• English
  • Business News
Wednesday, July 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Kori Karar Da Maina Ya Shigar Kan Ministan Harkokin Cikin Gida Da Wasu

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Kotu Ta Kori Karar Da Maina Ya Shigar Kan Ministan Harkokin Cikin Gida Da Wasu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mai shari’a Inyang Ekwo na babbar kotun tarayya da ke Abuja, ya yi watsi da karar da Abdulrasheed Maina ya shigar a kan ministan harkokin cikin gida, Rauf Aregbesola, da kuma babban jami’in gidan gyaran hali na Nijeriya, Haliru Nababa, bisa zargin tauye masa hakki.

Da yake yanke hukunci, Mai shari’a Ekwo, ya ce Maina bai bayar da wata kwakkwarar hujjar da ke nuna cewa ministan da CG sun tauye masa wani hakki nasa ba kamar yadda doka ta tanadar a lokacin da yake tsare.

  • Sin Za Ta Ci Gaba Da Hada Hannu Da Mambobin G20 Game Da Tsarin Tattalin Arziki Na Zamani
  • 2023: Indiya Za Ta Rage Kudin Zuwa Aikin Hajji

Alkalin ya dauki bukatar Maina a matsayin yaudara da kuma kokarin raina ma’anar hukuncin aikata laifi da kuma taimaka wa Maina koma kam turba.

Mai shari’a Ekwo ya yi watsi da bukatarsa ​​saboda rashin cancanta.

Maina, wanda tsohon Shugaban Hukumar Fansho ne, ya shigar da kara a ranar 17 ga Oktoba, inda ya gabatar da wani kuduri na neman a kula da lafiyarsa cikin gaggawa saboda yana fama da wata cuta mai barazana ga rayuwa.

Labarai Masu Nasaba

Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC

Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana

Tsohon shugaban hukumar fanshon ya roki kotun da ta ba shi umarnin wucin gadi da ya umarci ministan da CG ta hannun ma’aikatansu ko jami’ansu da su kai shi wani babban asibiti domin jinyar cututtukan da ke barazana ga rayuwarsa har zuwa lokacin da za a yanke hukunci.

Yanzu haka Maina yana zaman gidan yari na shekara takwas a gidan yari na Kuje da ke Abuja bisa samunsa da laifin almundahanar kudin fansho har Naira biliyan biyu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AlkaliBadakalaHukunciKotuMainaMinistaShari'a
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Ake Sallar Rokan Ruwan Sama

Next Post

Lalong Ya Yi Allah-wadai Da Kashe-kashen Da Aka Yi A Filato, Ya Bukaci A Gurfanar Da Masu Laifin

Related

Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC
Manyan Labarai

Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC

5 hours ago
Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana

7 hours ago
Za A Sake Gurfanar Da Faston Da Ake Zargi Da Sa Mabiyansa Azumin Mutuwa
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina

9 hours ago
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Neja

11 hours ago
Tinubu Ya Nada Ribadu Da Wasu A Matsayin Masu Ba Shi Shawara
Manyan Labarai

Ku Daina Kashe Mutane Ko Ku Miƙa Wuya – Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Bindiga

14 hours ago
Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace
Manyan Labarai

Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

1 day ago
Next Post
Lalong Ya Yi Allah-wadai Da Kashe-kashen Da Aka Yi A Filato, Ya Bukaci A Gurfanar Da Masu Laifin

Lalong Ya Yi Allah-wadai Da Kashe-kashen Da Aka Yi A Filato, Ya Bukaci A Gurfanar Da Masu Laifin

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja

Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja

July 30, 2025
Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5

Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5

July 30, 2025
Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya

Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya

July 30, 2025
Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma

Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma

July 30, 2025
Gine-gine 8 Sun Ruguje, Makabarta Ta Nutse A Wata Sabuwar Ambaliyar Ruwa A Borno

Gine-gine 8 Sun Ruguje, Makabarta Ta Nutse A Wata Sabuwar Ambaliyar Ruwa A Borno

July 30, 2025
Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 

Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 

July 30, 2025
Za A Bude Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Koli Na 20 Na JKS A Watan Oktoban bana

Za A Bude Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Koli Na 20 Na JKS A Watan Oktoban bana

July 30, 2025
Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna

Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna

July 30, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwar Sin Da Amurka

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwar Sin Da Amurka

July 30, 2025
Rashin Nasarar DPP A Zagayen Farko Na Kuri’ar Kiranye Ya Nuna Rashin Amincewar Al’ummar Taiwan Da Salon Mulkin Jami’yyar

Rashin Nasarar DPP A Zagayen Farko Na Kuri’ar Kiranye Ya Nuna Rashin Amincewar Al’ummar Taiwan Da Salon Mulkin Jami’yyar

July 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.