ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Lalong Ya Yi Allah-wadai Da Kashe-kashen Da Aka Yi A Filato, Ya Bukaci A Gurfanar Da Masu Laifin

by Sadiq
4 years ago
Filato

Gwamna Simon Lalong na Jihar Filato, ya yi Allah-wadai da harin da aka kai a daren ranar Talata a unguwar Maikatako da ke gundumar Butura ta karamar hukumar Bokkos, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane 11 tare da jikkata wasu mutane takwas.

A wata sanarwa da Daraktan yada labarai da hulda da jama’a na Jihar, Makut Machan ya fitar, Lalong ya bukaci jami’an tsaro a jihar da su kamo wadanda suka aikata wannan aika-aika domin gurfanar da su a gaban kuliya.

  • Sin Za Ta Kara Raya Sana’o’in Dake Shafar Kasuwar Sinadarin Carbon
  • Dakarun Soji A Jihar Kaduna Sun Kara Kashe Wani Jagoran ‘Yan Bindiga Gudau Kachalla

Gwamnan wanda ya jajantawa iyalan wadanda harin ya rutsa da su, ya nanata cewa gwamnatinsa ba za ta bari ‘yan ta’adda da ‘yan bindiga su kai hari a wani yanki na jihar ba saboda an umarci dukkanin hukumomin tsaro da su tabbatar da ta yi maganin duk wani mutum ko kungiyar da ta kai harin. .

ADVERTISEMENT

A cewarsa, yawaitar hare-hare da lalata amfanin gonaki, dabbobi, da sauran dukiyoyi a karamar hukumar ta Bokkos, na zama abin damuwa, kuma dole ne a duba su cikin gaggawa.

Wasu da ake zargin makiyaya ne sun afkawa al’ummar yankin da misalin karfe 11 na daren ranar Talata, inda suka kona gidaje hudu a harin, sannan suka fara harbi ba kakkautawa bayan da suka mamaye ‘yan banga da ke sintiri.

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

An ce guda tara daga cikin wadanda abin ya shafa an kona su ne ta yadda ba za a iya gane su ba a wani waje, yayin da sauran kuma aka same su da sanyin safiyar Laraba a gidajensu da suka kone bayan an harbe su.

Wani dan unguwar ya tuna cewa harin ba gaira ba dalili ya fara ne bayan ranar kasuwar Litinin ta mako-mako inda aka harbe wani yaro a Hilltop, wanda ke da tazarar kilomita daga Maikatako.

Rahotanni sun ce lamarin harbin ya haifar da tashin hankali a tsakanin al’ummar a ranar Talata duk da cewa ‘yan banga sun yi kokarin fatattakar maharan.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, kakakin rundunar ‘yansandan Jihar Filato, Alfred Alabo, ya ce har yanzu bai samu cikakken bayanin lamarin ba.

Sai dai kwamandan rundunar ‘Operation Safe Haven’ Manjo-Janar Ibrahim Ali, ya bayyana cewa rundunar tsaron da aka bai wa alhakin kula da al’amuran tsaro a Filato, da kuma wasu sassan jihohin Bauchi da Kaduna, sun kasance a kasa don shirin ko ta kwana.

MASU ALAKA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Next Post
Duk Bayan Shekaru 8 Ya Kamata Ake Sauya Fasalin Naira – Shugaban EFCC

Duk Bayan Shekaru 8 Ya Kamata Ake Sauya Fasalin Naira - Shugaban EFCC

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.