kasheshi ba, wannan babu tabbaci a cikinsa. Kuma mu ba za mu fito mu yi magana wa duniya ce ga abun da ke akwai ba kuma ya zo daga baya bincike ya nuna mana ba haka yake ba.

“Saboda haka wannan magaanar ba daidai ba ne kuma mu ‘yansanda muna nan muna cigaba da bincikenmu za mu yi bayani wa jama’a idan muka kammala bincikenmu. Babu wani abun boyewa a ciki,” a cewar kwamishinan.

Umar Mamman Sanda ya ce hatta zuwa ga wannan matakin ma bisa kokarinsu da jajircewarsu ne aka kawo ga wannan, in ba haka ba ma ai ba za mu sani ba.

Kwamishinan ya nemi jama’a da su ba su lokaci domin su kammala bincike tare da fito da bayanin hakikan abubuwan da suka faru.

Kwamishinan ya ce karar da Yakubu Dogara ya kai wajen shugaban ‘yansandan na kasa ba matsala ba ne, amma bai kamata ya nuna cewa su ‘yansandan a jihar Bauchi ba su yi abun da kamata ba ba daidai bane domin har yanzu suna bincike kan bayanin da suka samu da yadda za su tabbatar da shi, “Bayani ne muka samu daga wajen mutum daya, kuma babu wani mutum ko wasu da muka samu suka tababtar mana da wannan maganar cewa lallai a hakan take.

“Sai mun bai wa wasu kwararrunmu wadanda suke bincike a kan maganar bindigogi da maganar kashe mutane su ne za su gaya mana cewa eh lallai wannan maganar haka ne kuma an samu wane da wane a ciki sai mu fito mu fada wa duniya mu yi bayani ga abun da ke akwai, ko shi kansa (Dogara) ba mu kai ga inda za mu tambaya ko akwai wani barazana da ya gani a rayuwarsa kafin wannan abun don mu mu sani sannan mu fito da bayananmu na bincike,” kwamishinan ya karkare.

A gefe guda kuma Yakubu Dogara ya nuna mamakinsa kan yadda kwamishinan da kansa ya tabbatar da cewa sun kama dan sanda guda da bindigogi da yake kokarin sayarwa da kuma wanda suka kama da ya shaida da bakinsa cewa na son sayen bindiga ne don ya kashe shine amma kuma hakan bai zama hujja da zai tabbatar rayuwar tasa na cikin hatsari ba.

Dogaran ta bakin kakakinsa Turaki Hassan ya yi tambaya da cewa, “Akwai wata hujjar da ta wuce wanda ake zargi da kansa ya bayyana batu da bakinsa? Wai meye kwamishinan yake kokarin rufewa ne?.

Ya kuma sake yin tambayar cewa don meye kwamishinan bai bayyana wanda suka cafke da bisa zargin kamasa da bindigogin ba.?


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasurgumin Dan Bindiga ‘Bello Turji’ Ya Rungumi Zaman Lafiya, Ya Koma Yakar ‘Yan Bindiga – Gwamnati

Next Post

Masu Garkuwa Da Mutane Sun Shiga Komar ‘Yansanda, An Ceto Wadanda Suka Sace A Delta 

Related

Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta, Sun Kashe Ƴan Ta’adda A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta, Sun Kashe Ƴan Ta’adda A Borno

42 minutes ago
Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu
Ra'ayi Riga

Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu

2 hours ago
Ba Gaskiya Ba Ne Rahoton Da Ke Cewa An Yi Sulhu Da Bello Turji – Guyawa Isa
Labarai

Ba Gaskiya Ba Ne Rahoton Da Ke Cewa An Yi Sulhu Da Bello Turji – Guyawa Isa

4 hours ago
Tashin Gurneti Ya Hallaka Yara Uku A Borno
Labarai

Tashin Gurneti Ya Hallaka Yara Uku A Borno

5 hours ago
Yara Uku Sun Gamu Da Ajalinsu A Wani Tafki A Borno
Labarai

Yara Uku Sun Gamu Da Ajalinsu A Wani Tafki A Borno

7 hours ago
Jirgin Shugaban Ƙasa Ya Laƙume Naira Biliyan 26.38 Cikin Wata 18 Ƙarƙashin Tinubu
Labarai

Jirgin Shugaban Ƙasa Ya Laƙume Naira Biliyan 26.38 Cikin Wata 18 Ƙarƙashin Tinubu

9 hours ago
Next Post
Masu Garkuwa Da Mutane Sun Shiga Komar ‘Yansanda, An Ceto Wadanda Suka Sace A Delta 

Masu Garkuwa Da Mutane Sun Shiga Komar 'Yansanda, An Ceto Wadanda Suka Sace A Delta 

LABARAI MASU NASABA

Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta, Sun Kashe Ƴan Ta’adda A Borno

Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta, Sun Kashe Ƴan Ta’adda A Borno

August 8, 2025
UEFA Ta Ci Tarar Lamine Yamal Da Lewandowski Kan Karya Dokar Shan Ƙwayar Ƙara Kuzari

UEFA Ta Ci Tarar Lamine Yamal Da Lewandowski Kan Karya Dokar Shan Ƙwayar Ƙara Kuzari

August 8, 2025
Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu

Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu

August 8, 2025
Ba Gaskiya Ba Ne Rahoton Da Ke Cewa An Yi Sulhu Da Bello Turji – Guyawa Isa

Ba Gaskiya Ba Ne Rahoton Da Ke Cewa An Yi Sulhu Da Bello Turji – Guyawa Isa

August 8, 2025
Tashin Gurneti Ya Hallaka Yara Uku A Borno

Tashin Gurneti Ya Hallaka Yara Uku A Borno

August 8, 2025
Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji

Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji

August 8, 2025
GORON JUMA’A 8-8-2025

GORON JUMA’A 8-8-2025

August 8, 2025
Yara Uku Sun Gamu Da Ajalinsu A Wani Tafki A Borno

Yara Uku Sun Gamu Da Ajalinsu A Wani Tafki A Borno

August 8, 2025
Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (1)

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (1)

August 8, 2025
Jirgin Shugaban Ƙasa Ya Laƙume Naira Biliyan 26.38 Cikin Wata 18 Ƙarƙashin Tinubu

Jirgin Shugaban Ƙasa Ya Laƙume Naira Biliyan 26.38 Cikin Wata 18 Ƙarƙashin Tinubu

August 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.