• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Yanke Wa Wani Matashi Dan Kasar Nijar Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Laifin Kisan Kai A Kebbi

by Sulaiman and Umar Faruk
3 years ago
Kebbi

Wata babbar kotu ta daya da ke Birnin Kebbi, ta yanke wa wani dan kasar Jamhuriyar Nijar, Sulieman Idris, hukuncin kisa ta hanyar rataya , bisa samunsa da laifin kisan matar aure da’yar ta ‘yar shekara hudu da haihuwa a duniya.

Lauyoyin jihar sun gurfanar da Suleiman Idris a gaban kuliya tare da tuhumar shi da laifuka biyu na kisan kai wanda hukuncin kisa ne a karkashin sashe na 191 (a) da (b) na dokar Penal Code na jihar Kebbi, 2021.

  • NDLEA Ta Gudanar Da Bikin Ranar Yaki Da Sha Da Fataucin Miyagun Kwayoyi Na Duniya A Kebbi

Da yake yanke hukunci, Mai shari’a kuma Babbar jojin Jihar Sulieman Muhammad -Ambursa, ya ce masu gabatar da kara sun yi nasarar tabbatar da dukkan hujojin su da babu shakka a gaban kotu, inji kotun”

“A bisa la’akari da nauyi da shaidun da lauyoyin masu gabatar da kara su gabatar a gaban kotu, wadanda suka nuna tabbacin aikata laifin da ake tuhumar Sulieman Idris a gaban kotun sun tabbata, inji kotun”.

“ Haka Kuma bisa ga doka, tuhume-tuhume biyu na aikata laifin kisan kai da ke da hukuncin kisa a karkashin sashe na 191 (a) da (b) a karkashin dokar Penal Code, 2021 an tabbatar da su kuma wanda ake tuhumar ya nuna cewa ya aikata laifin da ake tuhumar su da aikatawa a gaban wannan kotu.

LABARAI MASU NASABA

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

“A bisa hujojin da suka nuna aikata laifin kisa da aka tuhumi Sulieman Idris, kotu ta yanke maka hukuncin kisa bisa laifin da kotu ta kama ka da shi. Don haka kotu ta yanke maka hukuncin kisa ta hanyar rataya har sai ya mutu, inji kotu”.

“Game da roƙon neman adalci tare da jinƙai ga waɗanda ake tuhuma da lauyan nasa ya yi, kan yanke masa hukunci.

Bugu da kari, kotu ta ce” kai Sulieman Idris, an yanke maka hukuncin kisa ta hanyar rataya, kuma a rataye ka da wuya har ka mutu,inji kotun”.

Tun da farko, mai gabatar da kara, Barista Zainab muhammad- Jabbo, ta shaida wa kotun cewa wanda ake kara ya aikata laifin da ya kashe matar har lahira tare da buga kan karamar yarinyar a kan tayal dakin mahaifiyar, wanda ya kai ga mutuwarta a ranar 11 ga Afrilu.

Ta ce bangaren da aka aikata laifukan a cikinsa ba shi da hurumi, don haka ta roki kotu da ta hukunta wadanda ake tuhuma kamar yadda yake kunshe a sashin.

A nasa jawabin, Lauyan mai kare wanda ake tuhumar, Barista Alhassan salihu-Muhammad, ya roki kotun da ta yi adalci da rahama wajen yanke wa wanda ake tuhuma hukuncin daurin rai da rai, kamar yadda ya nuna nadamar matakin da ya dauka.

Mijin marigayin, Malam Akilu Aliyu, wanda ya bayyana jin dadinsa da hukuncin, ya roki gwamnatin jihar da ta gaggauta zartar da hukuncin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump
Labarai

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya
Manyan Labarai

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

November 3, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki
Ra'ayi Riga

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

November 3, 2025
Next Post
2023: Akwai Yuyuwar Kwankwaso Ya Amince Ya Zama Mataimakin Peter Obi Na Jam’iyyar LP

Maganar Hadewar Kwankwaso Da Peter Obi Ta Rushe

LABARAI MASU NASABA

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

November 3, 2025
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

November 3, 2025
Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

November 3, 2025
Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

November 3, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

November 3, 2025
Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

November 3, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.