ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, November 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Daure Uban Da Ya Dirka Wa ‘Yarsa Ciki A Bayelsa

by Sulaiman and Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
kotu

Wata Babbar Kotun Jihar Bayelsa da ke zamanta a Yenagoa ta yanke wa wani mutum mai suna Baridapsi Needam mai shekaru 41 hukuncin daurin shekara 14 a gidan yari bisa samunsa da laifin yi wa ‘yarsa ciki ta hanyar fyade.

Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya, NAN, ya ruwaito a daidai lokacin da ake shari’ar an bayyana cewa yarinyar da aka yi wa cikin ta haifi ‘ya mace.

  • Binciken Ganduje: Kotu Ta Bai Wa Alkalan Kano Sa’o’i 48 Su Yi Murabus
  • Kotu Ta Rushe Dokar Da Ta Tsige Aminu Ado Bayero A Matsayin Sarkin Kano

Kwamishinan Shari’a na Jihar Bayelsa, kuma Babban Lauyan Gwamnati, Briyal Dambo, a kara mai lamba YHC/14C/2022, ya tuhumi wanda ake zargin da laifin aikata laifin fyade da ya saba wa sashe na 1 (1) na dokar cin zarafin jama’a ta Jihar Bayelsa ta 2021.

ADVERTISEMENT

Pere Amanda Egbuson, lauya mai shigar da kara na ma’aikatar shari’a ta Bayelsa, ya shaida wa kotun cewa bincike ya nuna cewa wanda ake zargin Needam ya fara cin zarafin ‘yarsa tun tana ‘yar shekara bakwai.
Egbuson ya ce Needam ya lalata ‘yar ne ta hanyar sanya yatsunsa a cikin al’aurarta kafin ya san ta ‘ya mace a shekarar 2020 har zuwa lokacin da ta samu ciki.

Mai shari’a D.E. Adokeme, yayin da yake yanke hukunci, ya bayyana cewa masu gabatar da kara sun gabatar da sahihiyar shaida tare da yin bincike kan sakamakon DNA, wanda ya nuna cewa kashi 99.99 cikin 100 tabbataccen rahoton cewa wanda aka yankewa hukuncin shi ne mahaifin yaron.
Kotun ta yanke hukuncin daurin shekaru 14 a gidan yari, inda mai gabatar da kara ya tabbatar da cewa Needam ta aikata laifin fyade.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

‘Yansanda Sun Kama Mutane 4 Kan Zargin Fashi Da Makami A Bauchi

Da yake magana bayan yanke hukuncin, Egbuson, jagoran masu shigar da kara, ya lura cewa hukuncin zai zama izna ga sauran masu aikata irin wadannan abubuwa na wuce tunanin dan dan’adam.

Ta gode wa babban mai shari’a kuma kwamishinan shari’a, Biriyai Dambo, bisa goyon bayan da ya bayar wajen ganin an gudanar da binciken DNA domin taimakawa masu gabatar da kara.

Da take mayar da martani kan wannan ci gaban, wata fitacciyar mai fafutukar yaki da cin zarafin mata, kuma wacce ta kafa gidauniyar Do Foundation, Dakta Dise Ogbise-Goddy Harry, ta yaba wa kotun bisa tabbatar da adalci.

“Gwamnatin Jihar Ta Hannun Ma’aikatar Shari’a, Ma’aikatar Harkokin Mata, Harkokin Yara da Ci Gaban jama’a da kuma kungiyar daidaita jinsi ta Jihar Bayelsa sun yi aiki mai kyau wajen ba wa wacce abin ya shafa kariya da kuma jaririyar.

Idan dai ba a manta ba Kungiyar Kare Hakkin Mata ta Jihar Bayelsa, ‘Gender Response Initiatibe Team’ (GRIT) ta mika Needman ga ‘yansanda, bayan da wani makwabcin da ya gano cewa shi ke da alhakin yi wa ‘yarsa ciki a shekarar 2022.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 
Labarai

Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 12, 2025
'yansanda
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 4 Kan Zargin Fashi Da Makami A Bauchi

November 12, 2025
Kashi 74% Na Marasa Lafiya Sun Gamsu Da Ayyukan Kiwon Lafiya Na Nijeriya — Minista
Manyan Labarai

Kashi 74% Na Marasa Lafiya Sun Gamsu Da Ayyukan Kiwon Lafiya Na Nijeriya — Minista

November 12, 2025
Next Post
An Ɗage Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Bauchi

An Ɗage Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

November 12, 2025
Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 12, 2025
Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

November 12, 2025
Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

November 12, 2025
'yansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutane 4 Kan Zargin Fashi Da Makami A Bauchi

November 12, 2025
Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci

Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci

November 12, 2025
Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki

Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki

November 12, 2025
Kashi 74% Na Marasa Lafiya Sun Gamsu Da Ayyukan Kiwon Lafiya Na Nijeriya — Minista

Kashi 74% Na Marasa Lafiya Sun Gamsu Da Ayyukan Kiwon Lafiya Na Nijeriya — Minista

November 12, 2025
Majalisar Kogi Ta Dakatar Da Shugaban Ƙaramar Hukuma Bisa Zargin Rashin Ɗa’a

Majalisar Jihar Kogi Ta Dakatar Da Shugaban Ƙaramar Hukuma Kan Laifin Rashin Ɗa’a

November 12, 2025
Xi Ya Gana Da Sarkin Sifaniya A Birnin Beijing

Xi Ya Gana Da Sarkin Sifaniya A Birnin Beijing

November 12, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.