ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Daure Hadimin Tambuwal Kan Yada Bidiyon Da Ake Wa Matar Gwamna Liki Da Dala

by Abubakar Sulaiman
2 years ago
Tambuwal

Kotun majistare ta daya da ke Sakkwato a yau ta tura mataimaki na musamman ga Sanata Aminu Waziri Tambuwal kan yada labarai, Shafi’u Umar Tureta a gidan gyaran hali a bisa ga yada bidiyon matar Gwamna Ahmed Aliyu a yayin da ake yi mata liki da Dala.

Mai Shari’a Fatima Hassan ta daga zaman kotun kan hukuncin da za a yi kan dan shekaru 36 zuwa ranar 6 ga Satumba da za a yanke shawarar bayar da belinsa kan laifin batanci. Sai dai duk kokarin manema labarai na halartar zaman kotun ya faskara kansancewar an haramta musu shiga.

  • Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
  • Kotu Ta Ɗaure Hadimin Tambuwal Kan Yaɗa Bidiyon Da Ake Yi Wa Matar Gwamnan Sakkwato Liƙi Da Dala

Mai shigar da kara ta bayyana bayyanan a ranar 18/7/2023 cewa ya yada bidiyon matar Gwamna, Fatima Ahmed Aliyu a yayin da take bukin zagayowar ranar haihuwarta tare da cewar ta na almubbazaranci a liki da kashe kudin a yayin da al’umma ke a cikin yunwa.

ADVERTISEMENT

Laifi na biyu da aka tuhumi shafukan shi ne sanya tsohuwar takardar kammala makarantar sakandiren Gwamna da sakamakon F9 tare da kiran sa bakauye bai iya magana da turanci ba, lamarin da dansanda mai shigar da kara Abdurrahman Mansur ya ce sun saba wa kundin dokar penal code ta jihar ta 2019 sashe na 378 da 379.

Sai dai jam’iyyar PDP a jihar ta ce ba Shafi’u ne ya dauki bidiyon da Gwamna ke turanciin ba don ba ya da damar shiga gidan gwamnati inda aka dauki bidiyon haka ma bai halarci bikin zagayowar ranar haihuwar matar gwamnan ba don haka ba inda zai same su idan ba yaran gwamnan da taimakonsa ne suka yada ba.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

Kakakin jam’iyyar, Hassan Sahabi Sanyinnawal ya bayyana mulkin kama – karya ne jaridun Sakkwato ke yi tare da kokarin cin zarafin ‘yan adawa ko ‘yan PDP, domin hakan rashin adalci ne kuma ba za su zuba ido a na nuna wa magoya bayan su ba.

A nata bangaren kungiyar kare hakkin zan’adam ta Amnesty International ta bi sahun wadanda suka soki lamarin, ta ce kama hotunan ya sabawa ‘yancinsa na dan’adam don haka ta yi Allah – wadai da kamen tare da kiran a gaggauta sakin sa.

Kungiyar ta ce maimakon kama marubucin wanda ya yada bidiyon da matar gwamna ke almubbazaranci da kudi, kamata ya yi a alakanta abin da wahala da matsalar da ake ciki ta fatara, yaran da ba su zuwa makaranta da ke gararanba kan tituna da shan wahala tsaro da ta kassara gabashin jihar

Tambuwal
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Hana INEC Amincewa Da Tarukan ADC Ƙarƙashin Jagorancin David Mark
  • Abubakar Sulaiman
    Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato
  • Abubakar Sulaiman
    FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

MASU ALAKA

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje
Manyan Labarai

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Next Post
Wasu Barayin Shanu Da Hatsabiban ‘Yan Bindiga Sun Shiga Hannu

Wasu Barayin Shanu Da Hatsabiban ‘Yan Bindiga Sun Shiga Hannu

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.