ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

by Sani Anwar
6 minutes ago
Kotu

Jami’ar Maryam Abacha da ke Kano (MAAUN), ta fuskantar matsanancin bincike daga hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta Kano, kan harajin da ta kakaba wa daliban da ta yaye na kimanin naira 750,000.

Hukumar kula da jami’ar mai zaman kanta da ke Kano, ta tilasta wa daliban da ta yaye biyan wadannan makudan kudade, kafin bayar da sakamakon karshe da kuma tura sunayensu zuwa hukumar NYSC da kuma ba su sauran takardun da suka dace kafin yaye daliban, lamarin da ya sa hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta shiga tsakani.

  • Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi
  • ‘Yan Wasa Biyar Da Tauraruwarsu Za Ta Haska A AFCON

Hukumar korafe-korafen da yaki da cin hanci da rashawa ta Jihar Kano, ta umarci jami’ar ta da dakatar da bukatar ta karbar Naira 750,000 daga hannun daliban.

ADVERTISEMENT

A wata wasika mai dauke da kwanan watan 27 ga watan Nuwamban 2025, mai dauke da sa hannun shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa, Salisu Saleh, an umarci jami’ar da ta dakatar da karbar wadannan kudade tare da bai wa daliban takardar shedar tafiya bautar kasa (NYSC) da kuma takardar shedar kammala karatun jami’ar.

Hukumar ta bayyana a cikin wasikar cewa, tana daukar matakin ne daidai da ikonta a karkashin sashe na 9 da 15 na dokar PCACC ta 2008 (kamar yadda aka yi wa kwaskwarima, 2010), da kuma hana ayyukan da ka iya kawo cikas ga binciken.

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

Hukumar ta tabbatar da samun korafi a hukumance game da sanya kudaden da kuma damuwar cewa, akwai barazanar hukunta daliban sakamakon kin biyan kudin.

Duk da umarnin da hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta bayar, iyayen daliban da aka yaye, sun koka da rashin mutunta sanarwar, kamar yadda hukumar gwamnati ta bayar, inda a maimakon haka jami’ar ta yi musu barazana.

Mahaifiyar dalibin da ya kammala karatun digirin da ya nemi a sakaya sunansa ya nuna damuwarsa kan yadda mahukuntan jami’ar suka rufe kofa tare da kin amsa tambayoyi daga iyayen.

Da yake mayar da martani game da karin korafe-korafen, Shugaban Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa, Saidu Yahya, ya tabbatar da binciken da ake yi kan lamarin tare da tabbatar da aniyar ganin cewa; ba a cutar da kowa ba.

Binciken LEADERSHIP, ta tabbatar da cewa, hukumar jami’ar ta Maryam Abacha, ta samu izinin daga kotu na dakatar da binciken hukumar korafe-korafen ta Jihar Kano kan al’amarin, har sai ta kammala bincikenta tare da yanke hukunci.

Har izuwa lokacin hada wannan rahoto, ba mu samu damar jin ta bakin hukumar jami’ar ta MAAUN din ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya
Labarai

Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

December 20, 2025
Auren Da Ya Fi Auren Gidan Daula Dadi Ga Mace
Rahotonni

Auren Da Ya Fi Auren Gidan Daula Dadi Ga Mace

December 20, 2025

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

December 20, 2025
An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

December 20, 2025
Auren Da Ya Fi Auren Gidan Daula Dadi Ga Mace

Auren Da Ya Fi Auren Gidan Daula Dadi Ga Mace

December 20, 2025
An Fara Aiki Da Na’urar Fasahar Samar Da Lantarki Daga Iskar CO₂ Da Aka Sarrafa A Lardin Guizhou Na Kasar Sin

An Fara Aiki Da Na’urar Fasahar Samar Da Lantarki Daga Iskar CO₂ Da Aka Sarrafa A Lardin Guizhou Na Kasar Sin

December 20, 2025
Shugaban Somaliya: Kara Fadada Bude Kofa Ga Kasashen Waje Da Sin Ke Yi Zai Inganta Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Afirka

Shugaban Somaliya: Kara Fadada Bude Kofa Ga Kasashen Waje Da Sin Ke Yi Zai Inganta Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Afirka

December 20, 2025
Shugaban Rasha Ya Bayyana Alakar Kasarsa Da Sin A Matsayin Matukar Muhimmanci Ga Samar Da Yanayin Daidaito A Duniya

Shugaban Rasha Ya Bayyana Alakar Kasarsa Da Sin A Matsayin Matukar Muhimmanci Ga Samar Da Yanayin Daidaito A Duniya

December 20, 2025
HOTUNA: Yadda Tinubu Ya Kai Ziyara Don Ta’aziyyar Sheikh Dahiru Bauchi

HOTUNA: Yadda Tinubu Ya Kai Ziyara Don Ta’aziyyar Sheikh Dahiru Bauchi

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.