ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu Barayin Shanu Da Hatsabiban ‘Yan Bindiga Sun Shiga Hannu

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Barayi

A wani ci gaba da rundunar ‘yansanda a Jihar Kaduna ta gudanar, ta cafke wasu barayin shanu biyu da wasu fitattun ‘yan bindiga guda biyu, tare da dakile wani yunkurin yin garkuwa da mutane a wasu ayyuka daban-daban a jihar.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan jihar, Mansir Hassan, ya kara da cewa ‘yansandan sun kama Aminu Saleh da Jafar Ibrahim, ‘yan kungiyar asiri ne da ke da alhakin satar shanu daga manoman da ba su ji ba ba su gani ba a yankin Kasuwa Magani da ke Kujama.

  • Dan Takarar Gwamnan Katsina A NNPP Ya Ba Da Tallafin Miliyan 50 Ga ‘Yan Gudun Hijira
  • CDD Ta Soki NBC Kan Cin Tarar Trust TV Da Wasu Miliyan 20

A wani labarin kuma, Hassan, a wata sanarwa da ya fitar ya ce jami’an ‘yansanda sun kuma dakile wani yunkurin yin garkuwa da su tare da kama wasu mutane uku Umar Baso, Shehu Filani, da Babangida Abdulkarim wadanda ke neman kudin fansar Naira miliyan 10 daga hannun wadanda aka sace.

ADVERTISEMENT

Ya ci gaba da cewa rundunar ‘yan sandan ta kama wasu mutane biyu, Dahiru Liman da Sani Abdullahi Makeri da ke da hannu wajen samar da makamai da alburusai ga masu garkuwa da mutane da ke aiki a Jihohin Kaduna, Katsina da Zamfara.

A cewarsa, an samu nasarar kwato bindiga kirar AK-47 da harsashi mai tsawon millimita biyar a yayin samamen.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

Kakakin rundunar ‘yansandan ya nakalto kwamishinan ‘yansandan jihar, Audu Ali Dabigi, ya yaba wa ‘yansandan bisa kokarin da suke yi, ya kuma bukaci jama’a da su sanya ido tare da kai rahoto ga ofishin ‘yansanda mafi kusa.

Ya kuma tabbatar wa mazauna jihar kan kudurin hukumar na wargaza hanyoyin sadarwar masu aikata laifuka da kuma tabbatar da tsaro da jin dadin dukkan ‘yan kasa a fadin jihar.

Sanarwar ta ce, “A ranar 22 ga watan Agusta, 2024, jami’an ‘yansanda sun yi nasarar kai samame a wata maboyar da wasu ‘yan kungiyar asiri masu satar shanu ke amfani da ita a unguwar Kasuwa Magani da ke Kujama, Kaduna. An kama wasu mutane biyu, Aminu Saleh mai shekaru 25 da Jafar Ibrahim mai shekaru 24, kuma sun amsa laifinsu.

“A wani lamari na daban, jami’an ‘yansanda sun dakile yunkurin sace mutane tare da kama wasu mutane uku Umar Baso, Shehu Filani, da Babangida Abdulkarim wadanda ke neman kudin fansa Naira miliyan 10m.

“Bugu da kari, a ranar 24 ga Agusta, 2024, jami’an tsaro sun kama wasu mutane biyu, Dahiru Liman mai shekaru 47 da Sani Abdullahi Makeri mai shekaru 45, wadanda ke da hannu wajen samar da makamai da alburusai ga masu garkuwa da mutane da ke aiki a jihohin Kaduna, Katsina da Zamfara. An samu nasarar kwato bindigu kirar AK-47 guda daya da harsashi mai girman millimita 9 a yayin samamen.

“Kwamishanan ‘yansandan Jihar Kaduna, Audu Ali Dabigi, ya yaba wa ‘yansandan bisa kokarin da suke yi, ya kuma bukaci jama’a da su sanya ido tare da bayar da rahoton duk wani abu da ake zargin su da aikatawa tare da tabbatar wa mazauna yankin kudurin rundunar na wargaza hanyoyin sadarwa da kuma tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali ga dukkan ‘yan kasa.

Barayi
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

MASU ALAKA

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
Labarai

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Next Post
Mutum 2,629,025 Ke Da Wuƙa Da Namar Zabo Sabon Gwamnan Edo -INEC 

Mutum 2,629,025 Ke Da Wuƙa Da Namar Zabo Sabon Gwamnan Edo -INEC 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.