• Leadership Hausa
Thursday, September 28, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NDLEA Ta Gudanar Da Bikin Ranar Yaki Da Sha Da Fataucin Miyagun Kwayoyi Na Duniya A Kebbi

by Sadiq
1 year ago
in Labarai
0
NDLEA Ta Gudanar Da Bikin Ranar Yaki Da Sha Da Fataucin Miyagun Kwayoyi Na Duniya A Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Hana Sha da Fataucin miyagun Kwayoyi ta Kasa (NDLEA), reshen Jihar Kebbi, ta bi sahun sauran jihohi da masu ruwa da tsaki wajen gudanar da bikin ranar yaki da fataucin miyagun kwayoyi ta duniya a jihar.

Bayan kudurin Majalisar Dinkin Duniya (MDD) a shekarar 1987, ranar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi na duniya da nufin karfafa aiki da hadin gwiwa don cimma burin al’ummar duniya da ba ta su ga muggan kwayoyi.

  • Mutane 3 Sun Mutu A Hatsarin Mota, Biyu Sun Jikkata A Kogi
  • G7 Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Taimakon Ukraine A Yakinta Da Rasha

Bikin na 2022 mai taken cewa” Magance kalubalen shan kwayoyi a cikin Lafiya da Rikicin Jin kai yana da matukar dacewa dangane da cutar ta Korona da karuwar kalubalen tsaro a Nijeriya”.

 

A shekarar 2021, NDLEA ta kama sama da tan bakwai na haramtattun kwayoyi da kudinsu ya haura Naira Biliyan 130 tare da gurfanar da mutane sama da 900 da ake zargi.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Uba Sani Ya Taya Kansa Murna Da Hukuncin Da Kotun Zaben Kaduna Ta Yanke

Babu Wata Yarjejeniya Tsakaninmu Da Gwamnatin Tarayya Kan Dakatar Da Yajin Aiki – NLC

A nasa jawabin, Kwamandan NDLEA na shiyyar Sokoto, Kebbi da Zamfara, Muhammad Misbahu Idris, ya yabawa kokarin mai girma Sanata Abubakar Atiku Bagudu, da uwar gidansa Dakta Zainab Shinkafi Bagudu,  bisa gagarumin goyon baya da gudunmawar da suke bayarwa a Jihar Kebbi wajen ganin an magance matsalar na shan miyagun kwayoyi a fadin Jihar.

Haka kuma ya ce” yawaitar shaye-shayen miyagun kwayoyi a Nijeriya ya yi yawa, kafin yawan shan muggan kwayoyi a duniya ya kai kashi 15 cikin 100 amma a Nijeriya a yau ya kai kashi 15.

Haka zalika, ya yi kira ga iyaye da masu ruwa da tsaki da su zage damtse wajen sauke nauyin da ya rataya a wuyansu wajen kula da ‘ya’yansu da kyau don kaucewa ga fadawa cikin shan miyagun kwayoyi ko kuma abokantaka da Matasa masu shaye shaye.

Bugu da kari, ya yi kira ga jami’an hukumarsa da su kara kaimi wajen sauke nauyin da ya rataya a wuyansu na kamawa da gurfanar da masu aikata laifin shan miyagun kwayoyi.

Tun da farko, kwamishinan ma’aikatar kiwon lafiya na jihar, Jafar Muhammad, wanda ya wakilci gwamnan jihar Kebbi, ya yi alkawarin ci gaba da bayar da goyon bayan gwamnatin jihar domin dakile ta’ammali da miyagun kwayoyi a jihar.

A wani bangare na bikin rana, an gudanar da atisayen tafiya da kafa da rera wakoki daga ofishin jiha zuwa fadar Sarkin Gwandu, daga nan sai suka zarce zuwa masaukin fadar shugaban kasa, inda aka gudanar da lakcoci kan shaye-shayen miyagun kwayoyi da laifuka, da kuma haramcin shan miyagun kwayoyi a cikin al’umma.

Mahalarta taron, sun hada da sakatare na dindindin na Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kebbi, Wakilan Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa, Hukumar Kula da Lafiyar Jama’a ta Tarayya, Jami’an Hukumar Kare Hadura ta Kasa, Jami’an Tsaro da Tsaron Farar Hula, Kungiyoyin Sa-kai da Kungiyoyin Jama’a.

