• English
  • Business News
Saturday, August 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Daure Hadimin Tambuwal Kan Yada Bidiyon Da Ake Wa Matar Gwamna Liki Da Dala

by Abubakar Sulaiman
12 months ago
in Labarai
0
Kotu Ta Daure Hadimin Tambuwal Kan Yada Bidiyon Da Ake Wa Matar Gwamna Liki Da Dala
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kotun majistare ta daya da ke Sakkwato a yau ta tura mataimaki na musamman ga Sanata Aminu Waziri Tambuwal kan yada labarai, Shafi’u Umar Tureta a gidan gyaran hali a bisa ga yada bidiyon matar Gwamna Ahmed Aliyu a yayin da ake yi mata liki da Dala.

Mai Shari’a Fatima Hassan ta daga zaman kotun kan hukuncin da za a yi kan dan shekaru 36 zuwa ranar 6 ga Satumba da za a yanke shawarar bayar da belinsa kan laifin batanci. Sai dai duk kokarin manema labarai na halartar zaman kotun ya faskara kansancewar an haramta musu shiga.

  • Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
  • Kotu Ta Ɗaure Hadimin Tambuwal Kan Yaɗa Bidiyon Da Ake Yi Wa Matar Gwamnan Sakkwato Liƙi Da Dala

Mai shigar da kara ta bayyana bayyanan a ranar 18/7/2023 cewa ya yada bidiyon matar Gwamna, Fatima Ahmed Aliyu a yayin da take bukin zagayowar ranar haihuwarta tare da cewar ta na almubbazaranci a liki da kashe kudin a yayin da al’umma ke a cikin yunwa.

Laifi na biyu da aka tuhumi shafukan shi ne sanya tsohuwar takardar kammala makarantar sakandiren Gwamna da sakamakon F9 tare da kiran sa bakauye bai iya magana da turanci ba, lamarin da dansanda mai shigar da kara Abdurrahman Mansur ya ce sun saba wa kundin dokar penal code ta jihar ta 2019 sashe na 378 da 379.

Sai dai jam’iyyar PDP a jihar ta ce ba Shafi’u ne ya dauki bidiyon da Gwamna ke turanciin ba don ba ya da damar shiga gidan gwamnati inda aka dauki bidiyon haka ma bai halarci bikin zagayowar ranar haihuwar matar gwamnan ba don haka ba inda zai same su idan ba yaran gwamnan da taimakonsa ne suka yada ba.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa

Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya

Kakakin jam’iyyar, Hassan Sahabi Sanyinnawal ya bayyana mulkin kama – karya ne jaridun Sakkwato ke yi tare da kokarin cin zarafin ‘yan adawa ko ‘yan PDP, domin hakan rashin adalci ne kuma ba za su zuba ido a na nuna wa magoya bayan su ba.

A nata bangaren kungiyar kare hakkin zan’adam ta Amnesty International ta bi sahun wadanda suka soki lamarin, ta ce kama hotunan ya sabawa ‘yancinsa na dan’adam don haka ta yi Allah – wadai da kamen tare da kiran a gaggauta sakin sa.

Kungiyar ta ce maimakon kama marubucin wanda ya yada bidiyon da matar gwamna ke almubbazaranci da kudi, kamata ya yi a alakanta abin da wahala da matsalar da ake ciki ta fatara, yaran da ba su zuwa makaranta da ke gararanba kan tituna da shan wahala tsaro da ta kassara gabashin jihar


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Dandalin Yaki Da Ta’addanci Na Sin Ya Tattara Ra’Ayoyin Kasashen Duniya

Next Post

Wasu Barayin Shanu Da Hatsabiban ‘Yan Bindiga Sun Shiga Hannu

Related

Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa
Labarai

Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa

6 hours ago
Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya
Rahotonni

Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya

6 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Labarai

Babu Dalilin Da Zai Sa ‘Yan Nijeriya Su Yi Talauci – Tinubu

7 hours ago
Akwai Bukatar Samar Da Sauyin Zaman Lafiya Mai Dorewa A Duniya — Maryam Bukar
Labarai

Akwai Bukatar Samar Da Sauyin Zaman Lafiya Mai Dorewa A Duniya — Maryam Bukar

9 hours ago
UBEC Ta Kaddamar Da Makarantun Zamani 21 A Sassan Nijeriya
Labarai

UBEC Ta Kaddamar Da Makarantun Zamani 21 A Sassan Nijeriya

10 hours ago
Gwamnatin Katsina Za Ta Samu Kudaden Bunkasa Ilimi
Labarai

Tetfund Ta Samar Da Naira Biliyan 100 Don Inganta Ilimin Likitanci – Masari

11 hours ago
Next Post
Wasu Barayin Shanu Da Hatsabiban ‘Yan Bindiga Sun Shiga Hannu

Wasu Barayin Shanu Da Hatsabiban ‘Yan Bindiga Sun Shiga Hannu

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi: Ya Kamata A Mutunta Tarihi Domin Magance Sake Yin Kuskure

Wang Yi: Ya Kamata A Mutunta Tarihi Domin Magance Sake Yin Kuskure

August 15, 2025
An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

August 15, 2025
Ya Kamata A Yi Wa Japan Jinyar Cutar “Mantuwar Tarihi”

Ya Kamata A Yi Wa Japan Jinyar Cutar “Mantuwar Tarihi”

August 15, 2025
Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

August 15, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Bikin Mu’amalar Al’adu Da Jama’a A Hedkwatar MDD

CMG Ya Kaddamar Da Bikin Mu’amalar Al’adu Da Jama’a A Hedkwatar MDD

August 15, 2025
Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa

Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa

August 15, 2025
Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya

Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya

August 15, 2025
Gasar Wasannin Mutum Mutumin Inji Ta Duniya Ta 2025 Na Gabatar Da Sabbin Fasahohin Zamani

Gasar Wasannin Mutum Mutumin Inji Ta Duniya Ta 2025 Na Gabatar Da Sabbin Fasahohin Zamani

August 15, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Babu Dalilin Da Zai Sa ‘Yan Nijeriya Su Yi Talauci – Tinubu

August 15, 2025
Tattalin Arzikin Sin Ya Bunkasa Yadda Ya Kamata A Watan Yuli

Tattalin Arzikin Sin Ya Bunkasa Yadda Ya Kamata A Watan Yuli

August 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.