ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Bayar Da Belin Emefiele Kan Miliyan 20

by Sadiq
3 years ago
Emefiele

Mai shari’a Nicholas Oweibo na babbar kotun tarayya da ke Legas, ya bayar da belin gwamnan babban bankin Nijeriya (CBN) da aka dakatar, Godwin Emefiele a kan kudi naira miliyan 20.

Ana tuhumar Emefiele bisa tuhume-tuhume biyu da suka hada da mallakar bindiga da harsasai 123 ba tare da lasisi ba.

  • An Gurfanar Da Emefiele A Kotu Kan Mallakar Makamai Ba Bisa Ka’ida Ba
  • ‘Yansanda Sun Cafke ‘Yan Boko Haram Kan Zargin Shirin Kai Hari Gidan Atiku

Sai dai Emefiele ya musanta zargin da ake masa.

ADVERTISEMENT

Bayan karar da ya shigar, lauyan wanda ake kara, Mista Joseph Daudu, SAN, wanda ya jagoranci wasu manyan lauyoyi hudu, ya sanar da kotun bukatar neman belin wanda ake karewa.

Lauya Dedence ya shaida wa kotun cewa an tsare wanda ake tuhumar ba bisa ka’ida ba.

LABARAI MASU NASABA

Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Sai dai mai gabatar da kara, Misis N.B Jones, ta ki amincewa da neman bayar belin Emefiele kan hujjar cewa ba a ba ta kwafin takardar bukatar belin nasa ba.

A hukuncin da ya yanke, Mai shari’a Oweibo ya amince da bukatar lauyoyin kan hujjar cewa laifin da ake tuhumar ake yi wa Emefiele bai cancanci a tsare shi na tsawon wannan lokaci ba.

Kotun ta ce ba za a hana belinsa ba duba da sashe na 162 na kundin dokar laifuka.

Saboda haka, kotun ta bayar da belin wanda ake kara a kan kudi Naira miliyan 20 tare da gabatar da mutum daya da zai tsaya masa.

Kotun ta yanke hukuncin cewa wanda zai tsaya masa dole ne ya bayar da wata takardar shaida kuma ya kasance yana da adadin kudin da aka bayar da belin a kasa.

Ya bukaci da a ci gaba da tsare wanda ake kara a gidan yari har sai an cika sharudan belin.

Kotun ta dage sauraren karar har zuwa ranar 14 ga watan Nuwamba.

Tun da fari, hukumar tsaro ta farin kaya (DSS), ta gurfanar da Emefiele a gaban kotu kan zargin mallakar makamai ba bisa ka’ida ba.

Laifin da ta ce ya ci karo da tanadin sashe na 4 da 8 na dokar mallakar mallamai na 2004.

MASU ALAKA

Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
Manyan Labarai

Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

June 5, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Next Post
DSS Ta Sake Kama Emefiele Bayan Bayar Da Belinsa —Lauyoyi

DSS Ta Sake Kama Emefiele Bayan Bayar Da Belinsa —Lauyoyi

LABARAI MASU NASABA

Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

June 5, 2026
Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.