• English
  • Business News
Saturday, August 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Bayar Da Belin Emefiele Kan Miliyan 20

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Kotu Ta Bayar Da Belin Emefiele Kan Miliyan 20
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mai shari’a Nicholas Oweibo na babbar kotun tarayya da ke Legas, ya bayar da belin gwamnan babban bankin Nijeriya (CBN) da aka dakatar, Godwin Emefiele a kan kudi naira miliyan 20.

Ana tuhumar Emefiele bisa tuhume-tuhume biyu da suka hada da mallakar bindiga da harsasai 123 ba tare da lasisi ba.

  • An Gurfanar Da Emefiele A Kotu Kan Mallakar Makamai Ba Bisa Ka’ida Ba
  • ‘Yansanda Sun Cafke ‘Yan Boko Haram Kan Zargin Shirin Kai Hari Gidan Atiku

Sai dai Emefiele ya musanta zargin da ake masa.

Bayan karar da ya shigar, lauyan wanda ake kara, Mista Joseph Daudu, SAN, wanda ya jagoranci wasu manyan lauyoyi hudu, ya sanar da kotun bukatar neman belin wanda ake karewa.

Lauya Dedence ya shaida wa kotun cewa an tsare wanda ake tuhumar ba bisa ka’ida ba.

Labarai Masu Nasaba

Farashin Kayayyaki A Nijeriya Sun Sauka Zuwa Kashi 21.88%

Sojoji Sun Ceto Shugaban Fulani, Mutane 5 Daga Hannun Ƴan Bindiga A Kogi

Sai dai mai gabatar da kara, Misis N.B Jones, ta ki amincewa da neman bayar belin Emefiele kan hujjar cewa ba a ba ta kwafin takardar bukatar belin nasa ba.

A hukuncin da ya yanke, Mai shari’a Oweibo ya amince da bukatar lauyoyin kan hujjar cewa laifin da ake tuhumar ake yi wa Emefiele bai cancanci a tsare shi na tsawon wannan lokaci ba.

Kotun ta ce ba za a hana belinsa ba duba da sashe na 162 na kundin dokar laifuka.

Saboda haka, kotun ta bayar da belin wanda ake kara a kan kudi Naira miliyan 20 tare da gabatar da mutum daya da zai tsaya masa.

Kotun ta yanke hukuncin cewa wanda zai tsaya masa dole ne ya bayar da wata takardar shaida kuma ya kasance yana da adadin kudin da aka bayar da belin a kasa.

Ya bukaci da a ci gaba da tsare wanda ake kara a gidan yari har sai an cika sharudan belin.

Kotun ta dage sauraren karar har zuwa ranar 14 ga watan Nuwamba.

Tun da fari, hukumar tsaro ta farin kaya (DSS), ta gurfanar da Emefiele a gaban kotu kan zargin mallakar makamai ba bisa ka’ida ba.

Laifin da ta ce ya ci karo da tanadin sashe na 4 da 8 na dokar mallakar mallamai na 2004.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BeliDSSEmefieleKotuMallakar Makamai
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Gurfanar Da Emefiele A Kotu Kan Mallakar Makamai Ba Bisa Ka’ida Ba

Next Post

DSS Ta Sake Kama Emefiele Bayan Bayar Da Belinsa —Lauyoyi

Related

Farashin Kayayyaki A Nijeriya Sun Sauka Zuwa Kashi 21.88%
Manyan Labarai

Farashin Kayayyaki A Nijeriya Sun Sauka Zuwa Kashi 21.88%

9 hours ago
Sojoji Sun Ceto Shugaban Fulani, Mutane 5 Daga Hannun Ƴan Bindiga A Kogi
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Shugaban Fulani, Mutane 5 Daga Hannun Ƴan Bindiga A Kogi

13 hours ago
An Taƙaita Zirga-Zirga A Ƙananan Hukumomi 4 Kafin Zaben Cike Gurbi A Kano
Labarai

An Taƙaita Zirga-Zirga A Ƙananan Hukumomi 4 Kafin Zaben Cike Gurbi A Kano

14 hours ago
Shugaba Tinubu Ya Naɗa Sabon Darakta-Janar Na NTA Da Wasu Daraktoci
Manyan Labarai

Shugaba Tinubu Ya Naɗa Sabon Darakta-Janar Na NTA Da Wasu Daraktoci

16 hours ago
Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa
Manyan Labarai

Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa

17 hours ago
Matsalar Shugabanci A Jihohi Ke Haifar Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki Ga Yara
Manyan Labarai

Matsalar Shugabanci A Jihohi Ke Haifar Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki Ga Yara

18 hours ago
Next Post
DSS Ta Sake Kama Emefiele Bayan Bayar Da Belinsa —Lauyoyi

DSS Ta Sake Kama Emefiele Bayan Bayar Da Belinsa —Lauyoyi

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi: Ya Kamata A Mutunta Tarihi Domin Magance Sake Yin Kuskure

Wang Yi: Ya Kamata A Mutunta Tarihi Domin Magance Sake Yin Kuskure

August 15, 2025
An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

August 15, 2025
Ya Kamata A Yi Wa Japan Jinyar Cutar “Mantuwar Tarihi”

Ya Kamata A Yi Wa Japan Jinyar Cutar “Mantuwar Tarihi”

August 15, 2025
Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

August 15, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Bikin Mu’amalar Al’adu Da Jama’a A Hedkwatar MDD

CMG Ya Kaddamar Da Bikin Mu’amalar Al’adu Da Jama’a A Hedkwatar MDD

August 15, 2025
Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa

Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa

August 15, 2025
Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya

Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya

August 15, 2025
Gasar Wasannin Mutum Mutumin Inji Ta Duniya Ta 2025 Na Gabatar Da Sabbin Fasahohin Zamani

Gasar Wasannin Mutum Mutumin Inji Ta Duniya Ta 2025 Na Gabatar Da Sabbin Fasahohin Zamani

August 15, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Babu Dalilin Da Zai Sa ‘Yan Nijeriya Su Yi Talauci – Tinubu

August 15, 2025
Tattalin Arzikin Sin Ya Bunkasa Yadda Ya Kamata A Watan Yuli

Tattalin Arzikin Sin Ya Bunkasa Yadda Ya Kamata A Watan Yuli

August 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.