ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Lalong Ya Yi Allah-wadai Da Kashe-kashen Da Aka Yi A Filato, Ya Bukaci A Gurfanar Da Masu Laifin

by Sadiq
4 years ago
Filato

Gwamna Simon Lalong na Jihar Filato, ya yi Allah-wadai da harin da aka kai a daren ranar Talata a unguwar Maikatako da ke gundumar Butura ta karamar hukumar Bokkos, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane 11 tare da jikkata wasu mutane takwas.

A wata sanarwa da Daraktan yada labarai da hulda da jama’a na Jihar, Makut Machan ya fitar, Lalong ya bukaci jami’an tsaro a jihar da su kamo wadanda suka aikata wannan aika-aika domin gurfanar da su a gaban kuliya.

  • Sin Za Ta Kara Raya Sana’o’in Dake Shafar Kasuwar Sinadarin Carbon
  • Dakarun Soji A Jihar Kaduna Sun Kara Kashe Wani Jagoran ‘Yan Bindiga Gudau Kachalla

Gwamnan wanda ya jajantawa iyalan wadanda harin ya rutsa da su, ya nanata cewa gwamnatinsa ba za ta bari ‘yan ta’adda da ‘yan bindiga su kai hari a wani yanki na jihar ba saboda an umarci dukkanin hukumomin tsaro da su tabbatar da ta yi maganin duk wani mutum ko kungiyar da ta kai harin. .

ADVERTISEMENT

A cewarsa, yawaitar hare-hare da lalata amfanin gonaki, dabbobi, da sauran dukiyoyi a karamar hukumar ta Bokkos, na zama abin damuwa, kuma dole ne a duba su cikin gaggawa.

Wasu da ake zargin makiyaya ne sun afkawa al’ummar yankin da misalin karfe 11 na daren ranar Talata, inda suka kona gidaje hudu a harin, sannan suka fara harbi ba kakkautawa bayan da suka mamaye ‘yan banga da ke sintiri.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

An ce guda tara daga cikin wadanda abin ya shafa an kona su ne ta yadda ba za a iya gane su ba a wani waje, yayin da sauran kuma aka same su da sanyin safiyar Laraba a gidajensu da suka kone bayan an harbe su.

Wani dan unguwar ya tuna cewa harin ba gaira ba dalili ya fara ne bayan ranar kasuwar Litinin ta mako-mako inda aka harbe wani yaro a Hilltop, wanda ke da tazarar kilomita daga Maikatako.

Rahotanni sun ce lamarin harbin ya haifar da tashin hankali a tsakanin al’ummar a ranar Talata duk da cewa ‘yan banga sun yi kokarin fatattakar maharan.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, kakakin rundunar ‘yansandan Jihar Filato, Alfred Alabo, ya ce har yanzu bai samu cikakken bayanin lamarin ba.

Sai dai kwamandan rundunar ‘Operation Safe Haven’ Manjo-Janar Ibrahim Ali, ya bayyana cewa rundunar tsaron da aka bai wa alhakin kula da al’amuran tsaro a Filato, da kuma wasu sassan jihohin Bauchi da Kaduna, sun kasance a kasa don shirin ko ta kwana.

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Next Post
Duk Bayan Shekaru 8 Ya Kamata Ake Sauya Fasalin Naira – Shugaban EFCC

Duk Bayan Shekaru 8 Ya Kamata Ake Sauya Fasalin Naira - Shugaban EFCC

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.