• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Daure Uban Da Ya Dirka Wa ‘Yarsa Ciki A Bayelsa

by Sulaiman and Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
in Labarai
0
kotu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata Babbar Kotun Jihar Bayelsa da ke zamanta a Yenagoa ta yanke wa wani mutum mai suna Baridapsi Needam mai shekaru 41 hukuncin daurin shekara 14 a gidan yari bisa samunsa da laifin yi wa ‘yarsa ciki ta hanyar fyade.

Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya, NAN, ya ruwaito a daidai lokacin da ake shari’ar an bayyana cewa yarinyar da aka yi wa cikin ta haifi ‘ya mace.

  • Binciken Ganduje: Kotu Ta Bai Wa Alkalan Kano Sa’o’i 48 Su Yi Murabus
  • Kotu Ta Rushe Dokar Da Ta Tsige Aminu Ado Bayero A Matsayin Sarkin Kano

Kwamishinan Shari’a na Jihar Bayelsa, kuma Babban Lauyan Gwamnati, Briyal Dambo, a kara mai lamba YHC/14C/2022, ya tuhumi wanda ake zargin da laifin aikata laifin fyade da ya saba wa sashe na 1 (1) na dokar cin zarafin jama’a ta Jihar Bayelsa ta 2021.

Pere Amanda Egbuson, lauya mai shigar da kara na ma’aikatar shari’a ta Bayelsa, ya shaida wa kotun cewa bincike ya nuna cewa wanda ake zargin Needam ya fara cin zarafin ‘yarsa tun tana ‘yar shekara bakwai.
Egbuson ya ce Needam ya lalata ‘yar ne ta hanyar sanya yatsunsa a cikin al’aurarta kafin ya san ta ‘ya mace a shekarar 2020 har zuwa lokacin da ta samu ciki.

Mai shari’a D.E. Adokeme, yayin da yake yanke hukunci, ya bayyana cewa masu gabatar da kara sun gabatar da sahihiyar shaida tare da yin bincike kan sakamakon DNA, wanda ya nuna cewa kashi 99.99 cikin 100 tabbataccen rahoton cewa wanda aka yankewa hukuncin shi ne mahaifin yaron.
Kotun ta yanke hukuncin daurin shekaru 14 a gidan yari, inda mai gabatar da kara ya tabbatar da cewa Needam ta aikata laifin fyade.

Labarai Masu Nasaba

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

Da yake magana bayan yanke hukuncin, Egbuson, jagoran masu shigar da kara, ya lura cewa hukuncin zai zama izna ga sauran masu aikata irin wadannan abubuwa na wuce tunanin dan dan’adam.

Ta gode wa babban mai shari’a kuma kwamishinan shari’a, Biriyai Dambo, bisa goyon bayan da ya bayar wajen ganin an gudanar da binciken DNA domin taimakawa masu gabatar da kara.

Da take mayar da martani kan wannan ci gaban, wata fitacciyar mai fafutukar yaki da cin zarafin mata, kuma wacce ta kafa gidauniyar Do Foundation, Dakta Dise Ogbise-Goddy Harry, ta yaba wa kotun bisa tabbatar da adalci.

“Gwamnatin Jihar Ta Hannun Ma’aikatar Shari’a, Ma’aikatar Harkokin Mata, Harkokin Yara da Ci Gaban jama’a da kuma kungiyar daidaita jinsi ta Jihar Bayelsa sun yi aiki mai kyau wajen ba wa wacce abin ya shafa kariya da kuma jaririyar.

Idan dai ba a manta ba Kungiyar Kare Hakkin Mata ta Jihar Bayelsa, ‘Gender Response Initiatibe Team’ (GRIT) ta mika Needman ga ‘yansanda, bayan da wani makwabcin da ya gano cewa shi ke da alhakin yi wa ‘yarsa ciki a shekarar 2022.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FyadeKotu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya(2)

Next Post

An Ɗage Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Bauchi

Related

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

1 hour ago
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

13 hours ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

18 hours ago
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?
Labarai

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

19 hours ago
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

20 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

21 hours ago
Next Post
An Ɗage Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Bauchi

An Ɗage Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

August 24, 2025
Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

August 24, 2025
Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

August 24, 2025
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

August 24, 2025
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.