Tags: Hukumar LafiyaKebbiKwamandaNDLEAShan Miyagun KwayoyiSokotoZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Kafa Cibiyar Raya Al’Adu Da Tattalin Arzikin Sin Da Afrika A Fuzhou

Next Post

Dole Ne A Ci Gaba Da Binciken Alkalin Alkalai Mai Murabus, Tanko Muhammad — Majalisa

Related

Gwamna Uba Sani Ya Taya Kansa Murna Da Hukuncin Da Kotun Zaben Kaduna Ta Yanke
Manyan Labarai

Gwamna Uba Sani Ya Taya Kansa Murna Da Hukuncin Da Kotun Zaben Kaduna Ta Yanke

3 hours ago
Kungiyar Kwadago (NLC) Na Shirin Tsunduma Wani Sabon Yajin Aiki Mai Dogon Zango
Manyan Labarai

Babu Wata Yarjejeniya Tsakaninmu Da Gwamnatin Tarayya Kan Dakatar Da Yajin Aiki – NLC

4 hours ago
Kotun Zabe Ta Ce Zaben Gwamnan Kaduna Bai Kammalu Ba (Inconclusive)
Manyan Labarai

Kotun Zabe Ta Ce Zaben Gwamnan Kaduna Bai Kammalu Ba (Inconclusive)

6 hours ago
Bauchi
Labarai

Kotu Ta Kori Karar APC Ta Tabbatar Da Nasarar Kakakin Majalisar Bauchi

6 hours ago
Hisbah
Labarai

Hisbah Ta Yi Wa Mutum 4,000 Rajista Da Ke Son Gwamnatin Kano Ta Aurar Da Su

7 hours ago
Dawanau
Manyan Labarai

Gwamnatin Kano Za Ta Kashe Naira Miliyan 600 Wajen Gudanar Da Ayyuka A Kasuwar Hatsi Ta Dawanau 

9 hours ago
Next Post
Dole Ne A Ci Gaba Da Binciken Alkalin Alkalai Mai Murabus, Tanko Muhammad — Majalisa

Dole Ne A Ci Gaba Da Binciken Alkalin Alkalai Mai Murabus, Tanko Muhammad — Majalisa

LABARAI MASU NASABA

Sin

Hadin Gwiwar Sin Da Ghana Na Da Muhimmanci Ga Ci Gaban Tattalin Arzikin Ghana

September 28, 2023
Bamu Da Niyyar Cin Zarafin Victor Osimhen-Napol

Bamu Da Niyyar Cin Zarafin Victor Osimhen-Napol

September 28, 2023
Adadin Jarin Da Kasar Sin Ta Zuba A Kasashen Waje A Shekarar 2022 Na Kan Gaba A Duniya

Adadin Jarin Da Kasar Sin Ta Zuba A Kasashen Waje A Shekarar 2022 Na Kan Gaba A Duniya

September 28, 2023
Cibiyar Kimiyyar Noma Na Sin CATAS Ta Cancanci Yabo

Cibiyar Kimiyyar Noma Na Sin CATAS Ta Cancanci Yabo

September 28, 2023
CISA: Masana’antun Sarrafa Karfe Na Tafiya Cikin Yanayi Mai Karko Tsakanin Watan Janairu Zuwa Na Agusta

CISA: Masana’antun Sarrafa Karfe Na Tafiya Cikin Yanayi Mai Karko Tsakanin Watan Janairu Zuwa Na Agusta

September 28, 2023
Gwamna Uba Sani Ya Taya Kansa Murna Da Hukuncin Da Kotun Zaben Kaduna Ta Yanke

Gwamna Uba Sani Ya Taya Kansa Murna Da Hukuncin Da Kotun Zaben Kaduna Ta Yanke

September 28, 2023
Kungiyar Kwadago (NLC) Na Shirin Tsunduma Wani Sabon Yajin Aiki Mai Dogon Zango

Babu Wata Yarjejeniya Tsakaninmu Da Gwamnatin Tarayya Kan Dakatar Da Yajin Aiki – NLC

September 28, 2023
Masana Kimiyya Na Sin Da Afrika Sun Lashi Takobin Hada Gwiwa Wajen Ganin An Cimma Ajandar Kyautata Rayuwar Jama’a

Masana Kimiyya Na Sin Da Afrika Sun Lashi Takobin Hada Gwiwa Wajen Ganin An Cimma Ajandar Kyautata Rayuwar Jama’a

September 28, 2023
“Wasannin Asiya Na Zamani” Wata Taga Ce Ta Lura Da Yadda Ake Gudanar Da Zamanintarwa Irin Na Kasar Sin

“Wasannin Asiya Na Zamani” Wata Taga Ce Ta Lura Da Yadda Ake Gudanar Da Zamanintarwa Irin Na Kasar Sin

September 28, 2023
Xi Ya Yi Kira Da A Samar Da Sabbi Da Manyan Gudummawa Don Ciyar Da Harkokin Mata Da Yara Gaba

Xi Ya Yi Kira Da A Samar Da Sabbi Da Manyan Gudummawa Don Ciyar Da Harkokin Mata Da Yara Gaba

September 28, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.