• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Daure Uban Da Ya Dirka Wa ‘Yarsa Ciki A Bayelsa

bySulaiman and Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
kotu

Wata Babbar Kotun Jihar Bayelsa da ke zamanta a Yenagoa ta yanke wa wani mutum mai suna Baridapsi Needam mai shekaru 41 hukuncin daurin shekara 14 a gidan yari bisa samunsa da laifin yi wa ‘yarsa ciki ta hanyar fyade.

Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya, NAN, ya ruwaito a daidai lokacin da ake shari’ar an bayyana cewa yarinyar da aka yi wa cikin ta haifi ‘ya mace.

  • Binciken Ganduje: Kotu Ta Bai Wa Alkalan Kano Sa’o’i 48 Su Yi Murabus
  • Kotu Ta Rushe Dokar Da Ta Tsige Aminu Ado Bayero A Matsayin Sarkin Kano

Kwamishinan Shari’a na Jihar Bayelsa, kuma Babban Lauyan Gwamnati, Briyal Dambo, a kara mai lamba YHC/14C/2022, ya tuhumi wanda ake zargin da laifin aikata laifin fyade da ya saba wa sashe na 1 (1) na dokar cin zarafin jama’a ta Jihar Bayelsa ta 2021.

Pere Amanda Egbuson, lauya mai shigar da kara na ma’aikatar shari’a ta Bayelsa, ya shaida wa kotun cewa bincike ya nuna cewa wanda ake zargin Needam ya fara cin zarafin ‘yarsa tun tana ‘yar shekara bakwai.
Egbuson ya ce Needam ya lalata ‘yar ne ta hanyar sanya yatsunsa a cikin al’aurarta kafin ya san ta ‘ya mace a shekarar 2020 har zuwa lokacin da ta samu ciki.

Mai shari’a D.E. Adokeme, yayin da yake yanke hukunci, ya bayyana cewa masu gabatar da kara sun gabatar da sahihiyar shaida tare da yin bincike kan sakamakon DNA, wanda ya nuna cewa kashi 99.99 cikin 100 tabbataccen rahoton cewa wanda aka yankewa hukuncin shi ne mahaifin yaron.
Kotun ta yanke hukuncin daurin shekaru 14 a gidan yari, inda mai gabatar da kara ya tabbatar da cewa Needam ta aikata laifin fyade.

LABARAI MASU NASABA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

Da yake magana bayan yanke hukuncin, Egbuson, jagoran masu shigar da kara, ya lura cewa hukuncin zai zama izna ga sauran masu aikata irin wadannan abubuwa na wuce tunanin dan dan’adam.

Ta gode wa babban mai shari’a kuma kwamishinan shari’a, Biriyai Dambo, bisa goyon bayan da ya bayar wajen ganin an gudanar da binciken DNA domin taimakawa masu gabatar da kara.

Da take mayar da martani kan wannan ci gaban, wata fitacciyar mai fafutukar yaki da cin zarafin mata, kuma wacce ta kafa gidauniyar Do Foundation, Dakta Dise Ogbise-Goddy Harry, ta yaba wa kotun bisa tabbatar da adalci.

“Gwamnatin Jihar Ta Hannun Ma’aikatar Shari’a, Ma’aikatar Harkokin Mata, Harkokin Yara da Ci Gaban jama’a da kuma kungiyar daidaita jinsi ta Jihar Bayelsa sun yi aiki mai kyau wajen ba wa wacce abin ya shafa kariya da kuma jaririyar.

Idan dai ba a manta ba Kungiyar Kare Hakkin Mata ta Jihar Bayelsa, ‘Gender Response Initiatibe Team’ (GRIT) ta mika Needman ga ‘yansanda, bayan da wani makwabcin da ya gano cewa shi ke da alhakin yi wa ‘yarsa ciki a shekarar 2022.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Next Post
An Ɗage Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Bauchi

An Ɗage Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version