ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu Barayin Shanu Da Hatsabiban ‘Yan Bindiga Sun Shiga Hannu

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Barayi

A wani ci gaba da rundunar ‘yansanda a Jihar Kaduna ta gudanar, ta cafke wasu barayin shanu biyu da wasu fitattun ‘yan bindiga guda biyu, tare da dakile wani yunkurin yin garkuwa da mutane a wasu ayyuka daban-daban a jihar.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan jihar, Mansir Hassan, ya kara da cewa ‘yansandan sun kama Aminu Saleh da Jafar Ibrahim, ‘yan kungiyar asiri ne da ke da alhakin satar shanu daga manoman da ba su ji ba ba su gani ba a yankin Kasuwa Magani da ke Kujama.

  • Dan Takarar Gwamnan Katsina A NNPP Ya Ba Da Tallafin Miliyan 50 Ga ‘Yan Gudun Hijira
  • CDD Ta Soki NBC Kan Cin Tarar Trust TV Da Wasu Miliyan 20

A wani labarin kuma, Hassan, a wata sanarwa da ya fitar ya ce jami’an ‘yansanda sun kuma dakile wani yunkurin yin garkuwa da su tare da kama wasu mutane uku Umar Baso, Shehu Filani, da Babangida Abdulkarim wadanda ke neman kudin fansar Naira miliyan 10 daga hannun wadanda aka sace.

ADVERTISEMENT

Ya ci gaba da cewa rundunar ‘yan sandan ta kama wasu mutane biyu, Dahiru Liman da Sani Abdullahi Makeri da ke da hannu wajen samar da makamai da alburusai ga masu garkuwa da mutane da ke aiki a Jihohin Kaduna, Katsina da Zamfara.

A cewarsa, an samu nasarar kwato bindiga kirar AK-47 da harsashi mai tsawon millimita biyar a yayin samamen.

LABARAI MASU NASABA

An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

Xi Ya Zanta Da Shugabar Namibia

Kakakin rundunar ‘yansandan ya nakalto kwamishinan ‘yansandan jihar, Audu Ali Dabigi, ya yaba wa ‘yansandan bisa kokarin da suke yi, ya kuma bukaci jama’a da su sanya ido tare da kai rahoto ga ofishin ‘yansanda mafi kusa.

Ya kuma tabbatar wa mazauna jihar kan kudurin hukumar na wargaza hanyoyin sadarwar masu aikata laifuka da kuma tabbatar da tsaro da jin dadin dukkan ‘yan kasa a fadin jihar.

Sanarwar ta ce, “A ranar 22 ga watan Agusta, 2024, jami’an ‘yansanda sun yi nasarar kai samame a wata maboyar da wasu ‘yan kungiyar asiri masu satar shanu ke amfani da ita a unguwar Kasuwa Magani da ke Kujama, Kaduna. An kama wasu mutane biyu, Aminu Saleh mai shekaru 25 da Jafar Ibrahim mai shekaru 24, kuma sun amsa laifinsu.

“A wani lamari na daban, jami’an ‘yansanda sun dakile yunkurin sace mutane tare da kama wasu mutane uku Umar Baso, Shehu Filani, da Babangida Abdulkarim wadanda ke neman kudin fansa Naira miliyan 10m.

“Bugu da kari, a ranar 24 ga Agusta, 2024, jami’an tsaro sun kama wasu mutane biyu, Dahiru Liman mai shekaru 47 da Sani Abdullahi Makeri mai shekaru 45, wadanda ke da hannu wajen samar da makamai da alburusai ga masu garkuwa da mutane da ke aiki a jihohin Kaduna, Katsina da Zamfara. An samu nasarar kwato bindigu kirar AK-47 guda daya da harsashi mai girman millimita 9 a yayin samamen.

“Kwamishanan ‘yansandan Jihar Kaduna, Audu Ali Dabigi, ya yaba wa ‘yansandan bisa kokarin da suke yi, ya kuma bukaci jama’a da su sanya ido tare da bayar da rahoton duk wani abu da ake zargin su da aikatawa tare da tabbatar wa mazauna yankin kudurin rundunar na wargaza hanyoyin sadarwa da kuma tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali ga dukkan ‘yan kasa.

Barayi
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Sarkin Zazzau Ya Umarci A Soke Wasu Al’adu Da Ke Kawo Wa Aure Cikas

MASU ALAKA

An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa
Manyan Labarai

An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

July 10, 2026
Xi Ya Zanta Da Shugabar Namibia
Labarai

Xi Ya Zanta Da Shugabar Namibia

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Labarai

Ko Ka San Dalilin Da Ya Sa Chana Da Indiya Ba Sa Buga Kofin Duniya?

July 10, 2026
Next Post
Mutum 2,629,025 Ke Da Wuƙa Da Namar Zabo Sabon Gwamnan Edo -INEC 

Mutum 2,629,025 Ke Da Wuƙa Da Namar Zabo Sabon Gwamnan Edo -INEC 

LABARAI MASU NASABA

An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

July 10, 2026
Xi Ya Zanta Da Shugabar Namibia

Xi Ya Zanta Da Shugabar Namibia

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ko Ka San Dalilin Da Ya Sa Chana Da Indiya Ba Sa Buga Kofin Duniya?

July 10, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Sana’ar Ɗinki: Yadda Telolin Zariya Suka Yi Fice A Sassan Afirka

July 10, 2026
Shugaba Xi Ya Gana Da Firaministan Koriya Ta Arewa A Beijing

Shugaba Xi Ya Gana Da Firaministan Koriya Ta Arewa A Beijing

July 10, 2026
Kofin Duniya: Na fi Son Faransa Ta Kara Da Argentina A Wasan Ƙarshe A Kan Ingila — Vieira

Kofin Duniya: Na fi Son Faransa Ta Kara Da Argentina A Wasan Ƙarshe A Kan Ingila — Vieira

July 10, 2026
Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga A Wani Ƙauyen Katsina

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga A Wani Ƙauyen Katsina

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ibrahim Aliyu Na Ci Gaba Da Rasa Tasiri A Harkar Fili Da Gidaje A Yankin Abuja

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Fafutukar Neman Sabon Sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya

July 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.