• English
  • Business News
Friday, August 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Ki Amincewa A Mayar Da Shari’ar Abduljabbar Abuja

by Sadiq
3 years ago
in Da ɗumi-ɗuminsa, Manyan Labarai
0
Kotu Ta Ki Amincewa A Mayar Da Shari’ar Abduljabbar Abuja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kotun tarayya da ke zamanta a jihar Kano, ta ki amincewa da bukatar mayar da shari’ar Sheikh Abduljabbar Kabara zuwa babban birnin tarayya, Abuja.

Abduljabbar dai ya bukaci kotun da ta mayar da shari’ar tasa zuwa wata kotun a Abuja saboda zargin da yake na cewar kotun Kano ba za ta yi masa adalci ba.

  • Barazanar ‘Yan Bindiga: Gwamnatin Nasarawa Ta Rufe Duk Makarantun Jihar
  • Rashin Tsaro: NYSC Ta Nemi Karin Sojoji A Sansanonin Masu Yi Wa Kasa Hidima

A yayin zaman kotun na yau Alhamis, wanda ya gudana karkashin mai shari’a Abdullahi Liman, lauyan Abduljabbar Nasir Kabara, Barista Dalhatu Shehu Usman, ya zargi alkalin kotun tarayyar na Kano da ganawa da kwamsihinan shari’a na Kano, Barista Musa Lawan a safiyar yau gabanin zaman kotun.

Wanda ya ce bisa ka’ida bai kamata a ce alkalin ya yi hakan ba, wanda kuma hakan yasa Sheikh Kabara ya karaya da cewar ba zai samu adalci a kotun ba.

Sai dai a wani martani da lauya gwamnati, Barista Dahiru Muhammad, ya kalubalanci wannan batu.

Labarai Masu Nasaba

Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara

Gwamnan Kano Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Gentle, Ya Bada Umarnin Zakulo Masu Laifin

Ya sanar da kotun cewar tun karfe 9 na safiyar yau, masu gabatar da karar suka ba shi kwafin wata sabuwar karar da suka shigar a Abuja na zargin take hakkinsa na dan adam, bayan batun na gaban alkalin wata kotu ta daban.

Daga nan ne mai shari’a Abdullahi Liman, ya ce ba zai rufe shari’ar ba, sannan a shari’ance babu inda aka ce bangare daya da ake shari’a da shi zai ce lallai shi ga kotun da yake bukata da ta saurari wata shari’ar.

Sannan ya umurci lauyan Abduljabbar da ya rubuto zargin da yake yi kan zuwan Kwamishinan shari’a na jihar Kano wajensa, tare da tabbatar da abin da suka tattauna na da alaka da shari’ar ta Abduljababr din ya shigar gabansa.

LEADERSHIP ta ruwaito a ranar 21 ga watan Yulin da muke ciki ne Shiekh Abduljabbar, ya garzaya kotun tarayyar da ke Kano, da bukatar a mayar da shari’ar da ake yi masa ta zargin batancin ga Annabi S.A.W zuwa ga wani alkalin daban.

Ya yi hakan ne saboda zargin cewar gwamantin Kano da Babbar Kotun Musulunci ta Kofar Kudu na take masa hakkinsa a matsayinsa na dan Adam.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbduljabbarAbujakanoShari'aZargin Batanci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Rashin Tsaro: NYSC Ta Nemi Karin Sojoji A Sansanonin Masu Yi Wa Kasa Hidima

Next Post

Tsoffin Mataimakan Gwamnonin Kebbi 2 Da Mata 5000 Daga Bauchi Sun Bar APC Zuwa PDP

Related

Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara
Manyan Labarai

Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara

4 hours ago
Gwamnan Kano Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Gentle, Ya Bada Umarnin Zakulo Masu Laifin
Manyan Labarai

Gwamnan Kano Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Gentle, Ya Bada Umarnin Zakulo Masu Laifin

9 hours ago
Masu Ƙwacen Waya Sun Kashe Ɗalibin BUK A Kano
Manyan Labarai

Masu Ƙwacen Waya Sun Kashe Ɗalibin BUK A Kano

14 hours ago
Jami’an Tsaro Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi
Manyan Labarai

Jami’an Tsaro Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi

16 hours ago
Yawancin ‘Yan Siyasar Nijeriya Ba Su Da Tarbiyya – Sarki Sanusi II
Manyan Labarai

Yawancin ‘Yan Siyasar Nijeriya Ba Su Da Tarbiyya – Sarki Sanusi II

19 hours ago
Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya
Manyan Labarai

Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya

1 day ago
Next Post
Tsoffin Mataimakan Gwamnonin Kebbi 2 Da Mata 5000 Daga Bauchi Sun Bar APC Zuwa PDP

Tsoffin Mataimakan Gwamnonin Kebbi 2 Da Mata 5000 Daga Bauchi Sun Bar APC Zuwa PDP

LABARAI MASU NASABA

Barcelona Ta Tube Ter Stergen Daga Mukaminsa Na Kaftin Din Kungiyar 

Barcelona Ta Tube Ter Stergen Daga Mukaminsa Na Kaftin Din Kungiyar 

August 7, 2025
Tallafin Kammala Makarantun Share Fagen Shiga Firamare Na Gwamnatin Kasar Sin Zai Amfani Mutane Kimanin Miliyan 12

Tallafin Kammala Makarantun Share Fagen Shiga Firamare Na Gwamnatin Kasar Sin Zai Amfani Mutane Kimanin Miliyan 12

August 7, 2025
Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara

Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara

August 7, 2025
Cinikayyar Kayayyaki a Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.5 Cikin 100 Cikin Watanni 7 Na Farkon Shekarar Nan

Cinikayyar Kayayyaki a Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.5 Cikin 100 Cikin Watanni 7 Na Farkon Shekarar Nan

August 7, 2025
Amurka Ta Fara Girbar Sakamakon Kare-Karen Haraji

Amurka Ta Fara Girbar Sakamakon Kare-Karen Haraji

August 7, 2025
Tsoffin Kansilolin APC Sun Yi Zanga-zangar Nesanta Kansu Da Maganganun Abdullahi Abbas 

Tsoffin Kansilolin APC Sun Yi Zanga-zangar Nesanta Kansu Da Maganganun Abdullahi Abbas 

August 7, 2025
Neja

Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Jihohin Makwabta, Ya Kara Ta’azzarar Rashin Tsaro A Neja – Bago

August 7, 2025
Nazarin CGTN: Alummar Duniya Na Adawa Da Fadada Mamaya A Gaza

Nazarin CGTN: Alummar Duniya Na Adawa Da Fadada Mamaya A Gaza

August 7, 2025
Ranar Cutar Daji Ta 2025: Akwai Matakan Kariya Daga Kamuwa Da Cutar Kansa -Masana

Ranar Cutar Daji Ta 2025: Akwai Matakan Kariya Daga Kamuwa Da Cutar Kansa -Masana

August 7, 2025
Kasar Sin Ta Kammala Gwajin Farko Na Sauka Da Tashin Kumbon Binciken Duniyar Wata Mai Dauke Da Bil Adama

Kasar Sin Ta Kammala Gwajin Farko Na Sauka Da Tashin Kumbon Binciken Duniyar Wata Mai Dauke Da Bil Adama

August 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.