• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Ki Amincewa A Mayar Da Shari’ar Abduljabbar Abuja

by Sadiq
3 years ago
in Da ɗumi-ɗuminsa, Manyan Labarai
0
Kotu Ta Ki Amincewa A Mayar Da Shari’ar Abduljabbar Abuja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kotun tarayya da ke zamanta a jihar Kano, ta ki amincewa da bukatar mayar da shari’ar Sheikh Abduljabbar Kabara zuwa babban birnin tarayya, Abuja.

Abduljabbar dai ya bukaci kotun da ta mayar da shari’ar tasa zuwa wata kotun a Abuja saboda zargin da yake na cewar kotun Kano ba za ta yi masa adalci ba.

  • Barazanar ‘Yan Bindiga: Gwamnatin Nasarawa Ta Rufe Duk Makarantun Jihar
  • Rashin Tsaro: NYSC Ta Nemi Karin Sojoji A Sansanonin Masu Yi Wa Kasa Hidima

A yayin zaman kotun na yau Alhamis, wanda ya gudana karkashin mai shari’a Abdullahi Liman, lauyan Abduljabbar Nasir Kabara, Barista Dalhatu Shehu Usman, ya zargi alkalin kotun tarayyar na Kano da ganawa da kwamsihinan shari’a na Kano, Barista Musa Lawan a safiyar yau gabanin zaman kotun.

Wanda ya ce bisa ka’ida bai kamata a ce alkalin ya yi hakan ba, wanda kuma hakan yasa Sheikh Kabara ya karaya da cewar ba zai samu adalci a kotun ba.

Sai dai a wani martani da lauya gwamnati, Barista Dahiru Muhammad, ya kalubalanci wannan batu.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

Ya sanar da kotun cewar tun karfe 9 na safiyar yau, masu gabatar da karar suka ba shi kwafin wata sabuwar karar da suka shigar a Abuja na zargin take hakkinsa na dan adam, bayan batun na gaban alkalin wata kotu ta daban.

Daga nan ne mai shari’a Abdullahi Liman, ya ce ba zai rufe shari’ar ba, sannan a shari’ance babu inda aka ce bangare daya da ake shari’a da shi zai ce lallai shi ga kotun da yake bukata da ta saurari wata shari’ar.

Sannan ya umurci lauyan Abduljabbar da ya rubuto zargin da yake yi kan zuwan Kwamishinan shari’a na jihar Kano wajensa, tare da tabbatar da abin da suka tattauna na da alaka da shari’ar ta Abduljababr din ya shigar gabansa.

LEADERSHIP ta ruwaito a ranar 21 ga watan Yulin da muke ciki ne Shiekh Abduljabbar, ya garzaya kotun tarayyar da ke Kano, da bukatar a mayar da shari’ar da ake yi masa ta zargin batancin ga Annabi S.A.W zuwa ga wani alkalin daban.

Ya yi hakan ne saboda zargin cewar gwamantin Kano da Babbar Kotun Musulunci ta Kofar Kudu na take masa hakkinsa a matsayinsa na dan Adam.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbduljabbarAbujakanoShari'aZargin Batanci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Rashin Tsaro: NYSC Ta Nemi Karin Sojoji A Sansanonin Masu Yi Wa Kasa Hidima

Next Post

Tsoffin Mataimakan Gwamnonin Kebbi 2 Da Mata 5000 Daga Bauchi Sun Bar APC Zuwa PDP

Related

NNPP
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

11 hours ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Manyan Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

13 hours ago
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis
Manyan Labarai

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

19 hours ago
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

20 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

23 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

1 day ago
Next Post
Tsoffin Mataimakan Gwamnonin Kebbi 2 Da Mata 5000 Daga Bauchi Sun Bar APC Zuwa PDP

Tsoffin Mataimakan Gwamnonin Kebbi 2 Da Mata 5000 Daga Bauchi Sun Bar APC Zuwa PDP

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.