ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Tsare Alkalai 8 Kan Zargin Karkatar Da Kudin Marayu A Kano

by Sadiq
3 years ago
Kotu

Wata kotun majistare a Jihar Kano ta bayar da umarnin tsare wasu alkalan kotun shari’ar Musulunci takwas da ma’aikatan Hukumar Shari’a bakwai a gidan yari bisa zargin karkatar da kudin wasu marayu da ya kai Naira miliyan 99 a jihar.

Alkalin kotun Mai shari’a Mustapha Sa’ad Datti, ya bayar da wannan umarni ne a ranar Alhamis biyo bayan tuhumar karkatar da Naira miliyan 99 da hukumar yaki da cin hanci da rashawa mai zaman kanta ta ICPC, ta shigar a gaban kotu kan mutane 15.

  • Masarautar Katsina Ta Warware Rawanin Hakimin Bakori, Makaman Katsina
  •  GORON JUMA’A

Alkalin kotun Mai shari’a Datti, ya bayar da umarnin a tsare wadanda ake kara a gidan yari har zuwa zaman kotun na gaba.

ADVERTISEMENT

Wadanda ake tuhumar sun hada da Gazzali Wada, Yusuf Abdullahi, Sani Ali, Bashir Baffa, Sani Uba Ali, Hadi Tijjani Mu’azu, Mustafah Bala, da Alkasim Abdullahi.

Sauran wadanda ake tuhuma da ke tsare a gidan yari sun hada da Abdullahi Sulaiman Zango, Jaafar Ahmad, Bashir Ali Kurawa, Adamu Balarabe, Garba Yusuf, Aminu Abdulhadi, da Usaina Imam.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Kamar yadda aka gabatar, an tuhumi alkalan da ma’aikatan da wajen “hada baki, cin amana da kuma satar Naira miliyan 99.”

A halin da ake ciki, wadanda ake tuhumar duk sun musanta aikata laifin.

Don haka, babban lauyan wanda ya shigar da kara, Zaharaddin Kofar Mata, ya bukaci a dage zaman domin gabatar da kwararan shaidu a gaban kotun.

Biyo bayan bukatar da lauyan ya yi na a bada belin wadanda ake karar, kotun ta ki amincewa da bukatar da kuma bayar da umarnin a tsare wadanda ake karar a gidan yari.

An dage sauraren karar har zuwa ranar 1 ga watan Fabrairu, 2023 don ci gaba da sauraren karar.

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Yadda Za Ka Sauke Bidiyo A Wayarka Daga Facebook Da YouTube 

Yadda Za Ka Sauke Bidiyo A Wayarka Daga Facebook Da YouTube 

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.