ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Daure Hadimin Tambuwal Kan Yada Bidiyon Da Ake Wa Matar Gwamna Liki Da Dala

by Abubakar Sulaiman
2 years ago
Tambuwal

Kotun majistare ta daya da ke Sakkwato a yau ta tura mataimaki na musamman ga Sanata Aminu Waziri Tambuwal kan yada labarai, Shafi’u Umar Tureta a gidan gyaran hali a bisa ga yada bidiyon matar Gwamna Ahmed Aliyu a yayin da ake yi mata liki da Dala.

Mai Shari’a Fatima Hassan ta daga zaman kotun kan hukuncin da za a yi kan dan shekaru 36 zuwa ranar 6 ga Satumba da za a yanke shawarar bayar da belinsa kan laifin batanci. Sai dai duk kokarin manema labarai na halartar zaman kotun ya faskara kansancewar an haramta musu shiga.

  • Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
  • Kotu Ta Ɗaure Hadimin Tambuwal Kan Yaɗa Bidiyon Da Ake Yi Wa Matar Gwamnan Sakkwato Liƙi Da Dala

Mai shigar da kara ta bayyana bayyanan a ranar 18/7/2023 cewa ya yada bidiyon matar Gwamna, Fatima Ahmed Aliyu a yayin da take bukin zagayowar ranar haihuwarta tare da cewar ta na almubbazaranci a liki da kashe kudin a yayin da al’umma ke a cikin yunwa.

ADVERTISEMENT

Laifi na biyu da aka tuhumi shafukan shi ne sanya tsohuwar takardar kammala makarantar sakandiren Gwamna da sakamakon F9 tare da kiran sa bakauye bai iya magana da turanci ba, lamarin da dansanda mai shigar da kara Abdurrahman Mansur ya ce sun saba wa kundin dokar penal code ta jihar ta 2019 sashe na 378 da 379.

Sai dai jam’iyyar PDP a jihar ta ce ba Shafi’u ne ya dauki bidiyon da Gwamna ke turanciin ba don ba ya da damar shiga gidan gwamnati inda aka dauki bidiyon haka ma bai halarci bikin zagayowar ranar haihuwar matar gwamnan ba don haka ba inda zai same su idan ba yaran gwamnan da taimakonsa ne suka yada ba.

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Kakakin jam’iyyar, Hassan Sahabi Sanyinnawal ya bayyana mulkin kama – karya ne jaridun Sakkwato ke yi tare da kokarin cin zarafin ‘yan adawa ko ‘yan PDP, domin hakan rashin adalci ne kuma ba za su zuba ido a na nuna wa magoya bayan su ba.

A nata bangaren kungiyar kare hakkin zan’adam ta Amnesty International ta bi sahun wadanda suka soki lamarin, ta ce kama hotunan ya sabawa ‘yancinsa na dan’adam don haka ta yi Allah – wadai da kamen tare da kiran a gaggauta sakin sa.

Kungiyar ta ce maimakon kama marubucin wanda ya yada bidiyon da matar gwamna ke almubbazaranci da kudi, kamata ya yi a alakanta abin da wahala da matsalar da ake ciki ta fatara, yaran da ba su zuwa makaranta da ke gararanba kan tituna da shan wahala tsaro da ta kassara gabashin jihar

Tambuwal
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Iyalin El-Rufai Sun Bai Ministan Tsaro Wa’adin Kwana 7 Kan Zargin Rikicin Kudancin Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Atiku Ya Zargi Gwamnatin Tarayya Da Cin Bashi Kamar Mashayin Da Kuɗi Ya Ƙarewa
  • Abubakar Sulaiman
    Boko Haram Ta Kai Hari Adamawa, Ana Fargabar Mutuwar Mutane 11
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Sokoto, Sun Kashe Mutane 7, Sun Yi Garkuwa Da 12

MASU ALAKA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Next Post
Wasu Barayin Shanu Da Hatsabiban ‘Yan Bindiga Sun Shiga Hannu

Wasu Barayin Shanu Da Hatsabiban ‘Yan Bindiga Sun Shiga Hannu

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.